< Ayuba 1 >

1 A ƙasar Uz akwai wani mutum mai suna Ayuba. Mutum ne marar laifi kuma mai adalci; yana tsoron Allah, ba ruwansa da mugunta.
In the land named Uz, there was a man named Job. He was a very godly/righteous [DOU] man, who greatly respected/revered God and always avoided doing evil things.
2 Yana da’ya’ya maza bakwai da’yan mata uku,
He had seven sons and three daughters.
3 yana da tumaki dubu bakwai, raƙuma dubu uku, shanu ɗari biyar, da jakuna ɗari biyar, yana kuma da masu yi masa aiki da yawa. A ƙasar Gabas ba wani kamar sa.
He owned 7,000 sheep, 3,000 camels, 1,000 oxen, and 500 female donkeys. He also had many servants. He was the richest man in all the area east [of the Jordan River].
4 ’Ya’yansa maza sukan yi biki a gidajensu, wannan yă yi yă ba wancan, sai su kira’yan’uwansu mata ukun su ci, su sha tare.
Each year, Job’s sons made feasts [in their houses] to celebrate their birthdays. Whenever each one made a feast, he would invite [all his brothers and] his three sisters to come and eat together.
5 Bayan lokacin bikin ya wuce, sai Ayuba yă aika su zo don yă tsarkake su. Tun da sassafe zai miƙa hadaya ta ƙonawa domin kowannensu, don yana tunani cewa, “Mai yiwuwa’ya’yana sun yi wa Allah zunubi, ko sun la’anta shi a cikin zuciyarsu.” Haka Ayuba ya saba yi.
When each celebration ended, Job would summon them. He would get up early in the morning and kill animals and burn them on the altar as sacrifices, one for each of his children. He said to himself, “Perhaps [one of] my sons has sinned and said something evil about God in his heart.”
6 Wata rana mala’iku suka kawo kansu gaban Ubangiji, Shaiɗan shi ma ya zo tare da su.
One day, the angels came and gathered together in front of Yahweh, and Satan came too.
7 Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Daga ina ka fito?” Shaiɗan ya amsa wa Ubangiji ya ce, “Daga yawo a duniya ina kai da kawowa a cikinta.”
Yahweh asked Satan, “Where have you come from?” Satan replied, “I have come from the earth, where I been traveling back and forth, seeing what is happening.”
8 Sai Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Ko ka ga bawana Ayuba? A cikin duniya babu wani kamar sa; shi marar laifi ne, adali kuma, mutum ne mai tsoron Allah, ba ruwansa da mugunta.”
Yahweh said to Satan, “Have you (noticed/thought about) my [faithful] servant Job? He is very godly/righteous [DOU], he greatly respects/reveres me, and he always avoids doing evil things. There is no one else on the earth like him.”
9 Sai Shaiɗan ya amsa ya ce, “Haka kawai Ayuba yake tsoron Allah?
Satan replied to Yahweh, “[What you say is true], but Job greatly respects you [only] because of what [you have done for him] [RHQ].
10 Ba ka kāre shi da iyalinsa gaba ɗaya da duk mallakarsa ba? Ka Albarkaci ayyukan hannunsa yadda dabbobinsa duk sun cika ko’ina.
You have always [RHQ] protected [MET] him and his family and everything that he owns. You have made him very prosperous/rich. He has livestock all over this land.
11 Ka ɗan miƙa hannunka ka raba shi da duk abin da yake da shi, ba shakka zai la’anta ka kana ji, kana gani.”
But if you take away [MTY] everything that he has, he will curse you openly. [IDM]”
12 Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “To, shi ke nan, duk abin da yake da shi yana hannunka, amma kada ka taɓa shi, shi kansa.” Sai Shaiɗan ya bar Ubangiji.
Yahweh replied to Satan, “(All right/Okay), I will permit you to take away everything that he has. But do not harm him.” Then Satan left, [and he prepared to cause many disastrous things to happen to Job].
13 Wata rana lokacin da’ya’yan Ayuba suke cikin biki a gidan babban ɗansa,
One day [after that], Job’s sons and daughters were feasting and drinking wine at the home of their oldest brother.
14 sai ɗan aika ya zo wurin Ayuba ya ce masa, “Shanu suna huɗa, jakuna kuma suna kiwo nan kusa,
While they were doing that, a messenger arrived at Job’s home and said to him, “While your oxen were plowing [the fields] and the donkeys were grazing nearby,
15 sai Sabenawa suka auka musu suka kwashe su suka tafi, suka karkashe masu yi maka aiki duka, ni kaɗai na tsira na zo in gaya maka!”
a group of men from [the] Sheba [area] came and attacked us. They killed all your servants [who were working in the fields] and took away all the oxen and donkeys! I am the only one who escaped to [come and] tell you what happened.”
16 Yana cikin magana sai ga wani ɗan aika ya zo ya ce, “Wutar Allah ta sauko daga sama ta ƙona dukan tumaki da masu lura da su, wato, bayinka, ni kaɗai na tsira na zo in gaya maka!”
While he was still talking to Job, another messenger arrived. He said to Job, “Lightning from the sky [MTY] struck and killed all the sheep and all the men who were taking care of the sheep! I am the only one who escaped to [come and] tell you [what happened].”
17 Yana cikin magana sai ga wani ɗan aika ya zo ya ce, “Ƙungiyoyin mahara uku na Kaldiyawa sun auka wa raƙumanka sun kwashe su duka, suka kuma karkashe masu yi maka aiki, ni kaɗai ne na tsira na zo in gaya maka!”
While he was still talking to Job, another messenger arrived. He said to Job, “Three groups [of robbers/bandits] from Chaldea [land] came and attacked us. They stole all the camels and killed all the men who were taking care of them. I am the only one who escaped to [come and] tell you [what happened].”
18 Yana cikin magana, sai ga wani ɗan aika ya zo ya ce, “’Ya’yanka maza da mata suna biki, suna ci suna sha a gidan babban ɗanka,
While he was still talking to Job, another messenger arrived and reported this to Job: “Your sons and daughters were feasting in the home of their oldest brother.
19 sai wata iska mai ƙarfi daga hamada ta auka ta rushe gidan, gidan kuwa ya fāɗi a kan’ya’yanka ya kashe su, ni kaɗai na tsira na zo in gaya maka!”
Suddenly a (very strong wind/tornado) came from the desert and struck the house. The house collapsed on your sons and daughters and killed them all! I am the only one who escaped to [come and] tell you [what happened].”
20 Da jin haka sai Ayuba ya tashi ya yayyaga tufafin jikinsa, ya aske kansa. Ya fāɗi a ƙasa ya yi sujada
Job stood up, and tore his robe and shaved his head [because he was very sad/grieved]. Then he prostrated himself on the ground [to worship God].
21 ya ce, “Tsirara na fito daga cikin mahaifiyata, tsirara kuma zan koma. Ubangiji ya bayar, Ubangiji kuma ya karɓa; yabo ya tabbata ga Ubangiji.”
He said, “When I was born, I had no clothes on. When I die, I will not take any clothes with me. Yahweh gave me [everything that I possessed], and [now] he has taken it all away. But (we should/I will) always praise Yahweh [anyway]! [MTY]”
22 Cikin wannan duka Ayuba bai yi wa Allah zunubi ta wurin ba shi laifi ba.
In spite of all these [things that happened to] Job, [he] did not sin by saying that what God had done was wrong.

< Ayuba 1 >