< Irmiya 9 >

1 Da ma kaina maɓulɓulan ruwa ne idanuna kuma maɓulɓulan hawaye! Da sai in yi kuka dare da rana saboda mutanena da aka kashe.
How I wish my head was a spring of water, and my eyes a fountain of tears! Then I would weep day and night over all my people who have been killed.
2 Da ma a hamada ina da wurin da matafiye za su sauka, don in bar mutanena in tafi in bar su; gama dukansu mazinata ne, taron mutane marasa aminci.
I wish I had a temporary shelter in the desert—I would give up on my people and leave them, because they're all adulterers, a bunch of traitors!
3 “Sun tanƙwasa harshensu kamar baka, don su harba ƙarya; ba da gaskiya ba ne suke nasara a cikin ƙasar. Sukan tashi daga wannan zunubi zuwa wancan; ba su san ni ba,” in ji Ubangiji.
Their words are like arrows shot from a bow. Lies win out over the truth throughout the country. They go from one evil thing to the next, forgetting all about me, declares the Lord.
4 “Ka yi hankali da abokanka; kada ka amince da’yan’uwanka. Gama kowane ɗan’uwa munafuki ne, kowane aboki kuma mai kushe ne.
Everyone, watch out for your friends! Don't even trust your brother! Every brother is deceitful, and every friend slanders other people.
5 Aboki kan ruɗi aboki, ba mai faɗar gaskiya. Sun koya wa harshensu faɗar ƙarya; sun gajiyar da kansu da yin zunubi.
Everyone betrays their friends; no one tells the truth. They've made themselves into expert liars; they tire themselves out doing wrong.
6 Kai kana zama a tsakiyar ruɗu; cikin ruɗunsu sun ƙi su san ni,” in ji Ubangiji.
Everyone exploits each other, and in all their lies they don't want to know me, declares the Lord.
7 Saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ga shi zan tace in kuma gwada su, gama me kuwa zan yi saboda zunubin mutanena?
So this is what the Lord Almighty says: Look, I'm going to test them and purify them like metal in a furnace. What else can I do because of what my people have done?
8 Harshensu kibiya ce mai dafi; yana magana da ruɗu. Da bakinsa kowa yana maganar alheri da maƙwabcinsa, amma a zuciyarsa ya sa masa tarko.
Their words are arrows that kill; they always tell lies. They're nice to their friends on the outside while plotting against them inside.
9 Bai kamata in hukunta su saboda wannan ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata in ɗau fansa a kan irin al’umma kamar wannan ba?”
Shouldn't I punish them for all this? declares the Lord. Shouldn't I retaliate for what this nation has done?
10 Zan yi kuka in yi kururuwa saboda duwatsu in kuma yi makoki game da wuraren kiwon hamada. Sun zama kango ba wanda yake bi cikinta, ba a kuma jin kukan shanu. Tsuntsaye sararin sama sun gudu namun jeji ma duk sun watse.
I will weep and wail for the mountains, I will sing a funeral song over the pastures in the countryside, because they have been so badly burned that no one can pass through, and there are no cattle to make any noise. The birds have flown and the wild animals have run away.
11 “Zan mai da Urushalima tsibin kufai, wurin zaman diloli; zan kuma lalace garuruwan Yahuda saboda haka ba wanda zai zauna a can.”
I'm going to make Jerusalem into a heap of rubble, a place where jackals live. I will destroy the towns of Judah, leaving them empty.
12 Wane mutum ne yana da isashiyar hikimar fahimtar wannan? Wa Ubangiji ya umarta da zai iya yin bayani? Me ya sa aka lalace ƙasar ta zama kufai kamar hamada da ba wanda zai iya ratsa ta?
Who is wise enough to understand this? Has the Lord told anyone so they can explain what's happened? Why has the land been destroyed and burned so it's like a desert, so no one can pass through it?
13 Ubangiji ya ce, “Domin sun bar dokata, wadda na sa a gabansu; ba su yi biyayya da ni ko su bi dokata ba.
The Lord replied, It's because they have given up keeping my laws that I placed before them. They haven't followed them; they haven't done what I told them.
14 A maimako, sun bi taurin zuciyarsu; suka bi Ba’al, yadda kakanninsu suka koya musu.”
On the contrary, they have followed their own stubborn way of thinking, and went to worship the Baals, just as their forefathers taught them.
15 Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa, “Ga shi zan sa wannan mutane su ci abinci mai ɗaci su kuma sha ruwan dafi.
So this is what the Lord Almighty, the God of Israel, says: Watch out! I will give these people wormwood to eat and poisoned water to drink.
16 Zan watsar da su a cikin al’ummai da su da kakanninsu ba su sani ba, zan kuma fafare su da takobi sai na hallaka su.”
I'm about to scatter them among nations unfamiliar to them and their forefathers, and I will send enemies with swords to chase after them until I have wiped them out.
17 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ku lura yanzu! Ku kira mata masu makoki su zo ku aika wa gwanaye a cikinsu su zo.
This is what the Lord Almighty says: Be aware of what's happening! Call for the professional women mourners, ask for the best of them.
18 Bari su zo da sauri su yi kuka a kanmu sai idanunmu sun cika da hawaye giranmu kuma su jiƙe sharkaf.
Have them come as quickly as possible, and sing a funeral song about us, so we can cry our eyes out, so our tears will flow like streams.
19 An ji karar kuka daga Sihiyona cewa, ‘Duba yadda muka lalace! Duba irin babban kunyar da muka sha! Dole mu bar ƙasar domin gidajenmu sun lalace.’”
The sound of weeping comes from Zion, “We're completely devastated! We're totally ashamed, because we've had to abandon our country, because our houses have been demolished.”
20 Yanzu, ya mata, ku ji maganar Ubangiji; ku buɗe kunnuwanku ga maganar bakina. Ku koya wa’yan matanku yadda za su yi kuka; ku koya wa juna makoki.
Women, listen to the Lord's message, hear what he has to say. Teach your daughters to mourn and sing songs of sadness.
21 Mutuwa ta haura ta tagoginmu ta kuma shiga katangarmu; ta karkashe’ya’ya a tituna ta kuma karkashe samari a dandali.
Death has slipped in through our windows; it has come into our fortresses. It has killed the children playing in the streets and the young people gathering in the town squares.
22 Ka ce, “Ga abin da Ubangiji ya furta, “‘Gawawwakin mutane za su fāɗi kamar juji a fili, kamar hatsin da aka yanka a bayan mai girbi, da ba mai tara su.’”
Tell everyone this is what the Lord says: Dead bodies will be left where they fall like manure in the fields, lying there like stalks of freshly-cut grain behind the reaper, with no one to collect them.
23 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada mai hikima ya yi fariya da hikimarsa ko mai ƙarfi ya yi fariya da ƙarfinsa ko mai arziki ya yi fariya da arzikinsa,
This is what the Lord says: The wise shouldn't boast about their wisdom. The strong shouldn't boast about their strength. The rich shouldn't boast about their riches.
24 amma bari shi wanda yake taƙama ya yi taƙama da wannan, cewa ya fahimci ya kuma san ni, cewa ni ne Ubangiji, wanda yake yin alheri, gaskiya da kuma adalci a duniya, gama a waɗannan ne nake jin daɗi,” in ji Ubangiji.
Anyone who wants to boast should boast that they really know and understand me, recognizing that I am the Lord who acts with trustworthy love, who shows fairness, and who does what is right everywhere on earth, because these mean the most to me, declares the Lord.
25 “Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan hukunta dukan waɗanda aka yi musu kaciya kawai a jiki,
Watch out, for the time is coming, declares the Lord, when I will punish all who are only physically circumcised.
26 Masar, Yahuda, Edom, Ammon, Mowab da dukan waɗanda suke zaune a hamada a wurare masu nisa. Gama dukan waɗannan al’ummai marasa kaciya ne, har dukan gidan Isra’ila ma marasa kaciya ne a zuciya.”
Egypt, Judah, Edom, Ammon, Moab, and all the desert people who trim their hair on the sides of their heads—all these nations are uncircumcised, and all the Israelites are spiritually uncircumcised.

< Irmiya 9 >