< Irmiya 8 >

1 “‘A wancan lokaci, in ji Ubangiji, za a fitar da ƙasusuwan sarakuna da na shugabannin Yahuda, ƙasusuwan firistoci da na annabawa, da kuma ƙasusuwan mutanen Urushalima daga kaburbura.
Yahweh says, “At the time [that your corpses are scattered on the ground], [your enemies will] break open the graves of your kings and [other] officials who lived in Judah, and the graves of your priests and prophets and other people who lived there.
2 Za a shimfiɗa su a rana da wata da kuma dukan taurarin sammai, waɗanda suka ƙaunata suka kuma bauta wa, waɗanda suka bi suka nemi shawarar suka kuma yi wa sujada. Ba za a tattara su ko a binne su ba, amma za su zama kamar juji a jibge a ƙasa.
They will take out their bones [from their graves] and [dishonor them by] scattering them on the ground under the sun and the moon and the stars— those are the gods which my people loved and served and worshiped. No one will gather up their bones and bury them [again]; they will remain scattered on the ground like dung.
3 Duk inda na kore su zuwa, dukan waɗanda suka ragu na wannan muguwar al’umma za su gwammaci mutuwa da rai, in ji Ubangiji Maɗaukaki.’
And all the people of this wicked nation [who are still alive and] whom I have exiled to other countries will say, ‘We would prefer to die than to continue to stay alive [here in these countries].’ [That will be true because I], Yahweh, have said it.”
4 “Fada musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Sa’ad da mutane suka fāɗi, ba sa tashi ne? Sa’ad da mutum ya kauce, ba ya dawowa?
[Yahweh said to me, “Jeremiah], tell the people that this is what [I], Yahweh, am saying to them: ‘When people fall down, they get up again, do they not [RHQ]? When people are going along a road and find out that they are walking on the wrong road, they go back [and find the correct road], do they not [RHQ]?
5 To, me ya sa waɗannan mutane suka kauce? Me ya sa Urushalima kullum take kaucewa? Sun manne wa ƙarya; suka ƙi su dawo.
[Yes, they do], so why do these people [of Judah] continue [trusting in those idols that have deceived them]? They continue turning away from me, [even though I have warned them].
6 Na saurara sosai, amma ba su faɗi wata maganar kirki ba. Ba wanda ya tuba daga muguntarsa, sai ma cewa yake, “Me na yi?” Kowa ta kai-ta-kai yake kamar dokin da ya kutsa kai a fagen fama.
I have listened carefully [DOU] [to what they say], but they do not say what they should say. Not one of them is sorry for having sinned. No one says, “I have done [RHQ] wicked things.” They are [sinning and] doing what they want to as fast as [SIM] a horse that is running into a battle.
7 Ko shamuwa ta sararin sama ma takan san lokutan da aka tsara mata, kurciya, mashirare da kuma zalɓe sukan lura da lokacin ƙauransu. Amma mutanena ba su san abubuwan da Ubangiji yake bukata ba.
All the birds [that fly south for the (winter/cold season)] know the time that they need to fly south, and they all return at the right time the following year. But my people [are not like those birds]! They do not know what [I], Yahweh, require them to do.
8 “‘Yaya za ku ce, “Muna da hikima, gama muna da dokar Ubangiji,” alhali alƙalamin ƙarya na magatakarda ya yi ƙarya?
Your men who teach you [the laws that Moses wrote] have been saying false things [about those laws]. [So], why [RHQ] do they [continue] saying, “We are [very] wise [because] we have the laws of Yahweh”?
9 Za a kunyatar da masu hikima; za su yi fargaba a kuma kama su. Da yake sun ƙi maganar Ubangiji, wace irin hikima kuka ce kuke da ita?
Those teachers, who think that [IRO] they are wise, will be ashamed/disgraced and dismayed when they are taken [to other countries by their enemies] because they sinned by rejecting what I told them. Truly, they were not [RHQ] very wise to do that!
10 Saboda haka zan ba da matansu ga waɗansu gonakinsu kuma ga waɗansu da suka ci da yaƙi. Tun daga ƙarami har zuwa babba, kowannensu yana haɗamar cin muguwar riba; har da annabawa da firistoci ma, kowannensu yana ƙarya.
So, I will give their wives to other men; I will give their fields to [the enemy soldiers] who conquer them. All the people, including those who are important and those who are not important, deceive [others] in order to obtain their possessions. Even [my] prophets and my priests do that.
11 Sukan ɗaura mikin mutanena sai ka ce mikin ba shi da matsala. Suna cewa, “Lafiya, Lafiya,” alhali kuwa ba lafiya.
[They act as though the sins of my people] are not serious, [like] [MET] wounds that do not need to be cleaned and bandaged. They tell the people that everything will go well with them, [but that is not true]; things will not go well with them.
12 Sukan ji kunyar halin banƙyamarsu kuwa? Sam, ba su da kunya ko kaɗan; ba su ma san yadda za su ji kunya ba. Saboda haka sukan fāɗi tare da fāɗaɗɗu; za su fāɗi sa’ad da aka hukunta su, in ji Ubangiji.
They should be [RHQ] ashamed when they do disgusting things [RHQ], but they do not even know how to show on their faces that they are ashamed [about their sins]. So, [they will be killed, and] their corpses [also] will lie among the corpses of others who have been slaughtered [by their enemies]. They will be killed when I punish them.
13 “‘Zan ƙwace girbinsu, in ji Ubangiji. Ba a za sami inabi a kuringa ba. Ba za a sami’ya’ya a itacen ɓaure ba, ganyayensu kuwa za su bushe. Abin da na ba su za a ƙwace.’”
I will [allow their enemies to] take away the figs and grapes that the people would have harvested from their fields. Their fruit trees will all wither. They will not receive [all] the blessings that I prepared for them. [This will certainly happen because I], Yahweh, have said it.’”
14 Me ya sa muke zama a nan? Mu tattaru! Mu gudu zuwa birane masu katanga mu mutu a can! Gama Ubangiji Allahnmu ya ƙaddara mana mutuwa ya kuma ba mu ruwan dafi mu sha, domin mun yi masa zunubi.
[Then the people will say], “(Why should we wait here [in these small towns]?/We should not wait here [in these small towns].) [RHQ]! We should go to the cities that have high walls around them, [but even if we do that] we will be killed there, because Yahweh our God has decided that we must be destroyed; [it is as though] [MET] he has given us a cup of poison to drink, because we sinned against him.
15 Mun sa zuciya ga salama amma ba lafiya, mun sa zuciya ga lokacin warkarwa amma sai ga razana.
We hoped/desired that things would go well for us, but things have not gone well. We hoped that bad things would not happen to us any more, but only things that terrify us [are happening to us].
16 Daga Dan ana jin tirjin dawakan abokin gāba; da jin haniniyar ingarmunsu dukan ƙasar ta girgiza. Sun zo su cinye ƙasar da kome da yake cikinta, birni da dukan mazaunanta.
People [far north in Israel] in [the city of] Dan can already hear the snorting of the horses of their enemies [who are preparing to attack us]. [It is as though] the entire land [of Judah] is shaking as their army approaches; they are coming to destroy our land and everything in it, the people and the cities.”
17 “Duba, zan aika macizai masu dafi a cikinku, kāsā, waɗanda ba su da maƙari, za su kuwa sassare ku,” in ji Ubangiji.
[Yahweh says], “I will send [those enemy soldiers to Judah], and they will be like [MET] poisonous snakes among you. No one will be able to stop them from attacking you [MET]; they will attack you like snakes do, [and kill you].”
18 Ya mai ta’aziyyata a cikin baƙin ciki, zuciyata ta ɓaci ƙwarai.
I grieve very much [for the people of Judah], and my grieving does not end. I am very sad [IDM].
19 Ka saurari kukan mutanena daga ƙasa mai nisa suna cewa, “Ubangiji ba ya a Sihiyona ne? Sarkinta ba ya can ne kuma?” “Me ya sa suka tsokane ni da gumakansu har na yi fushi, da baƙin gumakansu marasa amfani?”
Throughout our land, the people ask, “Has Yahweh abandoned Jerusalem? Is [he], our city’s king, no longer there?” [Yahweh replies], “Why do the people cause me to become very angry by [worshiping] idols and foreign gods?” [RHQ]
20 “Girbi ya wuce, damuna ta ƙare, ba a kuwa cece mu ba.”
[The people say], “The harvest [season] is finished, the (summer/hot season) has ended, [and we hoped that we would receive blessings from Yahweh], but he has not rescued us [from our enemies].”
21 Da yake an ragargazar da mutanena, an ragargaza ni ke nan; na yi kuka, tsoro ya kama ni.
I cry because my people have been crushed. I mourn, and I am completely dismayed.
22 Ba magani ne a Gileyad? Ba likita ne a can? To, me ya sa ba warkarwa wa raunin mutanena?
[I ask], “Surely there is [RHQ] medicinal balm in the Gilead [region]! Surely there are [RHQ] doctors there!” But my people have been badly wounded [in their spirits], and nothing can heal them.

< Irmiya 8 >