< Irmiya 8 >
1 “‘A wancan lokaci, in ji Ubangiji, za a fitar da ƙasusuwan sarakuna da na shugabannin Yahuda, ƙasusuwan firistoci da na annabawa, da kuma ƙasusuwan mutanen Urushalima daga kaburbura.
“‘Ngalesosikhathi, kutsho uThixo, amathambo amakhosi akoJuda lawezikhulu zakhona, amathambo abaphristi lawabaphrofethi, kanye lamathambo abantu baseJerusalema azakhutshwa emangcwabeni awo.
2 Za a shimfiɗa su a rana da wata da kuma dukan taurarin sammai, waɗanda suka ƙaunata suka kuma bauta wa, waɗanda suka bi suka nemi shawarar suka kuma yi wa sujada. Ba za a tattara su ko a binne su ba, amma za su zama kamar juji a jibge a ƙasa.
Azachaywa elangeni lasenyangeni lakuzo zonke izinkanyezi zasemazulwini, abakuthandayo bakukhonza njalo abakulandelayo bakubuza bakudumisa. Kawayikubuthwa loba angcwatshwe, kodwa azakuba njengezibi phezu komhlabathi.
3 Duk inda na kore su zuwa, dukan waɗanda suka ragu na wannan muguwar al’umma za su gwammaci mutuwa da rai, in ji Ubangiji Maɗaukaki.’
Loba kungaphi engibaxotshela khona, bonke abasilayo balesisizwe esibi bazakhetha ukufa kulokuphila, kutsho uThixo uSomandla.’”
4 “Fada musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Sa’ad da mutane suka fāɗi, ba sa tashi ne? Sa’ad da mutum ya kauce, ba ya dawowa?
“Wothi kubo, ‘UThixo uthi: Abantu bangawa, kabavuki na? Omunye angaphambuka, kaphenduki na?
5 To, me ya sa waɗannan mutane suka kauce? Me ya sa Urushalima kullum take kaucewa? Sun manne wa ƙarya; suka ƙi su dawo.
Pho kungani abantu laba bedukile? Kungani iJerusalema lihlala liseduka? Bayanamathela enkohlisweni, bayala ukuphenduka.
6 Na saurara sosai, amma ba su faɗi wata maganar kirki ba. Ba wanda ya tuba daga muguntarsa, sai ma cewa yake, “Me na yi?” Kowa ta kai-ta-kai yake kamar dokin da ya kutsa kai a fagen fama.
Ngilalele ngesineke, kodwa kabatsho okulungileyo. Kakho ophenduka ebubini bakhe, esithi, “Kuyini engikwenzileyo na?” Yilowo lalowo ulandela indlela yakhe njengebhiza lizithela empini.
7 Ko shamuwa ta sararin sama ma takan san lokutan da aka tsara mata, kurciya, mashirare da kuma zalɓe sukan lura da lokacin ƙauransu. Amma mutanena ba su san abubuwan da Ubangiji yake bukata ba.
Lengabuzane emoyeni liyazazi izikhathi zalo zomnyaka, lejuba, lenkonjane lohemu kuyasigcina isikhathi sakho sokuthutha. Kodwa abantu bami kabakwazi okufunwa nguThixo.
8 “‘Yaya za ku ce, “Muna da hikima, gama muna da dokar Ubangiji,” alhali alƙalamin ƙarya na magatakarda ya yi ƙarya?
Lingatsho kanjani ukuthi, “Sihlakaniphile, ngoba silomthetho kaThixo,” lona iqiniso kuyikuthi amanga alotshwe ngosiba lwababhali asenze umthetho wangabi liqiniso?
9 Za a kunyatar da masu hikima; za su yi fargaba a kuma kama su. Da yake sun ƙi maganar Ubangiji, wace irin hikima kuka ce kuke da ita?
Abahlakaniphileyo bazayangiswa, bazakwesaba bathiyeke. Njengoba belalile ilizwi likaThixo, balenhlakanipho bani na?
10 Saboda haka zan ba da matansu ga waɗansu gonakinsu kuma ga waɗansu da suka ci da yaƙi. Tun daga ƙarami har zuwa babba, kowannensu yana haɗamar cin muguwar riba; har da annabawa da firistoci ma, kowannensu yana ƙarya.
Ngakho abafazi babo ngizabapha amanye amadoda lamasimu abo abe ngawabanye abatsha. Kusukela kwabancane kusiya kwabakhulu, bonke bayizihwaba ezifuna inzuzo, banjalo abaphrofethi kanye labaphristi, bonke benza inkohliso.
11 Sukan ɗaura mikin mutanena sai ka ce mikin ba shi da matsala. Suna cewa, “Lafiya, Lafiya,” alhali kuwa ba lafiya.
Babopha inxeba labantu bami kungathi kalilibi kakhulu. Bathi, “Ukuthula, ukuthula,” khona ukuthula kungekho.
12 Sukan ji kunyar halin banƙyamarsu kuwa? Sam, ba su da kunya ko kaɗan; ba su ma san yadda za su ji kunya ba. Saboda haka sukan fāɗi tare da fāɗaɗɗu; za su fāɗi sa’ad da aka hukunta su, in ji Ubangiji.
Kambe bayayangeka na ngokuziphatha kwabo okunengisayo? Hatshi, bavele kabalazo inhloni, lokuyangeka kabakwazi. Ngakho bazawela phakathi kwabawileyo, bazakwehliselwa phansi lapho sebejeziswa, kutsho uThixo.
13 “‘Zan ƙwace girbinsu, in ji Ubangiji. Ba a za sami inabi a kuringa ba. Ba za a sami’ya’ya a itacen ɓaure ba, ganyayensu kuwa za su bushe. Abin da na ba su za a ƙwace.’”
Ngizabemuka isivuno sabo, kutsho uThixo. Akuyikuba lezithelo ezivinini zabo. Akuyikuba lezithelo zomkhiwa esihlahleni, lamahlamvu aso azabuna. Engibanike khona kuzathathwa kubo.’”
14 Me ya sa muke zama a nan? Mu tattaru! Mu gudu zuwa birane masu katanga mu mutu a can! Gama Ubangiji Allahnmu ya ƙaddara mana mutuwa ya kuma ba mu ruwan dafi mu sha, domin mun yi masa zunubi.
Pho sihlaleleni lapha? Buthanini! Kasibalekeleni emadolobheni avikelweyo siyebhubhela khona! Ngoba uThixo uNkulunkulu wethu usesilahlele ekubhubheni wasinika amanzi aletshefu ukuba sinathe, ngoba sonile kuye.
15 Mun sa zuciya ga salama amma ba lafiya, mun sa zuciya ga lokacin warkarwa amma sai ga razana.
Sathemba ukuba lokuthula kodwa akubanga lobuhle obukhona, ekubeni kube yisikhathi sokwelatshwa kwaba lokwesaba.
16 Daga Dan ana jin tirjin dawakan abokin gāba; da jin haniniyar ingarmunsu dukan ƙasar ta girgiza. Sun zo su cinye ƙasar da kome da yake cikinta, birni da dukan mazaunanta.
Ukuthimula kwamabhiza esitha kuyezwakala kuvelela koDani, ekukhaleni kwamabhiza amaduna ilizwe lonke liyaqhaqhazela. Zilande ukuzatshwabadela ilizwe lakho konke okukulo, idolobho labo bonke abahlala kulo.
17 “Duba, zan aika macizai masu dafi a cikinku, kāsā, waɗanda ba su da maƙari, za su kuwa sassare ku,” in ji Ubangiji.
“Khangelani, ngizathumela phakathi kwenu izinyoka ezilobuhlungu, izinhlangwana ezingeke zithakathwe, njalo zizaliluma,” kutsho uThixo.
18 Ya mai ta’aziyyata a cikin baƙin ciki, zuciyata ta ɓaci ƙwarai.
Awu Mduduzi wami osizini, inhliziyo yami isiqaleka phakathi kwami.
19 Ka saurari kukan mutanena daga ƙasa mai nisa suna cewa, “Ubangiji ba ya a Sihiyona ne? Sarkinta ba ya can ne kuma?” “Me ya sa suka tsokane ni da gumakansu har na yi fushi, da baƙin gumakansu marasa amfani?”
Lalela ukukhala kwabantu bami okuvela elizweni elikhatshana besithi: “UThixo kakho eZiyoni na? INkosi yalo kayisekho lapho na?” “Kungani bevuse ulaka lwami ngezifanekiso zabo, langezithombe zezizweni eziyize na?”
20 “Girbi ya wuce, damuna ta ƙare, ba a kuwa cece mu ba.”
“Ukuvuna sekwedlule, ihlobo seliphelile, kodwa kasihlengwanga.”
21 Da yake an ragargazar da mutanena, an ragargaza ni ke nan; na yi kuka, tsoro ya kama ni.
Njengoba abantu bami benqotshiwe lami nginqotshiwe, ngiyalila njalo ukwesaba kungiphethe.
22 Ba magani ne a Gileyad? Ba likita ne a can? To, me ya sa ba warkarwa wa raunin mutanena?
Akulamuthi yini eGiliyadi? Kakho yini lomelaphi khona? Pho kungani kungekho kwelatshwa kwenxeba labantu bami na?