< Irmiya 9 >
1 Da ma kaina maɓulɓulan ruwa ne idanuna kuma maɓulɓulan hawaye! Da sai in yi kuka dare da rana saboda mutanena da aka kashe.
Ack! det jag vatten nog hade i mitt hufvud, och min ögon voro en tårekälla, att jag natt och dag begråta måtte de slagna i mitt folk.
2 Da ma a hamada ina da wurin da matafiye za su sauka, don in bar mutanena in tafi in bar su; gama dukansu mazinata ne, taron mutane marasa aminci.
Ack! det jag ett herberge hade i öknene, så ville jag öfvergifva mitt folk, och draga ifrå dem; ty de äro allesammans horkarlar, och en arg hop.
3 “Sun tanƙwasa harshensu kamar baka, don su harba ƙarya; ba da gaskiya ba ne suke nasara a cikin ƙasar. Sukan tashi daga wannan zunubi zuwa wancan; ba su san ni ba,” in ji Ubangiji.
De skjuta med sina tungor allesammans lögn, och ingen sanning, och fara allt med våld i landena, och gå ifrå den ena ondskone till den andra, och akta mig intet, säger Herren.
4 “Ka yi hankali da abokanka; kada ka amince da’yan’uwanka. Gama kowane ɗan’uwa munafuki ne, kowane aboki kuma mai kushe ne.
Hvar och en tage sig vara för sinom nästa, och tro icke heller sinom broder; ty en broder undertrycker den andra, och en vän förråder den andra.
5 Aboki kan ruɗi aboki, ba mai faɗar gaskiya. Sun koya wa harshensu faɗar ƙarya; sun gajiyar da kansu da yin zunubi.
En vän gäckar den andra, och tala icke ett sant ord; de vinnlägga sig derom, huru den ene skall bedraga den andra, och dem tycker illa vara, att de ännu icke kunna görat värre.
6 Kai kana zama a tsakiyar ruɗu; cikin ruɗunsu sun ƙi su san ni,” in ji Ubangiji.
Der är allestäds bedrägeri ibland dem, och för bedrägeris skull vilja de icke känna mig, säger Herren.
7 Saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ga shi zan tace in kuma gwada su, gama me kuwa zan yi saboda zunubin mutanena?
Derföre säger Herren Zebaoth alltså: Si, jag vill smälta och probera dem; ty hvad skall jag annars göra, medan mitt folk så ställer sig?
8 Harshensu kibiya ce mai dafi; yana magana da ruɗu. Da bakinsa kowa yana maganar alheri da maƙwabcinsa, amma a zuciyarsa ya sa masa tarko.
Deras falska tungor äro mordskott; med sin mun tala de vänliga med sinom nästa; men i hjertat vakta de efter honom.
9 Bai kamata in hukunta su saboda wannan ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata in ɗau fansa a kan irin al’umma kamar wannan ba?”
Skulle jag nu icke sådant hemsöka uppå dem, säger Herren, och skulle min själ icke hämnas öfver sådant folk, som detta är.
10 Zan yi kuka in yi kururuwa saboda duwatsu in kuma yi makoki game da wuraren kiwon hamada. Sun zama kango ba wanda yake bi cikinta, ba a kuma jin kukan shanu. Tsuntsaye sararin sama sun gudu namun jeji ma duk sun watse.
Jag måste gråta och jämra mig på bergen, och beklaga mig vid de fäbodar i öknene; ty de äro så platt förhärjade, att der bor ingen mer, och man hörer der nu intet färop mer; både himmelens foglar och djuren äro alle borto.
11 “Zan mai da Urushalima tsibin kufai, wurin zaman diloli; zan kuma lalace garuruwan Yahuda saboda haka ba wanda zai zauna a can.”
Och jag skall göra Jerusalem till en stenhop, och till en drakaboning; och skall ödelägga Juda städer, att der ingen inne bo skall.
12 Wane mutum ne yana da isashiyar hikimar fahimtar wannan? Wa Ubangiji ya umarta da zai iya yin bayani? Me ya sa aka lalace ƙasar ta zama kufai kamar hamada da ba wanda zai iya ratsa ta?
Ack! att nu någor vis vore, och lade det uppå hjertat, och förkunnade hvad Herrans mun till honom säger: Hvarföre dock landet så förderfvadt och härjadt varder, likasom en ödemark, der ingen vistas?
13 Ubangiji ya ce, “Domin sun bar dokata, wadda na sa a gabansu; ba su yi biyayya da ni ko su bi dokata ba.
Och Herren sade: Derföre, att de öfvergifva min lag, som jag dem föregifvit hafver, och lyda intet min ord, och lefva der ej heller efter;
14 A maimako, sun bi taurin zuciyarsu; suka bi Ba’al, yadda kakanninsu suka koya musu.”
Utan följa sins hjertas tycko, och Baalim, såsom deras fäder dem lärt hafva.
15 Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa, “Ga shi zan sa wannan mutane su ci abinci mai ɗaci su kuma sha ruwan dafi.
Derföre säger Herren Zebaoth, Israels Gud: Si, jag skall spisa detta folket med malört, och gifva dem galla dricka.
16 Zan watsar da su a cikin al’ummai da su da kakanninsu ba su sani ba, zan kuma fafare su da takobi sai na hallaka su.”
Jag skall förskingra dem ibland Hedningarna, hvilka hvarken de eller deras fäder känna, och skall sända svärd efter dem, tilldess det blifver ute med dem.
17 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ku lura yanzu! Ku kira mata masu makoki su zo ku aika wa gwanaye a cikinsu su zo.
Så säger Herren Zebaoth: Skaffer och beställer gråterskor, att de komma; och sänder efter de som det väl kunna;
18 Bari su zo da sauri su yi kuka a kanmu sai idanunmu sun cika da hawaye giranmu kuma su jiƙe sharkaf.
Och begråta oss med hast, att vår ögon måga rinna med tårar, och var ögnahvarf flyta med vatten;
19 An ji karar kuka daga Sihiyona cewa, ‘Duba yadda muka lalace! Duba irin babban kunyar da muka sha! Dole mu bar ƙasar domin gidajenmu sun lalace.’”
Att man må höra en klagogråt i Zion, nämliga alltså: Ack! huru äre vi så platt förstörde och till skam vordne? Vi måste rymma landet; ty våra boningar äro nederslagna.
20 Yanzu, ya mata, ku ji maganar Ubangiji; ku buɗe kunnuwanku ga maganar bakina. Ku koya wa’yan matanku yadda za su yi kuka; ku koya wa juna makoki.
Så hörer nu, I qvinnor, Herrans ord, och edor öron fatte hans muns tal; lärer edra döttrar gråta, och den ena läre den andra klagogråt, nämliga alltså:
21 Mutuwa ta haura ta tagoginmu ta kuma shiga katangarmu; ta karkashe’ya’ya a tituna ta kuma karkashe samari a dandali.
Döden är igenom vår fenster infallen, och uti vår palats kommen, till att dräpa barnen på gatone, och ynglingarna i gränderna.
22 Ka ce, “Ga abin da Ubangiji ya furta, “‘Gawawwakin mutane za su fāɗi kamar juji a fili, kamar hatsin da aka yanka a bayan mai girbi, da ba mai tara su.’”
Säg: Så säger Herren: Menniskors kroppar skola ligga såsom träck på markene, och såsom kärfvar efter skördomannen, de ingen upptager.
23 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada mai hikima ya yi fariya da hikimarsa ko mai ƙarfi ya yi fariya da ƙarfinsa ko mai arziki ya yi fariya da arzikinsa,
Detta säger Herren: En vis berömme sig intet af sine vishet; an stark berömme sig intet af sin starkhet; en rik berömme sig intet af sin rikedom;
24 amma bari shi wanda yake taƙama ya yi taƙama da wannan, cewa ya fahimci ya kuma san ni, cewa ni ne Ubangiji, wanda yake yin alheri, gaskiya da kuma adalci a duniya, gama a waɗannan ne nake jin daɗi,” in ji Ubangiji.
Utan den som sig berömma vill, han berömme sig deraf, att han vet och känner mig, att jag är Herren, som gör barmhertighet, rätt och rättfärdighet på jordene; ty sådant behagar mig, säger Herren.
25 “Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan hukunta dukan waɗanda aka yi musu kaciya kawai a jiki,
Si, den tid kommer, säger Herren, att jag hemsöka skall alla de omskorna med de oomskorna;
26 Masar, Yahuda, Edom, Ammon, Mowab da dukan waɗanda suke zaune a hamada a wurare masu nisa. Gama dukan waɗannan al’ummai marasa kaciya ne, har dukan gidan Isra’ila ma marasa kaciya ne a zuciya.”
Nämliga Egypten, Juda, Edom, Ammons barn, Moab, och alla de som bo uti de rum i öknene; ty alle Hedningar hafva oomskoren förhud; men hela Israels hus hafver oomskoret hjerta.