< Irmiya 7 >

1 Maganar da ta zo wa Irmiya ke nan daga Ubangiji.
Beseda, ki je prišla Jeremiju od Gospoda, rekoč:
2 “Ka tsaya a ƙofar gidan Ubangiji, a can kuwa ka yi shelar wannan saƙo. “‘Ku ji maganar Ubangiji, dukanku mutanen Yahuda waɗanda suke shiga ta waɗannan ƙofofi don yin sujada ga Ubangiji.
»Stopi v velika vrata Gospodove hiše in razglasi to besedo in reci: ›Poslušajte Gospodovo besedo, vsi vi iz Juda, ki vstopate pri teh velikih vratih, da obožujete Gospoda.
3 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allahna Isra’ila, yana cewa ku gyara hanyoyinku da ayyukanku, zan kuwa bar ku ku zauna a wannan wuri.
Tako govori Gospod nad bojevniki, Izraelov Bog: ›Poboljšajte svoje poti in svoja dejanja in jaz vam bom povzročil, da prebivate na tem kraju.
4 Kada ku dogara ga maganganun nan na ruɗarwa cewa, “Wannan shi ne haikalin Ubangiji, haikalin Ubangiji, haikalin Ubangiji!”
Ne zaupajte v lažnive besede, rekoč: › Gospodov tempelj, ‹ › Gospodov tempelj, ‹ › Gospodov tempelj so ti.‹
5 In dai kuka canja hanyoyinku da ayyukanku kuma kuna aikata adalci da junanku,
Kajti če temeljito poboljšate svoje poti in svoja dejanja, če temeljito izvršite sodbo med človekom in njegovim sosedom,
6 in ba ku zalunci baƙo, maraya ko gwauruwa ba kuma in ba ku zub da jinin marar laifi a wannan wuri ba, in kuma ba ku bi waɗansu alloli da za su cuce ku ba,
če ne zatirate tujca, sirote, vdove, in na tem kraju ne prelivate nedolžne krvi niti v svojo škodo ne hodite za drugimi bogovi,
7 to, zan bar ku ku zauna a wannan wuri, a ƙasar da na ba kakanninku har abada abadin.
potem vam bom povzročil, da prebivate na tem kraju, v deželi, ki sem jo dal vašim očetom na veke vekov.
8 Amma ga shi, kuna dogara ga maganganu na ruɗami marasa amfani.
Glejte, zaupate v lažnive besede, ki ne morejo koristiti.
9 “‘Za ku yi sata da kisa, ku yi zina da rantsuwar ƙarya, kuna ƙone turare wa Ba’al kuna kuma bin waɗansu allolin da ba ku sani ba,
Ali boste kradli, morili, počeli zakonolomstvo, krivo prisegali, zažigali kadilo Báalu in hodili za drugimi bogovi, ki jih ne poznate
10 sa’an nan ku zo ku tsaya a gabana a wannan gida, wanda ake kira da Sunana, kuna cewa, “An cece mu,” mun dace mu aikata waɗannan abubuwa banƙyama?
in prišli ter stali pred menoj v tej hiši, ki je imenovana z mojim imenom in rekli: »Rešeni smo, da bi počeli vse te ogabnosti?
11 Wannan gidan da ake kira da Sunana ya zama kogon’yan fashi ne a gare ku? Amma ina kallo! In ji Ubangiji.
Ali je ta hiša, ki je imenovana z mojim imenom, v vaših očeh postala brlog roparjev? Glejte, celo jaz sem to videl, « govori Gospod.
12 “‘Yanzu ku fita zuwa Shilo inda na fara maishe shi wurin zama don Sunana, ku ga abin da na yi masa saboda muguntar mutanen Isra’ila.
»Toda pojdite sedaj k mojemu kraju, ki je bil v Šilu, kjer sem najprej postavil svoje ime in poglejte, kaj sem mu storil zaradi zlobnosti svojega ljudstva Izraela.
13 Yayinda kuke yin dukan waɗannan abubuwa, in ji Ubangiji, na yi muku magana sau da sau, amma ba ku ji ba; na kira ku, amma ba ku amsa ba.
In sedaj, ker ste storili vsa ta dejanja, « govori Gospod »in sem vam govoril, vas zgodaj vzdigoval in govoril, toda niste slišali; in vas klical, toda niste odgovorili;
14 Saboda haka, abin da na yi wa Shilo shi ne yanzu zan yi wa gidan da ake kira da Sunana, haikalin da kuka dogara a kai, wurin da na ba ku da kuma kakanninku.
zato bom tej hiši, ki je imenovana z mojim imenom, v katerega zaupate in kraju, ki sem ga dal vam in vašim očetom, storil kakor sem storil Šilu.
15 Zan kore ku daga gabana, kamar yadda na yi ga dukan’yan’uwanku, mutanen Efraim.’
Zavrgel vas bom iz svojega pogleda, kakor sem zavrgel vse vaše brate, celó celotno Efrájimovo seme.
16 “Saboda haka kada ka yi addu’a don wannan mutane ko ka yi wani kuka ko roƙo dominsu, gama ba zan ji ka ba.
Zato ne moli za to ljudstvo, niti ne povzdiguj klica, niti molitve zanje, niti ne posreduj k meni, kajti jaz te ne bom poslušal.
17 Ba ka gani abin da suke yi a biranen Yahuda da kuma a titunan Urushalima?
Mar ne vidiš, kaj počno v Judovih mestih in na ulicah [prestolnice] Jeruzalem?
18 Yara sukan tara itace, iyaye suka hura wuta, mata kuma sukan kwaɓa kullu don su yi wa Sarauniyar Sama waina. Sukan miƙa hadayun sha ga waɗansu alloli don su tsokane ni in yi fushi.
Otroci nabirajo les, očetje netijo ogenj in ženske gnetejo svoje testo, da naredijo kolače kraljici neba in da izlivajo pitne daritve k drugim bogovom, da bi me lahko dražili k jezi.
19 Amma ni ne suke tsokana? In ji Ubangiji Ashe, ba kansu ne suke cuta, suna kunyata kansu ba?
Mar me dražijo do jeze?« govori Gospod: » Mar ne dražijo sami sebe, do zmešnjave njihovih lastnih obrazov?«
20 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa fushina da hasalata za su kwarara a wannan wuri, a kan mutum da dabba, a kan itatuwan fili da a kan amfanin gona, za su yi ta kuna, ba kuwa za a kashe ba.
Zato tako govori Gospod Bog: »Glej, moja jeza in moja razjarjenost bo izlita na tem kraju, na človeka, na žival, na drevesa polja in na sad tal; ta bo gorela in ne bo pogašena.«
21 “‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa ci gaba, ku ƙara hadayun ƙonawarku da sauran sadakoki ku kuma yi ta cin naman!
Tako govori Gospod nad bojevniki, Izraelov Bog: »Položite svoje žgalne daritve k svojim klavnim daritvam in jejte meso.
22 Gama sa’ad da na fitar da kakanninku daga Masar na kuma yi musu magana, ban ba su dokoki kawai game da hadayun ƙonawa da sadakoki ba,
Kajti nisem govoril vašim očetom niti jim nisem zapovedal na dan, ko sem jih privedel iz egiptovske dežele, glede žgalnih daritev ali klavnih daritev,
23 amma na ba su wannan umarni cewa ku yi mini biyayya, zan kuwa zama Allahnku ku kuma ku zama mutanena. Ku yi tafiya cikin dukan hanyoyin da na umarce ku, don ku zauna lafiya.
toda ukazal sem jim to stvar, rekoč: ›Ubogajte moj glas in jaz bom vaš Bog in vi boste moje ljudstvo; hodite po vseh poteh, ki sem vam jih zapovedal, da vam bo lahko dobro.‹
24 Amma ba su saurara ba, ba su kuwa kula ba; a maimako, suka bi shawarar kansu da ta taurare muguwar zukatansu. Su ja da baya a maimakon yin gaba.
Toda niso prisluhnili niti nagnili svojega ušesa, temveč so hodili po nasvetih in po zamislih svojega zlega srca in odšli nazaj in ne naprej.
25 Daga lokacin da kakanninku suka bar Masar har yă zuwa yau, kullum na yi ta aikan bayina annabawa.
Od dneva, ko so vaši očetje izšli iz egiptovske dežele, do tega dne, sem vam celo pošiljal vse svoje služabnike preroke, dnevno sem jih zgodaj vzdigoval in pošiljal.
26 Amma ba su saurare ni ba, ba su kula ba. Sai suka taurare zukatansu suka aikata mugun abu fiye da na kakanninsu.’
Vendar mi niso prisluhnili niti nagnili svojega ušesa, temveč so otrdili svoj vrat. Ravnali so huje kakor njihovi očetje.
27 “Sa’ad da ka faɗa musu wannan duka, ba za su saurare ka ba; sa’ad da ka kira su, ba za su amsa ba.
Zato jim boš govoril vse te besede, toda ne bodo ti prisluhnili. Tudi klical boš k njim, toda ne bodo ti odgovorili.
28 Saboda haka ka faɗa musu cewa, ‘Wannan ce al’ummar da ba tă yi biyayya ga Ubangiji Allahnta ba, ba kuwa ta karɓi gyara ba. Gaskiya ta ƙare; ta ɓace gaba ɗaya daga leɓunansu.
Toda rekel jim boš: ›To je narod, ki ne uboga glasu Gospoda, svojega Boga niti ne prejema grajanja. Resnica je izginila in je iztrebljena iz njihovih ust.‹«
29 “‘Ku aske gashin kanku ku zubar; ku yi makoki a filayen tuddai, gama Ubangiji ya ƙi’yan zamanin nan ya kuma rabu da su saboda fushin da suka ba shi.
Ostriži svoje lase, oh [prestolnica] Jeruzalem in jih odvrzi proč in povzemi žalostinko na visokih krajih, kajti Gospod je zavrnil in zapustil rod svojega besa.
30 “‘Mutanen Yahuda sun yi mugunta a gabana, in ji Ubangiji. Sun kafa gumakansu masu banƙyama a gidan da ake kira da Sunana suka ƙazantar da shi.
Kajti Judovi otroci so storili zlo v mojem pogledu, « govori Gospod. »Svoje ogabnosti so postavili v hiši, ki se imenuje z mojim imenom, da jo oskrunijo.
31 Sun gida masujadan Tofet a Kwarin Ben Hinnom don miƙa’ya’yansu maza da mata a wuta, abin da ban yi umarni ba, ba kuwa yi tunaninsa ba.
Zgradili so visoke kraje Tofeta, ki je v dolini sina Hinómovega, da svoje sinove in svoje hčere sežigajo v ognju, kar jim nisem zapovedal niti ni prišlo v moje srce.
32 Saboda haka ku yi hankali, kwanaki suna zuwa in ji Ubangiji, sa’ad da mutane ba za su ƙara kira wurin Tofet ko Kwarin Ben Hinnom ba, amma Kwarin Kisa, gama za su binne matattu a Tofet sai har ba sauran wuri.
Zato, glej, prihajajo dnevi, « govori Gospod, »da ta ne bo več imenovan Tofet niti dolina sina Hinómovega, temveč dolina klanja, kajti v Tofetu bodo pokopavali, dokler tam ne bo več prostora.
33 Sa’an nan gawawwakin wannan mutane za su zama abinci ga tsuntsayen sama da kuma namun jeji, ba za a kuwa sami wani da zai kore su ba.
Trupla tega ljudstva bodo meso za perjad neba in zemeljske zveri in nihče jih ne bo podil proč.
34 Zan kawo ƙarshen muryar murna da farin ciki da muryar amarya da ango a garuruwan Yahuda da kuma a titunan Urushalima, gama ƙasar za tă zama kufai.
Potem bom povzročil, da od Judovih mest in od ulic [prestolnice] Jeruzalem preneha glas smeha, glas veselja, glas ženina in glas neveste, kajti dežela bo zapuščena.

< Irmiya 7 >