< Irmiya 8 >

1 “‘A wancan lokaci, in ji Ubangiji, za a fitar da ƙasusuwan sarakuna da na shugabannin Yahuda, ƙasusuwan firistoci da na annabawa, da kuma ƙasusuwan mutanen Urushalima daga kaburbura.
At that time, says Jehovah, they shall bring out the bones of the kings of Judah, and the bones of his rulers, and the bones of the priests, and the bones of the prophets, and the bones of the inhabitants of Jerusalem, out of their graves.
2 Za a shimfiɗa su a rana da wata da kuma dukan taurarin sammai, waɗanda suka ƙaunata suka kuma bauta wa, waɗanda suka bi suka nemi shawarar suka kuma yi wa sujada. Ba za a tattara su ko a binne su ba, amma za su zama kamar juji a jibge a ƙasa.
And they shall spread them before the sun, and the moon, and all the host of heaven, which they have loved, and which they have served, and after which they have walked, and which they have sought, and which they have worshiped. They shall not be gathered, nor be buried. They shall be for dung upon the face of the earth.
3 Duk inda na kore su zuwa, dukan waɗanda suka ragu na wannan muguwar al’umma za su gwammaci mutuwa da rai, in ji Ubangiji Maɗaukaki.’
And death shall be chosen rather than life by all the residue that remain of this evil family, that remain in all the places where I have driven them, says Jehovah of hosts.
4 “Fada musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Sa’ad da mutane suka fāɗi, ba sa tashi ne? Sa’ad da mutum ya kauce, ba ya dawowa?
Moreover thou shall say to them, Thus says Jehovah: Shall men fall, and not rise up again? Shall he turn away, and not return?
5 To, me ya sa waɗannan mutane suka kauce? Me ya sa Urushalima kullum take kaucewa? Sun manne wa ƙarya; suka ƙi su dawo.
Why then has this people of Jerusalem slid back by a perpetual backsliding? They hold firm deceit. They refuse to return.
6 Na saurara sosai, amma ba su faɗi wata maganar kirki ba. Ba wanda ya tuba daga muguntarsa, sai ma cewa yake, “Me na yi?” Kowa ta kai-ta-kai yake kamar dokin da ya kutsa kai a fagen fama.
I hearkened and heard, but they did not speak aright. No man repents of his wickedness, saying, What have I done? Everyone turns to his course as a horse that rushes headlong in the battle.
7 Ko shamuwa ta sararin sama ma takan san lokutan da aka tsara mata, kurciya, mashirare da kuma zalɓe sukan lura da lokacin ƙauransu. Amma mutanena ba su san abubuwan da Ubangiji yake bukata ba.
Yea, the stork in the heavens knows her appointed times, and the turtledove and the swallow and the crane observe the time of their coming, but my people know not the law of Jehovah.
8 “‘Yaya za ku ce, “Muna da hikima, gama muna da dokar Ubangiji,” alhali alƙalamin ƙarya na magatakarda ya yi ƙarya?
How can ye say, We are wise, and the law of Jehovah is with us? But behold, the false pen of the scribes has wrought falsely.
9 Za a kunyatar da masu hikima; za su yi fargaba a kuma kama su. Da yake sun ƙi maganar Ubangiji, wace irin hikima kuka ce kuke da ita?
The wise men are put to shame. They are dismayed and taken. Lo, they have rejected the word of Jehovah, and what manner of wisdom is in them?
10 Saboda haka zan ba da matansu ga waɗansu gonakinsu kuma ga waɗansu da suka ci da yaƙi. Tun daga ƙarami har zuwa babba, kowannensu yana haɗamar cin muguwar riba; har da annabawa da firistoci ma, kowannensu yana ƙarya.
Therefore I will give their wives to others, and their fields to those who shall possess them. For everyone from the least even to the greatest is given to covetousness. From the prophet even to the priest everyone deals falsely.
11 Sukan ɗaura mikin mutanena sai ka ce mikin ba shi da matsala. Suna cewa, “Lafiya, Lafiya,” alhali kuwa ba lafiya.
And they have lightly healed the hurt of the daughter of my people, saying, Peace, peace, when there is no peace.
12 Sukan ji kunyar halin banƙyamarsu kuwa? Sam, ba su da kunya ko kaɗan; ba su ma san yadda za su ji kunya ba. Saboda haka sukan fāɗi tare da fāɗaɗɗu; za su fāɗi sa’ad da aka hukunta su, in ji Ubangiji.
Were they ashamed when they had committed abomination? No, they were not at all ashamed, nor could they blush. Therefore they shall fall among those who fall. In the time of their visitation they shall be cast down, says Jehovah.
13 “‘Zan ƙwace girbinsu, in ji Ubangiji. Ba a za sami inabi a kuringa ba. Ba za a sami’ya’ya a itacen ɓaure ba, ganyayensu kuwa za su bushe. Abin da na ba su za a ƙwace.’”
I will utterly consume them, says Jehovah. There shall be no grapes on the vine, nor figs on the fig tree, and the leaf shall fade, and things I have given them shall pass away from them.
14 Me ya sa muke zama a nan? Mu tattaru! Mu gudu zuwa birane masu katanga mu mutu a can! Gama Ubangiji Allahnmu ya ƙaddara mana mutuwa ya kuma ba mu ruwan dafi mu sha, domin mun yi masa zunubi.
Why do we sit still? Assemble yourselves, and let us enter into the fortified cities, and let us be silent there. For Jehovah our God has put us to silence, and given us water of gall to drink, because we have sinned against Jehovah.
15 Mun sa zuciya ga salama amma ba lafiya, mun sa zuciya ga lokacin warkarwa amma sai ga razana.
We looked for peace, but no good came, for a time of healing, and, behold, dismay!
16 Daga Dan ana jin tirjin dawakan abokin gāba; da jin haniniyar ingarmunsu dukan ƙasar ta girgiza. Sun zo su cinye ƙasar da kome da yake cikinta, birni da dukan mazaunanta.
The snorting of his horses is heard from Dan. At the sound of the neighing of his strong ones the whole land trembles. For they have come, and have devoured the land and all that is in it, the city and those who dwell therein.
17 “Duba, zan aika macizai masu dafi a cikinku, kāsā, waɗanda ba su da maƙari, za su kuwa sassare ku,” in ji Ubangiji.
For, behold, I will send serpents, adders, among you, which will not be charmed, and they shall bite you, says Jehovah.
18 Ya mai ta’aziyyata a cikin baƙin ciki, zuciyata ta ɓaci ƙwarai.
Oh that I could comfort myself against sorrow! My heart is faint within me.
19 Ka saurari kukan mutanena daga ƙasa mai nisa suna cewa, “Ubangiji ba ya a Sihiyona ne? Sarkinta ba ya can ne kuma?” “Me ya sa suka tsokane ni da gumakansu har na yi fushi, da baƙin gumakansu marasa amfani?”
Behold, the voice of the cry of the daughter of my people from a land that is very far off: Is not Jehovah in Zion? Is not her King in her? Why have they provoked me to anger with their graven images, and with foreign vanities?
20 “Girbi ya wuce, damuna ta ƙare, ba a kuwa cece mu ba.”
The harvest is past, the summer is ended, and we are not saved.
21 Da yake an ragargazar da mutanena, an ragargaza ni ke nan; na yi kuka, tsoro ya kama ni.
For the hurt of the daughter of my people I am hurt. I mourn. Dismay has taken hold on me.
22 Ba magani ne a Gileyad? Ba likita ne a can? To, me ya sa ba warkarwa wa raunin mutanena?
Is there no balm in Gilead? Is there no physician there? Why then has not the health of the daughter of my people recovered?

< Irmiya 8 >