< Irmiya 8 >
1 “‘A wancan lokaci, in ji Ubangiji, za a fitar da ƙasusuwan sarakuna da na shugabannin Yahuda, ƙasusuwan firistoci da na annabawa, da kuma ƙasusuwan mutanen Urushalima daga kaburbura.
Tanī laikā, saka Tas Kungs, Jūda ķēniņu kaulus un viņu lielkungu kaulus un viņu priesteru kaulus un praviešu kaulus un Jeruzālemes iedzīvotāju kaulus izmetīs no viņu kapiem.
2 Za a shimfiɗa su a rana da wata da kuma dukan taurarin sammai, waɗanda suka ƙaunata suka kuma bauta wa, waɗanda suka bi suka nemi shawarar suka kuma yi wa sujada. Ba za a tattara su ko a binne su ba, amma za su zama kamar juji a jibge a ƙasa.
Un izmētās pret sauli un pret mēnesi un pret visu debess pulku, ko tie mīlējuši un kam tie kalpojuši un kam tie dzinušies pakaļ un ko tie meklējuši un ko tie pielūguši. Ne tos sakrās, ne tos apraks, tie būs par mēsliem zemes virsū.
3 Duk inda na kore su zuwa, dukan waɗanda suka ragu na wannan muguwar al’umma za su gwammaci mutuwa da rai, in ji Ubangiji Maɗaukaki.’
Un nāvi vēlēsies dzīvības vietā visi atlikušie, kas no šās niknās cilts atliks visās malās, kurp Es tos atlikušos būšu aizdzinis, saka Tas Kungs Cebaot.
4 “Fada musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Sa’ad da mutane suka fāɗi, ba sa tashi ne? Sa’ad da mutum ya kauce, ba ya dawowa?
Un saki uz tiem: tā saka Tas Kungs: kad krīt, vai atkal neceļas: kad nogriežas, vai atkal negriežas atpakaļ?
5 To, me ya sa waɗannan mutane suka kauce? Me ya sa Urushalima kullum take kaucewa? Sun manne wa ƙarya; suka ƙi su dawo.
Kāpēc tad šie Jeruzālemes ļaudis atkāpjas bez mitēšanās atkāpdamies? Tie stipri turas pie viltus un liedzās atgriezties.
6 Na saurara sosai, amma ba su faɗi wata maganar kirki ba. Ba wanda ya tuba daga muguntarsa, sai ma cewa yake, “Me na yi?” Kowa ta kai-ta-kai yake kamar dokin da ya kutsa kai a fagen fama.
Es esmu vērā ņēmis un dzirdējis: tie runā, kas nepareizi; neviena nav, kam būtu žēl savas blēdības, kas sacītu: ko esmu darījis? Visi atkāpjas, skriedami kā traks ērzelis kas karā.
7 Ko shamuwa ta sararin sama ma takan san lokutan da aka tsara mata, kurciya, mashirare da kuma zalɓe sukan lura da lokacin ƙauransu. Amma mutanena ba su san abubuwan da Ubangiji yake bukata ba.
Stārķis apakš debess zin savus laikus, un ūbele un dzērve un bezdelīga ņem vērā savu atnākšanas laiku, bet mani ļaudis neatzīst Tā Kunga tiesu.
8 “‘Yaya za ku ce, “Muna da hikima, gama muna da dokar Ubangiji,” alhali alƙalamin ƙarya na magatakarda ya yi ƙarya?
Kā tad jūs sakāt: mēs esam gudri, un Tā Kunga bauslība ir pie mums? Tiešām, redzi, rakstu mācītāju viltīgie raksti to pārvērtuši par meliem.
9 Za a kunyatar da masu hikima; za su yi fargaba a kuma kama su. Da yake sun ƙi maganar Ubangiji, wace irin hikima kuka ce kuke da ita?
Gudrie top apkaunoti, iztrūcināti un sagūstīti; redzi, Tā Kunga vārdu tie ir atmetuši, kāda gudrība tad tiem ir?
10 Saboda haka zan ba da matansu ga waɗansu gonakinsu kuma ga waɗansu da suka ci da yaƙi. Tun daga ƙarami har zuwa babba, kowannensu yana haɗamar cin muguwar riba; har da annabawa da firistoci ma, kowannensu yana ƙarya.
Tādēļ Es viņu sievas došu citiem, viņu tīrumus svešiem mantiniekiem; jo mazi un lieli, visi kāri pēc mantas; pravietis un priesteris, abi dzen viltību.
11 Sukan ɗaura mikin mutanena sai ka ce mikin ba shi da matsala. Suna cewa, “Lafiya, Lafiya,” alhali kuwa ba lafiya.
Un tie dziedina Manas tautas vainu kā par nieku un saka: miers! Miers! Kur tomēr miera nav.
12 Sukan ji kunyar halin banƙyamarsu kuwa? Sam, ba su da kunya ko kaɗan; ba su ma san yadda za su ji kunya ba. Saboda haka sukan fāɗi tare da fāɗaɗɗu; za su fāɗi sa’ad da aka hukunta su, in ji Ubangiji.
Tie ir tapuši kaunā, tāpēc ka darījuši negantību, bet tie nemaz nekaunas un kauna neprot; tādēļ tie kritīs starp tiem kritušiem, savas piemeklēšanas laikā tie gāzīsies pie zemes, saka Tas Kungs.
13 “‘Zan ƙwace girbinsu, in ji Ubangiji. Ba a za sami inabi a kuringa ba. Ba za a sami’ya’ya a itacen ɓaure ba, ganyayensu kuwa za su bushe. Abin da na ba su za a ƙwace.’”
Es tos rautin aizraušu, saka Tas Kungs, ka ķekari nepaliks pie vīna koka nedz vīģes pie vīģes koka, ir lapas nokritīs, un Es tiem dodu, kas pār tiem nāks.
14 Me ya sa muke zama a nan? Mu tattaru! Mu gudu zuwa birane masu katanga mu mutu a can! Gama Ubangiji Allahnmu ya ƙaddara mana mutuwa ya kuma ba mu ruwan dafi mu sha, domin mun yi masa zunubi.
Ko tad kavējamies? Pulcējaties un iesim stiprās pilsētās un meklēsim tur galu! Jo Tas Kungs, mūsu Dievs, mums nolicis galu un mūs dzirdinājis ar žulti, tāpēc ka esam apgrēkojušies pret To Kungu.
15 Mun sa zuciya ga salama amma ba lafiya, mun sa zuciya ga lokacin warkarwa amma sai ga razana.
Gaida mieru, bet nav labuma, dziedināšanas laiku, bet redzi, izbailes.
16 Daga Dan ana jin tirjin dawakan abokin gāba; da jin haniniyar ingarmunsu dukan ƙasar ta girgiza. Sun zo su cinye ƙasar da kome da yake cikinta, birni da dukan mazaunanta.
No Dana jau dzirdama viņa zirgu šņākšana; visa zeme dreb no viņa ērzeļu zviegšanas skaņas; tie nāk un noēd zemi ar viņas pilnumu, pilsētas un kas tur dzīvo.
17 “Duba, zan aika macizai masu dafi a cikinku, kāsā, waɗanda ba su da maƙari, za su kuwa sassare ku,” in ji Ubangiji.
Jo redzi, Es sūtu jūsu starpā čūskas un odzes, pret ko nepalīdz vārdošana, - tās jūs kodīs, saka Tas Kungs!
18 Ya mai ta’aziyyata a cikin baƙin ciki, zuciyata ta ɓaci ƙwarai.
Kas mani iepriecinās skumjās! Mana sirds man gurst.
19 Ka saurari kukan mutanena daga ƙasa mai nisa suna cewa, “Ubangiji ba ya a Sihiyona ne? Sarkinta ba ya can ne kuma?” “Me ya sa suka tsokane ni da gumakansu har na yi fushi, da baƙin gumakansu marasa amfani?”
Redzi, Manas tautas kliegšanas balss skan no tālas zemes: vai tad Tas Kungs vairs nav Ciānā? Vai viņas ķēniņš tur nav? Kāpēc tie Mani apkaitinājuši ar saviem dievekļiem, ar svešām nelietībām?
20 “Girbi ya wuce, damuna ta ƙare, ba a kuwa cece mu ba.”
Pļauja ir pagājusi, augļu laiks pagalam, bet mēs neesam atpestīti.
21 Da yake an ragargazar da mutanena, an ragargaza ni ke nan; na yi kuka, tsoro ya kama ni.
Es esmu satriekts savas tautas posta dēļ, es esmu noskumis, izbailes mani sagrābušas.
22 Ba magani ne a Gileyad? Ba likita ne a can? To, me ya sa ba warkarwa wa raunin mutanena?
Vai tad zāļu nav Gileādā? Vai tur nav ārsta? Kāpēc tad manas tautas sērga nav dziedināta?