< Irmiya 8 >

1 “‘A wancan lokaci, in ji Ubangiji, za a fitar da ƙasusuwan sarakuna da na shugabannin Yahuda, ƙasusuwan firistoci da na annabawa, da kuma ƙasusuwan mutanen Urushalima daga kaburbura.
استخوانهای پادشاهان یهودا واستخوانهای سرورانش و استخوانهای کهنه واستخوانهای انبیا و استخوانهای سکنه اورشلیم را از قبرهای ایشان بیرون خواهند‌آورد.۱
2 Za a shimfiɗa su a rana da wata da kuma dukan taurarin sammai, waɗanda suka ƙaunata suka kuma bauta wa, waɗanda suka bi suka nemi shawarar suka kuma yi wa sujada. Ba za a tattara su ko a binne su ba, amma za su zama kamar juji a jibge a ƙasa.
و آنهارا پیش آفتاب و ماه و تمامی لشکر آسمان که آنهارا دوست داشته و عبادت کرده و پیروی نموده وجستجو و سجده کرده‌اند پهن خواهند کرد و آنهارا جمع نخواهند نمود و دفن نخواهند کرد بلکه برروی زمین سرگین خواهد بود.۲
3 Duk inda na kore su zuwa, dukan waɗanda suka ragu na wannan muguwar al’umma za su gwammaci mutuwa da rai, in ji Ubangiji Maɗaukaki.’
و یهوه صبایوت می‌گوید که تمامی بقیه این قبیله شریر که باقی می‌مانند در هر مکانی که باقی‌مانده باشند و من ایشان را بسوی آن رانده باشم مرگ را بر حیات ترجیح خواهند داد.۳
4 “Fada musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Sa’ad da mutane suka fāɗi, ba sa tashi ne? Sa’ad da mutum ya kauce, ba ya dawowa?
«و ایشان را بگو خداوند چنین می‌فرماید: اگر کسی بیفتد آیا نخواهد برخاست و اگر کسی مرتد شود آیا بازگشت نخواهد نمود؟۴
5 To, me ya sa waɗannan mutane suka kauce? Me ya sa Urushalima kullum take kaucewa? Sun manne wa ƙarya; suka ƙi su dawo.
پس چرااین قوم اورشلیم به ارتداد دایمی مرتد شده‌اند وبه فریب متمسک شده، از بازگشت نمودن ابامی نمایند؟۵
6 Na saurara sosai, amma ba su faɗi wata maganar kirki ba. Ba wanda ya tuba daga muguntarsa, sai ma cewa yake, “Me na yi?” Kowa ta kai-ta-kai yake kamar dokin da ya kutsa kai a fagen fama.
من گوش خود را فرا داشته، شنیدم اما براستی تکلم ننمودند و کسی از شرارت خویش توبه نکرده و نگفته است چه کرده‌ام بلکه هر یک مثل اسبی که به جنگ می‌دود به راه خودرجوع می‌کند.۶
7 Ko shamuwa ta sararin sama ma takan san lokutan da aka tsara mata, kurciya, mashirare da kuma zalɓe sukan lura da lokacin ƙauransu. Amma mutanena ba su san abubuwan da Ubangiji yake bukata ba.
لقلق نیز در هوا موسم خود رامی داند و فاخته و پرستوک و کلنک زمان آمدن خود را نگاه می‌دارند لیکن قوم من احکام خداوندرا نمی دانند.۷
8 “‘Yaya za ku ce, “Muna da hikima, gama muna da dokar Ubangiji,” alhali alƙalamin ƙarya na magatakarda ya yi ƙarya?
چگونه می‌گویید که ما حکیم هستیم و شریعت خداوند با ما است. به تحقیق قلم کاذب کاتبان به دروغ عمل می‌نماید.۸
9 Za a kunyatar da masu hikima; za su yi fargaba a kuma kama su. Da yake sun ƙi maganar Ubangiji, wace irin hikima kuka ce kuke da ita?
حکیمان شرمنده و مدهوش و گرفتار شده‌اند. اینک کلام خداوند را ترک نموده‌اند پس چه نوع حکمتی دارند.۹
10 Saboda haka zan ba da matansu ga waɗansu gonakinsu kuma ga waɗansu da suka ci da yaƙi. Tun daga ƙarami har zuwa babba, kowannensu yana haɗamar cin muguwar riba; har da annabawa da firistoci ma, kowannensu yana ƙarya.
بنابراین زنان ایشان را به دیگران خواهم داد و مزرعه های ایشان را به مالکان دیگر. زیرا که جمیع ایشان چه خرد و چه بزرگ پر از طمع می‌باشند و همگی ایشان چه نبی و چه کاهن به فریب عمل می‌نمایند.۱۰
11 Sukan ɗaura mikin mutanena sai ka ce mikin ba shi da matsala. Suna cewa, “Lafiya, Lafiya,” alhali kuwa ba lafiya.
وجراحات قوم مرا اندک شفایی داده‌اند چونکه می‌گویند سلامتی است، سلامتی است، با آنکه سلامتی نیست.۱۱
12 Sukan ji kunyar halin banƙyamarsu kuwa? Sam, ba su da kunya ko kaɗan; ba su ma san yadda za su ji kunya ba. Saboda haka sukan fāɗi tare da fāɗaɗɗu; za su fāɗi sa’ad da aka hukunta su, in ji Ubangiji.
آیا چون مرتکب رجاسات شدند خجل گردیدند؟ نی ابد خجل نشدند بلکه حیا را احساس ننمودند بنابراین خداوندمی گوید: در میان افتادگان خواهند افتاد و حینی که من به ایشان عقوبت رسانم خواهند لغزید.»۱۲
13 “‘Zan ƙwace girbinsu, in ji Ubangiji. Ba a za sami inabi a kuringa ba. Ba za a sami’ya’ya a itacen ɓaure ba, ganyayensu kuwa za su bushe. Abin da na ba su za a ƙwace.’”
خداوند می‌گوید: «ایشان را بالکل تلف خواهم نمود که نه انگور بر مو و نه انجیر بردرخت انجیر یافت شود و برگها پژمرده خواهدشد و آنچه به ایشان بدهم از ایشان زایل خواهدشد.»۱۳
14 Me ya sa muke zama a nan? Mu tattaru! Mu gudu zuwa birane masu katanga mu mutu a can! Gama Ubangiji Allahnmu ya ƙaddara mana mutuwa ya kuma ba mu ruwan dafi mu sha, domin mun yi masa zunubi.
پس ما چرا می‌نشینیم؟ جمع بشوید تا به شهرهای حصاردار داخل شویم و در آنها ساکت باشیم. زیرا که یهوه خدای ما ما را ساکت گردانیده و آب تلخ به ما نوشانیده است زانرو که به خداوندگناه ورزیده‌ایم.۱۴
15 Mun sa zuciya ga salama amma ba lafiya, mun sa zuciya ga lokacin warkarwa amma sai ga razana.
برای سلامتی انتظار کشیدیم اما هیچ خیر حاصل نشد و برای زمان شفا و اینک آشفتگی پدید آمد.۱۵
16 Daga Dan ana jin tirjin dawakan abokin gāba; da jin haniniyar ingarmunsu dukan ƙasar ta girgiza. Sun zo su cinye ƙasar da kome da yake cikinta, birni da dukan mazaunanta.
صهیل اسبان او از دان شنیده شد و از صدای شیهه زورآورانش تمامی زمین متزلزل گردید زیرا که آمده‌اند و زمین و هرچه در آن است و شهر و ساکنانش را خورده‌اند.۱۶
17 “Duba, zan aika macizai masu dafi a cikinku, kāsā, waɗanda ba su da maƙari, za su kuwa sassare ku,” in ji Ubangiji.
زیرا خداوند می‌گوید: «اینک من در میان شمامارها و افعیها خواهم فرستاد که آنها را افسون نتوان کرد و شما را خواهند گزید.»۱۷
18 Ya mai ta’aziyyata a cikin baƙin ciki, zuciyata ta ɓaci ƙwarai.
کاش که ازغم خود تسلی می‌یافتم. دل من در اندرونم ضعف بهم رسانیده است.۱۸
19 Ka saurari kukan mutanena daga ƙasa mai nisa suna cewa, “Ubangiji ba ya a Sihiyona ne? Sarkinta ba ya can ne kuma?” “Me ya sa suka tsokane ni da gumakansu har na yi fushi, da baƙin gumakansu marasa amfani?”
اینک آواز تضرع دختر قوم من از زمین دور می‌آید که آیا خداوند در صهیون نیست و مگر پادشاهش در آن نیست پس چراخشم مرا به بتهای خود و اباطیل بیگانه به هیجان آوردند؟۱۹
20 “Girbi ya wuce, damuna ta ƙare, ba a kuwa cece mu ba.”
موسم حصاد گذشت و تابستان تمام شد و ما نجات نیافتیم.۲۰
21 Da yake an ragargazar da mutanena, an ragargaza ni ke nan; na yi kuka, tsoro ya kama ni.
به‌سبب جراحت دخترقوم خود مجروح شده و ماتم گرفته‌ام و حیرت مرا فرو گرفته است.۲۱
22 Ba magani ne a Gileyad? Ba likita ne a can? To, me ya sa ba warkarwa wa raunin mutanena?
آیا بلسان در جلعاد نیست و طبیبی در آن نی؟ پس دختر قوم من چرا شفانیافته است؟۲۲

< Irmiya 8 >