< Irmiya 9 >

1 Da ma kaina maɓulɓulan ruwa ne idanuna kuma maɓulɓulan hawaye! Da sai in yi kuka dare da rana saboda mutanena da aka kashe.
Who makes my head waters, And my eye a fountain of tears? And I weep by day and by night, For the wounded of the daughter of my people.
2 Da ma a hamada ina da wurin da matafiye za su sauka, don in bar mutanena in tafi in bar su; gama dukansu mazinata ne, taron mutane marasa aminci.
Who gives me in a wilderness A lodging-place for travelers? And I leave my people, and go from them, For all of them [are] adulterers, An assembly of treacherous ones.
3 “Sun tanƙwasa harshensu kamar baka, don su harba ƙarya; ba da gaskiya ba ne suke nasara a cikin ƙasar. Sukan tashi daga wannan zunubi zuwa wancan; ba su san ni ba,” in ji Ubangiji.
“And they bend their tongue, Their bow [is] a lie, And they have not been mighty for steadfastness in the land, For they have gone forth from evil to evil, And they have not known Me,” A declaration of YHWH!
4 “Ka yi hankali da abokanka; kada ka amince da’yan’uwanka. Gama kowane ɗan’uwa munafuki ne, kowane aboki kuma mai kushe ne.
“You each beware of his friend, And do not trust any brother, For every brother utterly supplants, For every friend slanderously walks,
5 Aboki kan ruɗi aboki, ba mai faɗar gaskiya. Sun koya wa harshensu faɗar ƙarya; sun gajiyar da kansu da yin zunubi.
And they each mock at his friend, And they do not speak truth, They taught their tongue to speak falsehood, They have labored to commit iniquity.
6 Kai kana zama a tsakiyar ruɗu; cikin ruɗunsu sun ƙi su san ni,” in ji Ubangiji.
Your dwelling [is] in the midst of deceit, Through deceit they refused to know Me,” A declaration of YHWH.
7 Saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ga shi zan tace in kuma gwada su, gama me kuwa zan yi saboda zunubin mutanena?
Therefore, thus said YHWH of Hosts: “Behold, I am refining them, and have tried them, For how do I deal with the daughter of My people?
8 Harshensu kibiya ce mai dafi; yana magana da ruɗu. Da bakinsa kowa yana maganar alheri da maƙwabcinsa, amma a zuciyarsa ya sa masa tarko.
Their tongue [is] a slaughtering arrow, It has spoken deceit in its mouth, It speaks peace with its neighbor, And in its heart it lays its ambush,
9 Bai kamata in hukunta su saboda wannan ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata in ɗau fansa a kan irin al’umma kamar wannan ba?”
Do I not see after them for these things?” A declaration of YHWH, “Does My soul not avenge itself against a nation such as this?”
10 Zan yi kuka in yi kururuwa saboda duwatsu in kuma yi makoki game da wuraren kiwon hamada. Sun zama kango ba wanda yake bi cikinta, ba a kuma jin kukan shanu. Tsuntsaye sararin sama sun gudu namun jeji ma duk sun watse.
I lift up weeping and wailing for the mountains, And a lamentation for the habitations of the wilderness, For they have been burned up without any passing over, Nor have they heard the voice of livestock, From the bird of the heavens and to the beast—they have fled, They have gone.
11 “Zan mai da Urushalima tsibin kufai, wurin zaman diloli; zan kuma lalace garuruwan Yahuda saboda haka ba wanda zai zauna a can.”
“And I make Jerusalem become heaps, A habitation of dragons, And I make the cities of Judah a desolation, Without inhabitant.”
12 Wane mutum ne yana da isashiyar hikimar fahimtar wannan? Wa Ubangiji ya umarta da zai iya yin bayani? Me ya sa aka lalace ƙasar ta zama kufai kamar hamada da ba wanda zai iya ratsa ta?
Who [is] the wise man? And he understands this, And he to whom the mouth of YHWH spoke? And he declares it, For why has the land perished? It has been burned up as a wilderness, Without any passing through.
13 Ubangiji ya ce, “Domin sun bar dokata, wadda na sa a gabansu; ba su yi biyayya da ni ko su bi dokata ba.
And YHWH says: “Because of their forsaking My law that I set before them, And they have not listened to My voice nor walked in it,
14 A maimako, sun bi taurin zuciyarsu; suka bi Ba’al, yadda kakanninsu suka koya musu.”
And they walk after the stubbornness of their heart, And after the Ba‘alim, That their fathers taught them,”
15 Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa, “Ga shi zan sa wannan mutane su ci abinci mai ɗaci su kuma sha ruwan dafi.
Therefore, thus said YHWH of Hosts, God of Israel: “Behold, I am causing them—this people—to eat wormwood, And I have caused them to drink water of gall,
16 Zan watsar da su a cikin al’ummai da su da kakanninsu ba su sani ba, zan kuma fafare su da takobi sai na hallaka su.”
And I have scattered them among nations Which they did not know, they and their fathers, And have sent the sword after them, Until I have consumed them.”
17 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ku lura yanzu! Ku kira mata masu makoki su zo ku aika wa gwanaye a cikinsu su zo.
Thus said YHWH of Hosts: “Consider, and call for mourning women, And they come, And send to the wise women, And they come,
18 Bari su zo da sauri su yi kuka a kanmu sai idanunmu sun cika da hawaye giranmu kuma su jiƙe sharkaf.
And they hurry, and lift up a wailing for us. And tears run down our eyes, And waters flow from our eyelids.
19 An ji karar kuka daga Sihiyona cewa, ‘Duba yadda muka lalace! Duba irin babban kunyar da muka sha! Dole mu bar ƙasar domin gidajenmu sun lalace.’”
For a voice of wailing is heard from Zion: How we have been spoiled! We have been greatly ashamed, Because we have forsaken the land, Because they have cast down our dwelling places.”
20 Yanzu, ya mata, ku ji maganar Ubangiji; ku buɗe kunnuwanku ga maganar bakina. Ku koya wa’yan matanku yadda za su yi kuka; ku koya wa juna makoki.
But hear, you women, a word of YHWH, And your ear receives a word of His mouth, And teach your daughters wailing, And each her neighbor lamentation.
21 Mutuwa ta haura ta tagoginmu ta kuma shiga katangarmu; ta karkashe’ya’ya a tituna ta kuma karkashe samari a dandali.
For death has come up into our windows, It has come into our palaces, To cut off the suckling from outside, Young men from the broad places.
22 Ka ce, “Ga abin da Ubangiji ya furta, “‘Gawawwakin mutane za su fāɗi kamar juji a fili, kamar hatsin da aka yanka a bayan mai girbi, da ba mai tara su.’”
Speak thus, “A declaration of YHWH, And the carcass of man has fallen, As dung on the face of the field, And as a handful after the reaper, And there is none gathering.”
23 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada mai hikima ya yi fariya da hikimarsa ko mai ƙarfi ya yi fariya da ƙarfinsa ko mai arziki ya yi fariya da arzikinsa,
Thus said YHWH: “Do not let the wise boast himself in his wisdom, Nor let the mighty boast himself in his might, Do not let the rich boast himself in his riches,
24 amma bari shi wanda yake taƙama ya yi taƙama da wannan, cewa ya fahimci ya kuma san ni, cewa ni ne Ubangiji, wanda yake yin alheri, gaskiya da kuma adalci a duniya, gama a waɗannan ne nake jin daɗi,” in ji Ubangiji.
But let the boaster boast himself in this, In understanding and knowing Me, For I [am] YHWH, doing kindness, Judgment, and righteousness, in the earth, For I have delighted in these,” A declaration of YHWH.
25 “Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan hukunta dukan waɗanda aka yi musu kaciya kawai a jiki,
“Behold, days are coming,” A declaration of YHWH, “And I have laid a charge on all circumcised in the foreskin,
26 Masar, Yahuda, Edom, Ammon, Mowab da dukan waɗanda suke zaune a hamada a wurare masu nisa. Gama dukan waɗannan al’ummai marasa kaciya ne, har dukan gidan Isra’ila ma marasa kaciya ne a zuciya.”
On Egypt, and on Judah, and on Edom, And on the sons of Ammon, and on Moab, And on all cutting the corner [of the beard], Who are dwelling in the wilderness, For all the nations [are] uncircumcised, And all the house of Israel [are] uncircumcised in heart!”

< Irmiya 9 >