< Irmiya 1 >

1 Kalmomin Irmiya ɗan Hilkiya, ɗaya daga cikin firistoci a Anatot a yankin Benyamin.
The wordis of Jeremye, sone of Helchie, of the preestis that weren in Anathot, in the lond of Beniamyn.
2 Maganar Ubangiji ta zo gare shi a shekara ta goma sha uku ta sarautar Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda,
For the word of the Lord was maad to hym in the daies of Josie, the sone of Amon, kyng of Juda, in the threttenethe yeer of his rewme.
3 da kuma a zamanin Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, har zuwa watan biyar na shekara goma sha ɗaya na Zedekiya ɗan Yosiya sarkin Yahuda, sa’ad da aka kai mutanen Urushalima zaman bauta.
And it was don in the daies of Joachym, the sone of Josie, the king of Juda, til to the endyng of the enleuenthe yeer of Sedechie, sone of Josie, kyng of Juda, til the passyng ouer, ether caitifte, of Jerusalem, in the fyuethe monethe.
4 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the Lord was maad to me,
5 “Kafin in siffanta ka a cikin ciki na san ka, kafin a haife ka, na keɓe ka; na naɗa ka ka zama annabi ga al’ummai.”
and seide, Bifor that Y fourmede thee in the wombe, Y knewe thee; and bifor that thou yedist out of the wombe, Y halewide thee; and Y yaf thee a profete among folkis.
6 Sai na ce, “Kayya, Ubangiji Mai Iko Duka, ban iya magana ba; ni ɗan yaro ne kawai.”
And Y seide, A! A! A! Lord God, lo! Y kan not speke, for Y am a child.
7 Amma Ubangiji ya ce mini, “Kada ka ce, ‘Ni ɗan yaro ne kawai.’ Dole ka je wurin kowane mutumin da na aike ka ka kuma faɗa abin da na umarce ka.
And the Lord seide to me, Nyle thou seie, that Y am a child; for thou schalt go to alle thingis, to whiche Y schal sende thee, and thou schalt speke alle thingis, what euer thingis Y schal comaunde to thee.
8 Kada ka ji tsoronsu, gama ina tare da kai kuma zan kiyaye ka,” in ji Ubangiji.
Drede thou not of the face of hem, for Y am with thee, to delyuere thee, seith the Lord.
9 Sai Ubangiji ya miƙa hannunsa ya taɓa bakina ya ce mini, “Yanzu na sa kalmomina a bakinka.
And the Lord sente his hond, and touchide my mouth; and the Lord seide to me, Lo! Y haue youe my wordis in thi mouth; lo!
10 Duba, yau na naɗa ka a kan al’ummai da mulkoki don ka tumɓuke ka kuma rusar, ka hallaka ka kuma kakkaɓe, ka gina ka kuma shuka.”
Y haue ordeynede thee to day on folkis, and on rewmes, that thou drawe vp, and distrie, and leese, and scatere, and bilde, and plaunte.
11 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa, “Me ka gani, Irmiya?” Sai na amsa na ce, “Na ga reshen itacen almon.”
And the word of the Lord was maad to me, and seide, What seest thou, Jeremye?
12 Ubangiji ya ce mini, “Daidai ne ka gani, gama ina lura in ga cewa maganata ta cika.”
And Y seide, Y se a yerde wakynge. And the Lord seide to me, Thou hast seen wel, for Y schal wake on my word, to do it.
13 Maganar Ubangiji ta sāke zo mini cewa, “Me ka gani?” Na amsa na ce, “Na ga tukunya tana tafasa, tana juyewa daga arewa.”
And the word of the Lord was maad the secounde tyme to me, and seide, What seest thou? Y se a pot buylynge, and the face therof fro the face of the north.
14 Ubangiji ya ce mini, “Daga arewa za a zubo masifa a kan dukan mazaunan ƙasar.
And the Lord seide to me, Fro the north schal be schewid al yuel on alle the dwelleris of the lond.
15 Ina shirin kiran dukan mutanen masarautar arewanci,” in ji Ubangiji. “Sarakunansu za su zo su kafa kursiyoyinsu a mashigin ƙofofin Urushalima; za su zo su kewaye dukan katangarta su kewaye dukan garuruwan Yahuda.
For lo! Y schal clepe togidere alle the naciouns of rewmes of the north, seith the Lord, and thei schulen come, and sette ech man his seete in the entryng of the yatis of Jerusalem, and on alle the wallis therof in cumpas, and on alle the citees of Juda.
16 Zan furta hukunci a kan mutanena saboda muguntarsu na yashe ni, suna ƙona turare ga waɗansu alloli suna kuma bauta wa abin da hannuwansu suka yi.
And Y schal speke my domes with hem on al the malice of hem, that forsoken me, and maden sacrifice to alien goddis, and worschipiden the werk of her hondis.
17 “Ka kintsa kanka! Ka tashi tsaye ka faɗa musu abin da na umarce ka. Kada su firgita ka, in ba haka ba zan firgita ka a gabansu.
Therfor girde thou thi leendis, and rise thou, and speke to hem alle thingis whiche Y comaunde to thee; drede thou not of the face of hem, for Y schal not make thee for to drede the cheer of hem.
18 Yau na mai da kai birni mai katanga, ginshiƙin ƙarfe da bangon tagulla don ka tsaya gāba da dukan ƙasar, ya kuma yi gāba da sarakunan Yahuda da fadawan, da firistoci da kuma mutanenta.
For Y yaf thee to dai in to a strong citee, and in to an yrun piler, and in to a brasun wal, on al the lond, to the kyngis of Juda, and to the princis therof, and to the preestis therof, and to al the puple of the lond.
19 Za su yi yaƙi da kai amma ba za su ci nasara a kanka ba, gama ina tare da kai, zan kuma kiyaye ka,” in ji Ubangiji.
And thei schulen fiyte ayens thee, and thei schulen not haue the maistrie; for Y am with thee, seith the Lord, that Y delyuere thee.

< Irmiya 1 >