< Irmiya 7 >

1 Maganar da ta zo wa Irmiya ke nan daga Ubangiji.
A palavra que veio de Javé a Jeremias, dizendo:
2 “Ka tsaya a ƙofar gidan Ubangiji, a can kuwa ka yi shelar wannan saƙo. “‘Ku ji maganar Ubangiji, dukanku mutanen Yahuda waɗanda suke shiga ta waɗannan ƙofofi don yin sujada ga Ubangiji.
“Fiquem no portão da casa de Javé, e proclamem esta palavra lá, e digam: 'Ouçam a palavra de Javé, todos vocês de Judá, que entram por estes portões para adorar a Javé'”.
3 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allahna Isra’ila, yana cewa ku gyara hanyoyinku da ayyukanku, zan kuwa bar ku ku zauna a wannan wuri.
Yahweh dos Exércitos, o Deus de Israel diz: “Altere seus caminhos e seus feitos, e eu farei com que você habite neste lugar”.
4 Kada ku dogara ga maganganun nan na ruɗarwa cewa, “Wannan shi ne haikalin Ubangiji, haikalin Ubangiji, haikalin Ubangiji!”
Não confie em palavras mentirosas, dizendo: 'templo de Javé, templo de Javé, templo de Javé, são estes'.
5 In dai kuka canja hanyoyinku da ayyukanku kuma kuna aikata adalci da junanku,
Pois se você emendar completamente seus caminhos e seus atos, se você executar completamente a justiça entre um homem e seu próximo;
6 in ba ku zalunci baƙo, maraya ko gwauruwa ba kuma in ba ku zub da jinin marar laifi a wannan wuri ba, in kuma ba ku bi waɗansu alloli da za su cuce ku ba,
if você não oprime o estrangeiro, o órfão de pai e a viúva, e não derrama sangue inocente neste lugar, e não caminha atrás de outros deuses para seu próprio mal,
7 to, zan bar ku ku zauna a wannan wuri, a ƙasar da na ba kakanninku har abada abadin.
então eu farei com que você habite neste lugar, na terra que eu dei a seus pais, de outrora até mais para sempre.
8 Amma ga shi, kuna dogara ga maganganu na ruɗami marasa amfani.
Eis que você confia em palavras mentirosas que não podem lucrar.
9 “‘Za ku yi sata da kisa, ku yi zina da rantsuwar ƙarya, kuna ƙone turare wa Ba’al kuna kuma bin waɗansu allolin da ba ku sani ba,
Você vai roubar, assassinar, cometer adultério, jurar falsamente, queimar incenso para Baal, e andar atrás de outros deuses que você não conheceu,
10 sa’an nan ku zo ku tsaya a gabana a wannan gida, wanda ake kira da Sunana, kuna cewa, “An cece mu,” mun dace mu aikata waɗannan abubuwa banƙyama?
então venha e fique diante de mim nesta casa, que é chamada pelo meu nome, e diga: 'Nós somos entregues', para que você possa fazer todas estas abominações?
11 Wannan gidan da ake kira da Sunana ya zama kogon’yan fashi ne a gare ku? Amma ina kallo! In ji Ubangiji.
Esta casa, que é chamada pelo meu nome, tornou-se um antro de ladrões aos seus olhos? Eis que eu mesmo a vi”, diz Yahweh.
12 “‘Yanzu ku fita zuwa Shilo inda na fara maishe shi wurin zama don Sunana, ku ga abin da na yi masa saboda muguntar mutanen Isra’ila.
“Mas vá agora para minha casa que ficava em Shiloh, onde fiz habitar meu nome no início, e veja o que fiz com ele pela maldade de meu povo Israel.
13 Yayinda kuke yin dukan waɗannan abubuwa, in ji Ubangiji, na yi muku magana sau da sau, amma ba ku ji ba; na kira ku, amma ba ku amsa ba.
Agora, porque você fez todos estes trabalhos”, diz Javé, “e eu falei com você, levantando-me cedo e falando, mas você não ouviu; e eu o chamei, mas você não respondeu;
14 Saboda haka, abin da na yi wa Shilo shi ne yanzu zan yi wa gidan da ake kira da Sunana, haikalin da kuka dogara a kai, wurin da na ba ku da kuma kakanninku.
portanto farei à casa que é chamada pelo meu nome, na qual você confia, e ao lugar que eu dei a você e a seus pais, como fiz a Shiloh.
15 Zan kore ku daga gabana, kamar yadda na yi ga dukan’yan’uwanku, mutanen Efraim.’
Eu o expulsarei de minha vista, como expulsei todos os seus irmãos, mesmo toda a descendência de Efraim.
16 “Saboda haka kada ka yi addu’a don wannan mutane ko ka yi wani kuka ko roƙo dominsu, gama ba zan ji ka ba.
“Portanto, não reze por este povo. Não levantem um grito ou oração por elas ou intercedam por mim; pois eu não os ouvirei.
17 Ba ka gani abin da suke yi a biranen Yahuda da kuma a titunan Urushalima?
Você não vê o que eles fazem nas cidades de Judá e nas ruas de Jerusalém?
18 Yara sukan tara itace, iyaye suka hura wuta, mata kuma sukan kwaɓa kullu don su yi wa Sarauniyar Sama waina. Sukan miƙa hadayun sha ga waɗansu alloli don su tsokane ni in yi fushi.
As crianças recolhem lenha, e os pais acendem o fogo, e as mulheres amassam a massa, para fazer bolos para a rainha do céu, e para derramar ofertas de bebida para outros deuses, para que me provoquem à ira.
19 Amma ni ne suke tsokana? In ji Ubangiji Ashe, ba kansu ne suke cuta, suna kunyata kansu ba?
Do eles me provocam à raiva...” diz Yahweh. “Eles não provocam a si mesmos, à confusão de seus próprios rostos?”
20 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa fushina da hasalata za su kwarara a wannan wuri, a kan mutum da dabba, a kan itatuwan fili da a kan amfanin gona, za su yi ta kuna, ba kuwa za a kashe ba.
Portanto, o Senhor Javé diz: “Eis que minha ira e minha ira se derramarão sobre este lugar, sobre o homem, sobre o animal, sobre as árvores do campo e sobre os frutos do solo; e arderá e não se apagará”.
21 “‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa ci gaba, ku ƙara hadayun ƙonawarku da sauran sadakoki ku kuma yi ta cin naman!
Yahweh dos Exércitos, o Deus de Israel diz: “Adicione suas ofertas queimadas aos seus sacrifícios e coma carne”.
22 Gama sa’ad da na fitar da kakanninku daga Masar na kuma yi musu magana, ban ba su dokoki kawai game da hadayun ƙonawa da sadakoki ba,
Pois eu não falei com seus pais nem os ordenei no dia em que os tirei da terra do Egito a respeito de holocaustos ou sacrifícios;
23 amma na ba su wannan umarni cewa ku yi mini biyayya, zan kuwa zama Allahnku ku kuma ku zama mutanena. Ku yi tafiya cikin dukan hanyoyin da na umarce ku, don ku zauna lafiya.
mas isto eu lhes ordenei, dizendo: 'Escutai minha voz, e eu serei vosso Deus, e vós sereis meu povo'. Caminhem em todo o caminho que eu vos ordeno, para que esteja bem convosco
24 Amma ba su saurara ba, ba su kuwa kula ba; a maimako, suka bi shawarar kansu da ta taurare muguwar zukatansu. Su ja da baya a maimakon yin gaba.
Mas eles não ouviram ou viraram os ouvidos, mas caminharam em seus próprios conselhos e na teimosia de seu coração maligno, e foram para trás, e não para frente.
25 Daga lokacin da kakanninku suka bar Masar har yă zuwa yau, kullum na yi ta aikan bayina annabawa.
Desde o dia em que seus pais saíram da terra do Egito até hoje, tenho enviado a vocês todos os meus servos os profetas, levantando-se diariamente cedo e enviando-os.
26 Amma ba su saurare ni ba, ba su kula ba. Sai suka taurare zukatansu suka aikata mugun abu fiye da na kakanninsu.’
No entanto, eles não me escutaram ou inclinaram o ouvido, mas endureceram seu pescoço. Eles fizeram pior do que seus pais.
27 “Sa’ad da ka faɗa musu wannan duka, ba za su saurare ka ba; sa’ad da ka kira su, ba za su amsa ba.
“Você lhes dirá todas estas palavras, mas eles não lhe darão ouvidos. Você também chamá-los-á, mas eles não lhe responderão.
28 Saboda haka ka faɗa musu cewa, ‘Wannan ce al’ummar da ba tă yi biyayya ga Ubangiji Allahnta ba, ba kuwa ta karɓi gyara ba. Gaskiya ta ƙare; ta ɓace gaba ɗaya daga leɓunansu.
“Dir-lhes-eis: “Esta é a nação que não escutou a voz de Javé, nem recebeu instruções. A verdade pereceu, e está cortada de sua boca”.
29 “‘Ku aske gashin kanku ku zubar; ku yi makoki a filayen tuddai, gama Ubangiji ya ƙi’yan zamanin nan ya kuma rabu da su saboda fushin da suka ba shi.
Corte seu cabelo e jogue-o fora, e faça uma lamentação sobre as alturas nuas; pois Javé rejeitou e abandonou a geração de sua ira.
30 “‘Mutanen Yahuda sun yi mugunta a gabana, in ji Ubangiji. Sun kafa gumakansu masu banƙyama a gidan da ake kira da Sunana suka ƙazantar da shi.
“Pois as crianças de Judá fizeram o que é mau aos meus olhos”, diz Yahweh. “Eles colocaram suas abominações na casa que é chamada pelo meu nome, para profaná-la”.
31 Sun gida masujadan Tofet a Kwarin Ben Hinnom don miƙa’ya’yansu maza da mata a wuta, abin da ban yi umarni ba, ba kuwa yi tunaninsa ba.
Eles construíram os lugares altos de Topheth, que fica no vale do filho de Hinnom, para queimar seus filhos e suas filhas no fogo, o que eu não ordenei, nem me veio à mente.
32 Saboda haka ku yi hankali, kwanaki suna zuwa in ji Ubangiji, sa’ad da mutane ba za su ƙara kira wurin Tofet ko Kwarin Ben Hinnom ba, amma Kwarin Kisa, gama za su binne matattu a Tofet sai har ba sauran wuri.
Portanto, eis que vêm os dias”, diz Javé, “que não se chamará mais 'Topheth' ou 'O vale do filho de Hinnom', mas 'O vale da Matança'; pois eles enterrarão em Topheth até que não haja mais lugar para enterrar.
33 Sa’an nan gawawwakin wannan mutane za su zama abinci ga tsuntsayen sama da kuma namun jeji, ba za a kuwa sami wani da zai kore su ba.
Os cadáveres deste povo serão alimento para as aves do céu, e para os animais da terra. Ninguém os afugentará.
34 Zan kawo ƙarshen muryar murna da farin ciki da muryar amarya da ango a garuruwan Yahuda da kuma a titunan Urushalima, gama ƙasar za tă zama kufai.
Então farei cessar das cidades de Judá e das ruas de Jerusalém a voz da alegria e a voz da alegria, a voz do noivo e a voz da noiva; pois a terra se tornará um desperdício”.

< Irmiya 7 >