< Irmiya 8 >
1 “‘A wancan lokaci, in ji Ubangiji, za a fitar da ƙasusuwan sarakuna da na shugabannin Yahuda, ƙasusuwan firistoci da na annabawa, da kuma ƙasusuwan mutanen Urushalima daga kaburbura.
"En ce temps-là, dit l’Eternel, on tirera de leurs tombeaux les ossements des rois de Juda, et les ossements de ses princes, et les ossements des prêtres, et les ossements des prophètes et les ossements des habitants de Jérusalem,
2 Za a shimfiɗa su a rana da wata da kuma dukan taurarin sammai, waɗanda suka ƙaunata suka kuma bauta wa, waɗanda suka bi suka nemi shawarar suka kuma yi wa sujada. Ba za a tattara su ko a binne su ba, amma za su zama kamar juji a jibge a ƙasa.
et on les étalera à la face du soleil, de la lune et de tous les astres du ciel, qu’ils avaient aimés et adorés, qu’ils avaient suivis et recherchés, et devant lesquels ils s’étaient prosternés; ils ne seront ni recueillis ni rendus à la tombe: ils serviront d’engrais à la surface du sol.
3 Duk inda na kore su zuwa, dukan waɗanda suka ragu na wannan muguwar al’umma za su gwammaci mutuwa da rai, in ji Ubangiji Maɗaukaki.’
Alors la mort paraîtra plus désirable que la vie à tous les survivants qui resteront de cette race perverse, qui resteront dans les lieux où je les reléguerai", dit l’Eternel-Cebaot.
4 “Fada musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Sa’ad da mutane suka fāɗi, ba sa tashi ne? Sa’ad da mutum ya kauce, ba ya dawowa?
Tu leur diras: "Si l’on tombe, ne doit-on pas se relever? Si l’on se détourne, ne doit-on pas revenir?
5 To, me ya sa waɗannan mutane suka kauce? Me ya sa Urushalima kullum take kaucewa? Sun manne wa ƙarya; suka ƙi su dawo.
Pourquoi ce peuple, à Jérusalem, se rend-il coupable d’une défection obstinée? Pourquoi persévèrent-ils dans la fraude, refusent-ils de s’amender?
6 Na saurara sosai, amma ba su faɗi wata maganar kirki ba. Ba wanda ya tuba daga muguntarsa, sai ma cewa yake, “Me na yi?” Kowa ta kai-ta-kai yake kamar dokin da ya kutsa kai a fagen fama.
J’Ai prêté attention et j’ai écouté: ils profèrent des mensonges, personne parmi eux ne regrette ses mauvaises actions et ne dit: "Qu’ai-je fait?" Tous ils reprennent leur course, tels qu’un cheval qui se précipite au combat.
7 Ko shamuwa ta sararin sama ma takan san lokutan da aka tsara mata, kurciya, mashirare da kuma zalɓe sukan lura da lokacin ƙauransu. Amma mutanena ba su san abubuwan da Ubangiji yake bukata ba.
Même la cigogne dans les airs connaît les saisons qui lui sont propres; la tourterelle, l’hirondelle et la grue observent l’époque de leurs migrations, mais mon peuple ne connaît point la loi de l’Eternel!
8 “‘Yaya za ku ce, “Muna da hikima, gama muna da dokar Ubangiji,” alhali alƙalamin ƙarya na magatakarda ya yi ƙarya?
Comment pouvez-vous dire: "Nous sommes des sages! Nous sommes en possession de la doctrine de l’Eternel!" Oui, mais le stylet mensonger des scribes en a fait un mensonge!
9 Za a kunyatar da masu hikima; za su yi fargaba a kuma kama su. Da yake sun ƙi maganar Ubangiji, wace irin hikima kuka ce kuke da ita?
Ils seront couverts de confusion, ces sages. Ils seront pris de terreur, ils seront capturés; aussi bien, ils ont traité avec dédain la parole de l’Eternel: en quoi consiste donc leur sagesse?
10 Saboda haka zan ba da matansu ga waɗansu gonakinsu kuma ga waɗansu da suka ci da yaƙi. Tun daga ƙarami har zuwa babba, kowannensu yana haɗamar cin muguwar riba; har da annabawa da firistoci ma, kowannensu yana ƙarya.
C’Est pourquoi je livrerai leurs femmes à d’autres, leurs champs à des conquérants; car, du plus petit au plus grand, tous sont âpres au gain; du prophète jusqu’au prêtre, tous pratiquent le mensonge.
11 Sukan ɗaura mikin mutanena sai ka ce mikin ba shi da matsala. Suna cewa, “Lafiya, Lafiya,” alhali kuwa ba lafiya.
Ils ont bien vite fait de remédier à la ruina de mon peuple en disant: "Paix! Paix!" et il n’y a point de paix.
12 Sukan ji kunyar halin banƙyamarsu kuwa? Sam, ba su da kunya ko kaɗan; ba su ma san yadda za su ji kunya ba. Saboda haka sukan fāɗi tare da fāɗaɗɗu; za su fāɗi sa’ad da aka hukunta su, in ji Ubangiji.
Ils devraient avoir honte de commettre des abominations; mais ils n’ont aucune pudeur ni ne savent rougir; aussi succomberont-ils avec ceux qui succombent; à l’heure où j’aurai à les châtier, ils trébucheront", dit l’Eternel.
13 “‘Zan ƙwace girbinsu, in ji Ubangiji. Ba a za sami inabi a kuringa ba. Ba za a sami’ya’ya a itacen ɓaure ba, ganyayensu kuwa za su bushe. Abin da na ba su za a ƙwace.’”
"Je suis décidé à en finir avec eux", dit l’Eternel. Il n’y a plus de raisins au vignoble, ni de figues au figuier, les feuilles sont flétries: ce que je leur avais donné passera en d’autres mains.
14 Me ya sa muke zama a nan? Mu tattaru! Mu gudu zuwa birane masu katanga mu mutu a can! Gama Ubangiji Allahnmu ya ƙaddara mana mutuwa ya kuma ba mu ruwan dafi mu sha, domin mun yi masa zunubi.
Pourquoi demeurons-nous sur place? Rassemblez-vous! Retirons-nous dans les villes fortes et demeurons-y immobiles, car l’Eternel, notre Dieu, nous a condamnés à périr et abreuvés d’eaux empoisonnées, parce que nous avons péché contre l’Eternel.
15 Mun sa zuciya ga salama amma ba lafiya, mun sa zuciya ga lokacin warkarwa amma sai ga razana.
On espérait la paix, et rien d’heureux n’arrive; une ère de réparation, et voici l’épouvante!
16 Daga Dan ana jin tirjin dawakan abokin gāba; da jin haniniyar ingarmunsu dukan ƙasar ta girgiza. Sun zo su cinye ƙasar da kome da yake cikinta, birni da dukan mazaunanta.
Depuis Dan on entend le souffle de ses chevaux, le bruyant hennissement de ses puissants coursiers fait trembler la terre: ils viennent et dévorent le pays avec ce qu’il renferme, la ville et ses habitants.
17 “Duba, zan aika macizai masu dafi a cikinku, kāsā, waɗanda ba su da maƙari, za su kuwa sassare ku,” in ji Ubangiji.
Car je vais lâcher contre vous des serpents, des basilics qui défient toute incantation; ils vous déchireront de leurs morsures, dit l’Eternel.
18 Ya mai ta’aziyyata a cikin baƙin ciki, zuciyata ta ɓaci ƙwarai.
Comme je voudrais dominer ma douleur! Mon coeur souffre au dedans de moi.
19 Ka saurari kukan mutanena daga ƙasa mai nisa suna cewa, “Ubangiji ba ya a Sihiyona ne? Sarkinta ba ya can ne kuma?” “Me ya sa suka tsokane ni da gumakansu har na yi fushi, da baƙin gumakansu marasa amfani?”
Voici, j’entends la voix suppliante de la fille de mon peuple venant d’un pays lointain: "L’Eternel n’est-il plus à Sion? Son roi n’y est-il plus? Pourquoi aussi m’ont-ils contrarié par leurs idoles, les vaines divinités de l’étranger?"
20 “Girbi ya wuce, damuna ta ƙare, ba a kuwa cece mu ba.”
La moisson est achevée, la récolte touche à sa fin et nous n’avons pas reçu de secours!
21 Da yake an ragargazar da mutanena, an ragargaza ni ke nan; na yi kuka, tsoro ya kama ni.
A cause de la catastrophe qui a brisé la fille de mon peuple, je suis brisé; je suis voilé de deuil, en proie au désespoir.
22 Ba magani ne a Gileyad? Ba likita ne a can? To, me ya sa ba warkarwa wa raunin mutanena?
N’Y a-t-il plus de baume à Galaad? Ne s’y trouve-t-il plus de médecin? Pourquoi ne s’offre-t-il aucun remède pour la fille de mon peuple?