< Irmiya 8 >

1 “‘A wancan lokaci, in ji Ubangiji, za a fitar da ƙasusuwan sarakuna da na shugabannin Yahuda, ƙasusuwan firistoci da na annabawa, da kuma ƙasusuwan mutanen Urushalima daga kaburbura.
“Naquele tempo”, diz Javé, “eles trarão os ossos dos reis de Judá, os ossos de seus príncipes, os ossos dos sacerdotes, os ossos dos profetas e os ossos dos habitantes de Jerusalém, para fora de seus túmulos”.
2 Za a shimfiɗa su a rana da wata da kuma dukan taurarin sammai, waɗanda suka ƙaunata suka kuma bauta wa, waɗanda suka bi suka nemi shawarar suka kuma yi wa sujada. Ba za a tattara su ko a binne su ba, amma za su zama kamar juji a jibge a ƙasa.
Eles os espalharão diante do sol, da lua e de todo o exército do céu, que eles amaram, que serviram, depois dos quais caminharam, que procuraram e que adoraram. Eles não serão reunidos ou enterrados. Eles serão como esterco na superfície da terra.
3 Duk inda na kore su zuwa, dukan waɗanda suka ragu na wannan muguwar al’umma za su gwammaci mutuwa da rai, in ji Ubangiji Maɗaukaki.’
A morte será escolhida em vez da vida por todos os resíduos que restam desta família maligna, que permanecem em todos os lugares onde eu os conduzi”, diz Yahweh dos Exércitos.
4 “Fada musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Sa’ad da mutane suka fāɗi, ba sa tashi ne? Sa’ad da mutum ya kauce, ba ya dawowa?
“Além disso, você lhes dirá: 'Yahweh diz: “'Os homens caem e não se levantam de novo? Será que se vira costas e não se volta?
5 To, me ya sa waɗannan mutane suka kauce? Me ya sa Urushalima kullum take kaucewa? Sun manne wa ƙarya; suka ƙi su dawo.
Por que, então, o povo de Jerusalém caiu de volta por um retrocesso perpétuo? Eles se agarram ao engano. Eles se recusam a retornar.
6 Na saurara sosai, amma ba su faɗi wata maganar kirki ba. Ba wanda ya tuba daga muguntarsa, sai ma cewa yake, “Me na yi?” Kowa ta kai-ta-kai yake kamar dokin da ya kutsa kai a fagen fama.
Eu escutei e ouvi, mas eles não disseram o que é certo. Ninguém se arrepende de sua maldade, dizendo: “O que eu fiz”? Todos se voltam para seu curso, como um cavalo que se apressa de cabeça na batalha.
7 Ko shamuwa ta sararin sama ma takan san lokutan da aka tsara mata, kurciya, mashirare da kuma zalɓe sukan lura da lokacin ƙauransu. Amma mutanena ba su san abubuwan da Ubangiji yake bukata ba.
Sim, a cegonha no céu conhece os tempos que lhe foram indicados. A rola, a andorinha e a grua observam a hora de sua chegada; mas meu povo não conhece a lei de Yahweh.
8 “‘Yaya za ku ce, “Muna da hikima, gama muna da dokar Ubangiji,” alhali alƙalamin ƙarya na magatakarda ya yi ƙarya?
“'Como se diz: “Somos sábios, e a lei de Javé está conosco”? Mas, eis que a falsa caneta dos escribas fez disso uma mentira.
9 Za a kunyatar da masu hikima; za su yi fargaba a kuma kama su. Da yake sun ƙi maganar Ubangiji, wace irin hikima kuka ce kuke da ita?
Os homens sábios estão desapontados. Eles estão consternados e encurralados. Eis que eles rejeitaram a palavra de Javé. Que tipo de sabedoria está neles?
10 Saboda haka zan ba da matansu ga waɗansu gonakinsu kuma ga waɗansu da suka ci da yaƙi. Tun daga ƙarami har zuwa babba, kowannensu yana haɗamar cin muguwar riba; har da annabawa da firistoci ma, kowannensu yana ƙarya.
Portanto, darei suas esposas a outros e seus campos para aqueles que os possuirão. Para todos, desde o menor até o maior, a cobiça é dada à cobiça; desde o profeta até o sacerdote, todos negociam falsamente.
11 Sukan ɗaura mikin mutanena sai ka ce mikin ba shi da matsala. Suna cewa, “Lafiya, Lafiya,” alhali kuwa ba lafiya.
Eles curaram ligeiramente a ferida da filha do meu povo, dizendo, “Paz, paz”, quando não há paz.
12 Sukan ji kunyar halin banƙyamarsu kuwa? Sam, ba su da kunya ko kaɗan; ba su ma san yadda za su ji kunya ba. Saboda haka sukan fāɗi tare da fāɗaɗɗu; za su fāɗi sa’ad da aka hukunta su, in ji Ubangiji.
Eles tinham vergonha quando cometeram abominação? Não, eles não tinham vergonha nenhuma. Eles não conseguiam corar. Portanto, eles cairão entre aqueles que caem. No momento de sua visita, eles serão lançados para baixo, diz Yahweh.
13 “‘Zan ƙwace girbinsu, in ji Ubangiji. Ba a za sami inabi a kuringa ba. Ba za a sami’ya’ya a itacen ɓaure ba, ganyayensu kuwa za su bushe. Abin da na ba su za a ƙwace.’”
“'Eu os consumirei totalmente, diz Yahweh. Nenhuma uva estará na videira, sem figos na figueira, e a folha se desvanecerá. As coisas que eu lhes dei falecerão deles'”.
14 Me ya sa muke zama a nan? Mu tattaru! Mu gudu zuwa birane masu katanga mu mutu a can! Gama Ubangiji Allahnmu ya ƙaddara mana mutuwa ya kuma ba mu ruwan dafi mu sha, domin mun yi masa zunubi.
“Por que ficamos quietos? Monte-se! Vamos entrar nas cidades fortificadas, e vamos ficar em silêncio lá; para Yahweh nosso Deus nos colocou em silêncio, e nos deu água envenenada para beber, porque pecamos contra Yahweh.
15 Mun sa zuciya ga salama amma ba lafiya, mun sa zuciya ga lokacin warkarwa amma sai ga razana.
We buscou a paz, mas nenhum bem veio; e por um tempo de cura, e eis que o desânimo!
16 Daga Dan ana jin tirjin dawakan abokin gāba; da jin haniniyar ingarmunsu dukan ƙasar ta girgiza. Sun zo su cinye ƙasar da kome da yake cikinta, birni da dukan mazaunanta.
O cheiro de seus cavalos é ouvido de Dan. Toda a terra treme ao som do relinchar de seus fortes; pois eles vieram, e devoraram a terra e tudo o que nela existe, a cidade e aqueles que nela habitam”.
17 “Duba, zan aika macizai masu dafi a cikinku, kāsā, waɗanda ba su da maƙari, za su kuwa sassare ku,” in ji Ubangiji.
“Pois, eis que eu enviarei serpentes, vendedores entre vocês, que não será encantada; e eles o morderão”, diz Yahweh.
18 Ya mai ta’aziyyata a cikin baƙin ciki, zuciyata ta ɓaci ƙwarai.
Oh que eu poderia me consolar contra a tristeza! Meu coração está desmaiado dentro de mim.
19 Ka saurari kukan mutanena daga ƙasa mai nisa suna cewa, “Ubangiji ba ya a Sihiyona ne? Sarkinta ba ya can ne kuma?” “Me ya sa suka tsokane ni da gumakansu har na yi fushi, da baƙin gumakansu marasa amfani?”
Eis a voz do grito da filha do meu povo de uma terra que está muito distante: “Iahweh não está em Zion? O rei dela não está dentro dela?” “Por que eles me provocaram à raiva com suas imagens gravadas”, e com ídolos estrangeiros”...
20 “Girbi ya wuce, damuna ta ƙare, ba a kuwa cece mu ba.”
“A colheita é passada. O verão terminou, e nós não estamos salvos”.
21 Da yake an ragargazar da mutanena, an ragargaza ni ke nan; na yi kuka, tsoro ya kama ni.
Pela dor da filha do meu povo, eu estou ferido. Eu lamento. A consternação tomou conta de mim.
22 Ba magani ne a Gileyad? Ba likita ne a can? To, me ya sa ba warkarwa wa raunin mutanena?
Não há bálsamo em Gilead? Não há um médico lá? Por que então a saúde da filha do meu povo não está recuperada?

< Irmiya 8 >