< Irmiya 9 >

1 Da ma kaina maɓulɓulan ruwa ne idanuna kuma maɓulɓulan hawaye! Da sai in yi kuka dare da rana saboda mutanena da aka kashe.
If only my head could produce water, and my eyes be a fountain of tears! For I wish to weep day and night for those among the daughter of my people who have been killed.
2 Da ma a hamada ina da wurin da matafiye za su sauka, don in bar mutanena in tafi in bar su; gama dukansu mazinata ne, taron mutane marasa aminci.
If only someone would give me a place for travelers in the wilderness to stay, where I could go to abandon my people. If only I could leave them, since all of them are adulterers, a band of traitors!
3 “Sun tanƙwasa harshensu kamar baka, don su harba ƙarya; ba da gaskiya ba ne suke nasara a cikin ƙasar. Sukan tashi daga wannan zunubi zuwa wancan; ba su san ni ba,” in ji Ubangiji.
Yahweh declares, “They tread on their bows of lies with their tongues, but it is not because of any faithfulness of theirs that they grow strong on the earth. They go from one wicked act to another. They do not know me.”
4 “Ka yi hankali da abokanka; kada ka amince da’yan’uwanka. Gama kowane ɗan’uwa munafuki ne, kowane aboki kuma mai kushe ne.
Each of you, be on guard against your neighbor and do not trust in any brother. For every brother is certainly a deceiver, and every neighbor walks in slander.
5 Aboki kan ruɗi aboki, ba mai faɗar gaskiya. Sun koya wa harshensu faɗar ƙarya; sun gajiyar da kansu da yin zunubi.
Each man mocks his neighbor and does not speak the truth. Their tongues teach deceitful things. They are exhausted from committing iniquity.
6 Kai kana zama a tsakiyar ruɗu; cikin ruɗunsu sun ƙi su san ni,” in ji Ubangiji.
Your dwelling is in the midst of deception; in their deceit they refuse to acknowledge me—this is Yahweh's declaration.”
7 Saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ga shi zan tace in kuma gwada su, gama me kuwa zan yi saboda zunubin mutanena?
Yahweh of hosts says this, “See, I am about to refine them and test them, for what else can I do, because of what my people have done?
8 Harshensu kibiya ce mai dafi; yana magana da ruɗu. Da bakinsa kowa yana maganar alheri da maƙwabcinsa, amma a zuciyarsa ya sa masa tarko.
Their tongues are sharpened arrows; they speak unfaithful things. With their mouths they proclaim peace with their neighbors, but with their hearts they lie in wait for them.
9 Bai kamata in hukunta su saboda wannan ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata in ɗau fansa a kan irin al’umma kamar wannan ba?”
Should I not punish them because of these things—this is Yahweh's declaration— and should I not avenge myself on a nation that is like this?
10 Zan yi kuka in yi kururuwa saboda duwatsu in kuma yi makoki game da wuraren kiwon hamada. Sun zama kango ba wanda yake bi cikinta, ba a kuma jin kukan shanu. Tsuntsaye sararin sama sun gudu namun jeji ma duk sun watse.
I will sing a song of mourning and wailing for the mountains, and a funeral song will be sung for the meadows. For they are burned so no one can pass through them. They will not hear the sound of any cattle. The birds of the skies and the animals have all fled away.
11 “Zan mai da Urushalima tsibin kufai, wurin zaman diloli; zan kuma lalace garuruwan Yahuda saboda haka ba wanda zai zauna a can.”
So I will turn Jerusalem into piles of ruins, a hideout for jackals. I will make Judah's cities ruined places without inhabitants.”
12 Wane mutum ne yana da isashiyar hikimar fahimtar wannan? Wa Ubangiji ya umarta da zai iya yin bayani? Me ya sa aka lalace ƙasar ta zama kufai kamar hamada da ba wanda zai iya ratsa ta?
What man is wise enough to understand this? To whom has the mouth of Yahweh spoken, and he will declare it? Why has the land perished and been destroyed like the wilderness that no one can pass through?
13 Ubangiji ya ce, “Domin sun bar dokata, wadda na sa a gabansu; ba su yi biyayya da ni ko su bi dokata ba.
Yahweh says, “It is because they have abandoned my law that I set before them, because they do not listen to my voice or walk by it.
14 A maimako, sun bi taurin zuciyarsu; suka bi Ba’al, yadda kakanninsu suka koya musu.”
It is because they have walked by their stubborn hearts and have followed the Baals as their fathers taught them to do.
15 Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa, “Ga shi zan sa wannan mutane su ci abinci mai ɗaci su kuma sha ruwan dafi.
Therefore Yahweh of hosts, the God of Israel, says this, 'See, I am about to make this people eat wormwood and drink poisonous water.
16 Zan watsar da su a cikin al’ummai da su da kakanninsu ba su sani ba, zan kuma fafare su da takobi sai na hallaka su.”
Then I will scatter them among the nations that they have not known, neither they nor their ancestors. I will send out a sword after them until I have completely destroyed them.'”
17 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ku lura yanzu! Ku kira mata masu makoki su zo ku aika wa gwanaye a cikinsu su zo.
Yahweh of hosts says this, “Think about this: Summon funeral singers; let them come. Send out for women skilled at lamenting; let them come.
18 Bari su zo da sauri su yi kuka a kanmu sai idanunmu sun cika da hawaye giranmu kuma su jiƙe sharkaf.
Let them hurry and sing a mournful song over us, so our eyes may run with tears and our eyelids flow with water.
19 An ji karar kuka daga Sihiyona cewa, ‘Duba yadda muka lalace! Duba irin babban kunyar da muka sha! Dole mu bar ƙasar domin gidajenmu sun lalace.’”
For the sound of wailing is heard in Zion, 'How we are devastated. We are greatly ashamed, for we have abandoned the land since they tore down our houses.'
20 Yanzu, ya mata, ku ji maganar Ubangiji; ku buɗe kunnuwanku ga maganar bakina. Ku koya wa’yan matanku yadda za su yi kuka; ku koya wa juna makoki.
So you women, hear Yahweh's word; pay attention to the messages that come from his mouth. Then teach your daughters a mourning song, and each neighbor woman a funeral song.
21 Mutuwa ta haura ta tagoginmu ta kuma shiga katangarmu; ta karkashe’ya’ya a tituna ta kuma karkashe samari a dandali.
For death has come through our windows; it goes into our palaces. It destroys children from outside, and young men in the city squares.
22 Ka ce, “Ga abin da Ubangiji ya furta, “‘Gawawwakin mutane za su fāɗi kamar juji a fili, kamar hatsin da aka yanka a bayan mai girbi, da ba mai tara su.’”
Declare this, 'This is Yahweh's declaration—the corpses of men will fall like dung in the fields, and like grain stalks after the reapers, and there will be no one to gather them.'”
23 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada mai hikima ya yi fariya da hikimarsa ko mai ƙarfi ya yi fariya da ƙarfinsa ko mai arziki ya yi fariya da arzikinsa,
Yahweh says this, “Do not let the wise man take pride in his wisdom, or the warrior in his might. Do not let the wealthy man take pride in his riches.
24 amma bari shi wanda yake taƙama ya yi taƙama da wannan, cewa ya fahimci ya kuma san ni, cewa ni ne Ubangiji, wanda yake yin alheri, gaskiya da kuma adalci a duniya, gama a waɗannan ne nake jin daɗi,” in ji Ubangiji.
For if a man takes pride in anything, let it be in this, that he has insight and knows me. For I am Yahweh, who acts with covenant loyalty, justice and righteousness on earth. For it is in these that I take pleasure —this is Yahweh's declaration.”
25 “Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan hukunta dukan waɗanda aka yi musu kaciya kawai a jiki,
“See, days are coming—this is Yahweh's declaration—when I will punish all the circumcised who are such only in their body.
26 Masar, Yahuda, Edom, Ammon, Mowab da dukan waɗanda suke zaune a hamada a wurare masu nisa. Gama dukan waɗannan al’ummai marasa kaciya ne, har dukan gidan Isra’ila ma marasa kaciya ne a zuciya.”
I will punish Egypt and Judah, Edom, the people of Ammon, Moab, and all the people who cut the hair on their heads very short. For all these nations are uncircumcised, and all the house of Israel has an uncircumcised heart.”

< Irmiya 9 >