< Irmiya 8 >

1 “‘A wancan lokaci, in ji Ubangiji, za a fitar da ƙasusuwan sarakuna da na shugabannin Yahuda, ƙasusuwan firistoci da na annabawa, da kuma ƙasusuwan mutanen Urushalima daga kaburbura.
En ce temps-là, dit l'Éternel, on jettera les os des rois de Juda, et les os de ses princes, les os des sacrificateurs, les os des prophètes et les os des habitants de Jérusalem, hors de leurs sépultures;
2 Za a shimfiɗa su a rana da wata da kuma dukan taurarin sammai, waɗanda suka ƙaunata suka kuma bauta wa, waɗanda suka bi suka nemi shawarar suka kuma yi wa sujada. Ba za a tattara su ko a binne su ba, amma za su zama kamar juji a jibge a ƙasa.
On les étendra devant le soleil, et devant la lune, et devant toute l'armée des cieux qu'ils ont aimés, qu'ils ont servis et après lesquels ils ont marché, qu'ils ont recherchés et devant lesquels ils se sont prosternés. Ils ne seront point recueillis, ni ensevelis; ils seront comme du fumier sur la face du sol.
3 Duk inda na kore su zuwa, dukan waɗanda suka ragu na wannan muguwar al’umma za su gwammaci mutuwa da rai, in ji Ubangiji Maɗaukaki.’
Et la mort sera plus désirable que la vie pour tous ceux qui seront restés de cette race mauvaise, dans tous les lieux où j'en aurai chassé les restes, dit l'Éternel des armées.
4 “Fada musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Sa’ad da mutane suka fāɗi, ba sa tashi ne? Sa’ad da mutum ya kauce, ba ya dawowa?
Tu leur diras donc: Ainsi a dit l'Éternel: Si l'on tombe, ne se relève-t-on pas? et si l'on se détourne, ne revient-on pas?
5 To, me ya sa waɗannan mutane suka kauce? Me ya sa Urushalima kullum take kaucewa? Sun manne wa ƙarya; suka ƙi su dawo.
Pourquoi donc ce peuple de Jérusalem, s'est-il égaré d'un égarement continuel? Ils persistent dans la tromperie; ils refusent de se convertir.
6 Na saurara sosai, amma ba su faɗi wata maganar kirki ba. Ba wanda ya tuba daga muguntarsa, sai ma cewa yake, “Me na yi?” Kowa ta kai-ta-kai yake kamar dokin da ya kutsa kai a fagen fama.
J'ai prêté l'oreille, j'ai écouté: ils ne parlent pas droitement. Nul ne se repent de sa méchanceté, et ne dit: Qu'ai-je fait? Tous ils retournent à leur course, comme le cheval qui se précipite au combat.
7 Ko shamuwa ta sararin sama ma takan san lokutan da aka tsara mata, kurciya, mashirare da kuma zalɓe sukan lura da lokacin ƙauransu. Amma mutanena ba su san abubuwan da Ubangiji yake bukata ba.
La cigogne même connaît dans les cieux ses saisons; la tourterelle, l'hirondelle et la grue observent le temps où elles doivent venir; mais mon peuple ne connaît pas le jugement de l'Éternel.
8 “‘Yaya za ku ce, “Muna da hikima, gama muna da dokar Ubangiji,” alhali alƙalamin ƙarya na magatakarda ya yi ƙarya?
Comment dites-vous: Nous sommes sages, et la loi de l'Éternel est avec nous? Mais voici, la plume menteuse des scribes en fait un mensonge!
9 Za a kunyatar da masu hikima; za su yi fargaba a kuma kama su. Da yake sun ƙi maganar Ubangiji, wace irin hikima kuka ce kuke da ita?
Les sages seront confus; ils seront épouvantés, et ils seront pris. Car ils ont rejeté la parole de l'Éternel, et quelle sagesse auraient-ils?
10 Saboda haka zan ba da matansu ga waɗansu gonakinsu kuma ga waɗansu da suka ci da yaƙi. Tun daga ƙarami har zuwa babba, kowannensu yana haɗamar cin muguwar riba; har da annabawa da firistoci ma, kowannensu yana ƙarya.
C'est pourquoi je donnerai leurs femmes à d'autres, et leurs champs à de nouveaux possesseurs. Car, depuis le plus petit jusqu'au plus grand, tous sont avides de gain. Depuis le prophète jusqu'au sacrificateur, tous se conduisent faussement.
11 Sukan ɗaura mikin mutanena sai ka ce mikin ba shi da matsala. Suna cewa, “Lafiya, Lafiya,” alhali kuwa ba lafiya.
Ils pansent à la légère la plaie de la fille de mon peuple, en disant: Paix, paix! et il n'y a point de paix.
12 Sukan ji kunyar halin banƙyamarsu kuwa? Sam, ba su da kunya ko kaɗan; ba su ma san yadda za su ji kunya ba. Saboda haka sukan fāɗi tare da fāɗaɗɗu; za su fāɗi sa’ad da aka hukunta su, in ji Ubangiji.
Ont-ils été confus de ce qu'ils ont commis l'abomination? Ils n'en ont même eu aucune honte, et ils ne savent ce que c'est de rougir. C'est pourquoi ils tomberont avec ceux qui tombent; au temps de leur visitation ils seront renversés, dit l'Éternel.
13 “‘Zan ƙwace girbinsu, in ji Ubangiji. Ba a za sami inabi a kuringa ba. Ba za a sami’ya’ya a itacen ɓaure ba, ganyayensu kuwa za su bushe. Abin da na ba su za a ƙwace.’”
Je les enlèverai entièrement, dit l'Éternel. Il n'y a point de grappes à la vigne; il n'y a point de figues au figuier; la feuille est flétrie; ce que je leur ai donné sera enlevé!
14 Me ya sa muke zama a nan? Mu tattaru! Mu gudu zuwa birane masu katanga mu mutu a can! Gama Ubangiji Allahnmu ya ƙaddara mana mutuwa ya kuma ba mu ruwan dafi mu sha, domin mun yi masa zunubi.
Pourquoi demeurons-nous assis? Assemblez-vous, et entrons dans les villes fortes, et nous y périrons! Car l'Éternel notre Dieu a résolu notre perte; il nous fait boire des eaux empoisonnées; parce que nous avons péché contre l'Éternel.
15 Mun sa zuciya ga salama amma ba lafiya, mun sa zuciya ga lokacin warkarwa amma sai ga razana.
On attendait la paix, mais il n'y a rien de bon; un temps de guérison, et voici la terreur!
16 Daga Dan ana jin tirjin dawakan abokin gāba; da jin haniniyar ingarmunsu dukan ƙasar ta girgiza. Sun zo su cinye ƙasar da kome da yake cikinta, birni da dukan mazaunanta.
Du côté de Dan se fait entendre le ronflement de leurs chevaux; au bruit du hennissement de leurs puissants coursiers, toute la terre tremble. Ils viennent; ils dévorent le pays et ce qu'il contient, la ville et ceux qui y habitent.
17 “Duba, zan aika macizai masu dafi a cikinku, kāsā, waɗanda ba su da maƙari, za su kuwa sassare ku,” in ji Ubangiji.
Car voici, j'envoie contre vous des serpents, des basilics, contre lesquels il n'y a point de charme; ils vous mordront, dit l'Éternel.
18 Ya mai ta’aziyyata a cikin baƙin ciki, zuciyata ta ɓaci ƙwarai.
Ah! du répit pour ma douleur! Mon cœur souffre au-dedans de moi!
19 Ka saurari kukan mutanena daga ƙasa mai nisa suna cewa, “Ubangiji ba ya a Sihiyona ne? Sarkinta ba ya can ne kuma?” “Me ya sa suka tsokane ni da gumakansu har na yi fushi, da baƙin gumakansu marasa amfani?”
Voici la voix de la fille de mon peuple, qui crie d'un pays éloigné: L'Éternel n'est-il plus dans Sion? Son roi n'est-il plus au milieu d'elle? Pourquoi m'ont-ils irrité par leurs images taillées, par les vanités de l'étranger?
20 “Girbi ya wuce, damuna ta ƙare, ba a kuwa cece mu ba.”
La moisson est passée, l'été a pris fin, et nous ne sommes pas délivrés!
21 Da yake an ragargazar da mutanena, an ragargaza ni ke nan; na yi kuka, tsoro ya kama ni.
Je suis blessé de la blessure de la fille de mon peuple; j'en suis en deuil, la désolation m'en a saisi.
22 Ba magani ne a Gileyad? Ba likita ne a can? To, me ya sa ba warkarwa wa raunin mutanena?
N'y a-t-il point de baume en Galaad? N'y a-t-il point de médecin? Pourquoi donc la plaie de la fille de mon peuple n'est-elle pas consolidée?

< Irmiya 8 >