< Irmiya 8 >

1 “‘A wancan lokaci, in ji Ubangiji, za a fitar da ƙasusuwan sarakuna da na shugabannin Yahuda, ƙasusuwan firistoci da na annabawa, da kuma ƙasusuwan mutanen Urushalima daga kaburbura.
“‘O zaman, diyor RAB, Yahuda krallarıyla önderlerinin, kâhinlerin, peygamberlerin, Yeruşalim'de yaşamış olanların kemikleri mezarlarından çıkarılacak.
2 Za a shimfiɗa su a rana da wata da kuma dukan taurarin sammai, waɗanda suka ƙaunata suka kuma bauta wa, waɗanda suka bi suka nemi shawarar suka kuma yi wa sujada. Ba za a tattara su ko a binne su ba, amma za su zama kamar juji a jibge a ƙasa.
Toplanmayacak, gömülmeyecek kemikler, toprağın üzerinde gübre gibi olacaklar. Yeruşalim halkının sevdiği, kulluk ettiği, izlediği, danıştığı, taptığı güneşin, ayın, gök cisimlerinin önüne serilecekler.
3 Duk inda na kore su zuwa, dukan waɗanda suka ragu na wannan muguwar al’umma za su gwammaci mutuwa da rai, in ji Ubangiji Maɗaukaki.’
Bu kötü ulustan bütün sağ kalanlar, kendilerini sürdüğüm yerlerde yaşayanlar, ölümü yaşama yeğleyecekler. Her Şeye Egemen RAB böyle diyor.’
4 “Fada musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Sa’ad da mutane suka fāɗi, ba sa tashi ne? Sa’ad da mutum ya kauce, ba ya dawowa?
“Onlara de ki, ‘RAB şöyle diyor: “‘İnsan yere düşer de kalkmaz mı, Yoldan sapar da geri dönmez mi?
5 To, me ya sa waɗannan mutane suka kauce? Me ya sa Urushalima kullum take kaucewa? Sun manne wa ƙarya; suka ƙi su dawo.
Öyleyse neden bu halk yoldan saptı? Neden Yeruşalim sürekli döneklik ediyor? Hileye yapışıyor, Geri dönmeyi reddediyorlar.
6 Na saurara sosai, amma ba su faɗi wata maganar kirki ba. Ba wanda ya tuba daga muguntarsa, sai ma cewa yake, “Me na yi?” Kowa ta kai-ta-kai yake kamar dokin da ya kutsa kai a fagen fama.
Dikkatle dinledim, Ama doğru söylemiyorlar. Kimse, ne yaptım, diyerek kötülüğünden pişmanlık duymuyor. Savaşta seğirten at gibi Herkes kendi yoluna gidiyor.
7 Ko shamuwa ta sararin sama ma takan san lokutan da aka tsara mata, kurciya, mashirare da kuma zalɓe sukan lura da lokacin ƙauransu. Amma mutanena ba su san abubuwan da Ubangiji yake bukata ba.
Gökteki leylek bile Belli mevsimlerini bilir. Kumru da kırlangıç da turna da Göç etme zamanını gözetir. Oysa halkım buyruklarımı bilmez.
8 “‘Yaya za ku ce, “Muna da hikima, gama muna da dokar Ubangiji,” alhali alƙalamin ƙarya na magatakarda ya yi ƙarya?
“‘Nasıl, biz bilge kişileriz, RAB'bin Yasası bizdedir, diyebiliyorsunuz? İşte, bilginlerin yalancı kalemi Yasayı yalana çevirmiş.
9 Za a kunyatar da masu hikima; za su yi fargaba a kuma kama su. Da yake sun ƙi maganar Ubangiji, wace irin hikima kuka ce kuke da ita?
Bilgeler utandırıldı, Yıldırılıp ele geçirildi. RAB'bin sözünü reddettiler. Nasıl bir bilgelikmiş onlarınki?
10 Saboda haka zan ba da matansu ga waɗansu gonakinsu kuma ga waɗansu da suka ci da yaƙi. Tun daga ƙarami har zuwa babba, kowannensu yana haɗamar cin muguwar riba; har da annabawa da firistoci ma, kowannensu yana ƙarya.
Bundan ötürü karılarını başkalarına, Tarlalarını sahiplenecek yeni kişilere vereceğim. Küçük büyük herkes kazanç peşinde, Peygamberler, kâhinler, hepsi halkı aldatıyor.
11 Sukan ɗaura mikin mutanena sai ka ce mikin ba shi da matsala. Suna cewa, “Lafiya, Lafiya,” alhali kuwa ba lafiya.
Esenlik yokken, Esenlik, esenlik, diyerek Halkımın yarasını sözde iyileştirdiler.
12 Sukan ji kunyar halin banƙyamarsu kuwa? Sam, ba su da kunya ko kaɗan; ba su ma san yadda za su ji kunya ba. Saboda haka sukan fāɗi tare da fāɗaɗɗu; za su fāɗi sa’ad da aka hukunta su, in ji Ubangiji.
Yaptıkları iğrençliklerden utandılar mı? Hayır, ne utanması? Kızarıp bozarmanın ne olduğunu bile bilmiyorlar. Bu yüzden onlar da düşenlerin arasında yer alacak, Cezalandırıldıklarında sendeleyip düşecekler’ diyor RAB.
13 “‘Zan ƙwace girbinsu, in ji Ubangiji. Ba a za sami inabi a kuringa ba. Ba za a sami’ya’ya a itacen ɓaure ba, ganyayensu kuwa za su bushe. Abin da na ba su za a ƙwace.’”
“‘Onları büsbütün yok edeceğim, diyor RAB, Ne asmada üzüm kalacak, Ne incir ağacında incir. Yaprakları solup kuruyacak. Onlara ne verdiysem, Ellerinden alınacak.’”
14 Me ya sa muke zama a nan? Mu tattaru! Mu gudu zuwa birane masu katanga mu mutu a can! Gama Ubangiji Allahnmu ya ƙaddara mana mutuwa ya kuma ba mu ruwan dafi mu sha, domin mun yi masa zunubi.
“Neden burada oturup duruyoruz? Toplanalım da surlu kentlere kaçalım, Orada ölelim! Tanrımız RAB bizi ölüme terk etti, Bize zehirli su içirdi. Çünkü O'na karşı günah işledik.
15 Mun sa zuciya ga salama amma ba lafiya, mun sa zuciya ga lokacin warkarwa amma sai ga razana.
Esenlik bekledik, iyilik gelmedi. Şifa umduk, yılgınlık bulduk.
16 Daga Dan ana jin tirjin dawakan abokin gāba; da jin haniniyar ingarmunsu dukan ƙasar ta girgiza. Sun zo su cinye ƙasar da kome da yake cikinta, birni da dukan mazaunanta.
Düşman atlarının hırıltısı Dan bölgesinden duyuluyor, Aygırlarının kişnemesinden Bütün ülke titriyor. Ülkeyi ve içindeki her şeyi, Kenti ve orada yaşayanları Yok etmeye geliyorlar.”
17 “Duba, zan aika macizai masu dafi a cikinku, kāsā, waɗanda ba su da maƙari, za su kuwa sassare ku,” in ji Ubangiji.
“Bakın, aranıza yılanlar, Büyüden etkilenmeyen engerekler göndereceğim, Sizi sokacaklar” diyor RAB.
18 Ya mai ta’aziyyata a cikin baƙin ciki, zuciyata ta ɓaci ƙwarai.
Üzüntüm avutulamaz, Yüreğim baygın,
19 Ka saurari kukan mutanena daga ƙasa mai nisa suna cewa, “Ubangiji ba ya a Sihiyona ne? Sarkinta ba ya can ne kuma?” “Me ya sa suka tsokane ni da gumakansu har na yi fushi, da baƙin gumakansu marasa amfani?”
Ülkenin en uzak köşelerinden Halkımın feryadını dinleyin: “RAB Siyon'da değil mi? Kralı orada değil mi?” RAB, “Putlarıyla, İşe yaramaz yabancı ilahlarıyla Neden öfkelendiriyorlar beni?” diyor.
20 “Girbi ya wuce, damuna ta ƙare, ba a kuwa cece mu ba.”
“Ürün biçme zamanı geçti, Yaz sona erdi, Biz ise kurtulmadık” diye haykırıyorlar.
21 Da yake an ragargazar da mutanena, an ragargaza ni ke nan; na yi kuka, tsoro ya kama ni.
Halkımın yarasından ben de yaralandım. Yasa büründüm, dehşete düştüm.
22 Ba magani ne a Gileyad? Ba likita ne a can? To, me ya sa ba warkarwa wa raunin mutanena?
Gilat'ta merhem yok mu, Hekim yok mu? Öyleyse halkımın yarası neden iyi edilmedi?

< Irmiya 8 >