< Ayuba 1 >
1 A ƙasar Uz akwai wani mutum mai suna Ayuba. Mutum ne marar laifi kuma mai adalci; yana tsoron Allah, ba ruwansa da mugunta.
A man there hath been in the land of Uz — Job his name — and that man hath been perfect and upright — both fearing God, and turning aside from evil.
2 Yana da’ya’ya maza bakwai da’yan mata uku,
And there are borne to him seven sons and three daughters,
3 yana da tumaki dubu bakwai, raƙuma dubu uku, shanu ɗari biyar, da jakuna ɗari biyar, yana kuma da masu yi masa aiki da yawa. A ƙasar Gabas ba wani kamar sa.
and his substance is seven thousand sheep, and three thousand camels, and five hundred pairs of oxen, and five hundred she-asses, and a service very abundant; and that man is greater than any of the sons of the east.
4 ’Ya’yansa maza sukan yi biki a gidajensu, wannan yă yi yă ba wancan, sai su kira’yan’uwansu mata ukun su ci, su sha tare.
And his sons have gone and made a banquet — the house of each [in] his day — and have sent and called to their three sisters to eat and to drink with them;
5 Bayan lokacin bikin ya wuce, sai Ayuba yă aika su zo don yă tsarkake su. Tun da sassafe zai miƙa hadaya ta ƙonawa domin kowannensu, don yana tunani cewa, “Mai yiwuwa’ya’yana sun yi wa Allah zunubi, ko sun la’anta shi a cikin zuciyarsu.” Haka Ayuba ya saba yi.
and it cometh to pass, when they have gone round the days of the banquet, that Job doth send and sanctify them, and hath risen early in the morning, and caused to ascend burnt-offerings — the number of them all — for Job said, 'Perhaps my sons have sinned, yet blessed God in their heart.' Thus doth Job all the days.
6 Wata rana mala’iku suka kawo kansu gaban Ubangiji, Shaiɗan shi ma ya zo tare da su.
And the day is, that sons of God come in to station themselves by Jehovah, and there doth come also the Adversary in their midst.
7 Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Daga ina ka fito?” Shaiɗan ya amsa wa Ubangiji ya ce, “Daga yawo a duniya ina kai da kawowa a cikinta.”
And Jehovah saith unto the Adversary, 'Whence comest thou?' And the Adversary answereth Jehovah and saith, 'From going to and fro in the land, and from walking up and down on it.'
8 Sai Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Ko ka ga bawana Ayuba? A cikin duniya babu wani kamar sa; shi marar laifi ne, adali kuma, mutum ne mai tsoron Allah, ba ruwansa da mugunta.”
And Jehovah saith unto the Adversary, 'Hast thou set thy heart against My servant Job because there is none like him in the land, a man perfect and upright, fearing God, and turning aside from evil?'
9 Sai Shaiɗan ya amsa ya ce, “Haka kawai Ayuba yake tsoron Allah?
And the Adversary answereth Jehovah and saith, 'For nought is Job fearing God?
10 Ba ka kāre shi da iyalinsa gaba ɗaya da duk mallakarsa ba? Ka Albarkaci ayyukan hannunsa yadda dabbobinsa duk sun cika ko’ina.
Hast not Thou made a hedge for him, and for his house, and for all that he hath — round about?
11 Ka ɗan miƙa hannunka ka raba shi da duk abin da yake da shi, ba shakka zai la’anta ka kana ji, kana gani.”
The work of his hands Thou hast blessed, and his substance hath spread in the land, and yet, put forth, I pray Thee, Thy hand, and strike against anything that he hath — if not: to Thy face he doth bless Thee!'
12 Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “To, shi ke nan, duk abin da yake da shi yana hannunka, amma kada ka taɓa shi, shi kansa.” Sai Shaiɗan ya bar Ubangiji.
And Jehovah saith unto the Adversary, 'Lo, all that he hath [is] in thy hand, only unto him put not forth thy hand.' And the Adversary goeth out from the presence of Jehovah.
13 Wata rana lokacin da’ya’yan Ayuba suke cikin biki a gidan babban ɗansa,
And the day is, that his sons and his daughters are eating, and drinking wine, in the house of their brother, the first-born.
14 sai ɗan aika ya zo wurin Ayuba ya ce masa, “Shanu suna huɗa, jakuna kuma suna kiwo nan kusa,
And a messenger hath come in unto Job and saith, 'The oxen have been plowing, and the she-asses feeding by their sides,
15 sai Sabenawa suka auka musu suka kwashe su suka tafi, suka karkashe masu yi maka aiki duka, ni kaɗai na tsira na zo in gaya maka!”
and Sheba doth fall, and take them, and the young men they have smitten by the mouth of the sword, and I am escaped — only I alone — to declare [it] to thee.'
16 Yana cikin magana sai ga wani ɗan aika ya zo ya ce, “Wutar Allah ta sauko daga sama ta ƙona dukan tumaki da masu lura da su, wato, bayinka, ni kaɗai na tsira na zo in gaya maka!”
While this [one] is speaking another also hath come and saith, 'Fire of God hath fallen from the heavens, and burneth among the flock, and among the young men, and consumeth them, and I am escaped — only I alone — to declare [it] to thee.'
17 Yana cikin magana sai ga wani ɗan aika ya zo ya ce, “Ƙungiyoyin mahara uku na Kaldiyawa sun auka wa raƙumanka sun kwashe su duka, suka kuma karkashe masu yi maka aiki, ni kaɗai ne na tsira na zo in gaya maka!”
While this [one] is speaking another also hath come and saith, 'Chaldeans made three heads, and rush on the camels, and take them, and the young men they have smitten by the mouth of the sword, and I am escaped — only I alone — to declare [it] to thee.'
18 Yana cikin magana, sai ga wani ɗan aika ya zo ya ce, “’Ya’yanka maza da mata suna biki, suna ci suna sha a gidan babban ɗanka,
While this [one] is speaking another also hath come and saith, 'Thy sons and thy daughters are eating, and drinking wine, in the house of their brother, the first-born.
19 sai wata iska mai ƙarfi daga hamada ta auka ta rushe gidan, gidan kuwa ya fāɗi a kan’ya’yanka ya kashe su, ni kaɗai na tsira na zo in gaya maka!”
And lo, a great wind hath come from over the wilderness, and striketh against the four corners of the house, and it falleth on the young men, and they are dead, and I am escaped — only I alone — to declare [it] to thee.'
20 Da jin haka sai Ayuba ya tashi ya yayyaga tufafin jikinsa, ya aske kansa. Ya fāɗi a ƙasa ya yi sujada
And Job riseth, and rendeth his robe, and shaveth his head, and falleth to the earth, and doth obeisance,
21 ya ce, “Tsirara na fito daga cikin mahaifiyata, tsirara kuma zan koma. Ubangiji ya bayar, Ubangiji kuma ya karɓa; yabo ya tabbata ga Ubangiji.”
and he saith, 'Naked came I forth from the womb of my mother, and naked I turn back thither: Jehovah hath given and Jehovah hath taken: let the name of Jehovah be blessed.'
22 Cikin wannan duka Ayuba bai yi wa Allah zunubi ta wurin ba shi laifi ba.
In all this Job hath not sinned, nor given folly to God.