< Irmiya 7 >

1 Maganar da ta zo wa Irmiya ke nan daga Ubangiji.
The woordes that came to Ieremiah from the Lord, saying,
2 “Ka tsaya a ƙofar gidan Ubangiji, a can kuwa ka yi shelar wannan saƙo. “‘Ku ji maganar Ubangiji, dukanku mutanen Yahuda waɗanda suke shiga ta waɗannan ƙofofi don yin sujada ga Ubangiji.
Stand in the gate of the Lordes house and crie this woorde there, and say, Heare the woorde of the Lord, all yee of Iudah that enter in at these gates to worship the Lord.
3 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allahna Isra’ila, yana cewa ku gyara hanyoyinku da ayyukanku, zan kuwa bar ku ku zauna a wannan wuri.
Thus sayeth the Lord of hostes, the God of Israel, Amend your waies and your woorkes, and I will let you dwell in this place.
4 Kada ku dogara ga maganganun nan na ruɗarwa cewa, “Wannan shi ne haikalin Ubangiji, haikalin Ubangiji, haikalin Ubangiji!”
Trust not in lying woordes, saying, The Temple of the Lord, the Temple of the Lord: this is the Temple of the Lord.
5 In dai kuka canja hanyoyinku da ayyukanku kuma kuna aikata adalci da junanku,
For if you amende and redresse your waies and your woorkes: if you execute iudgement betweene a man and his neighbour,
6 in ba ku zalunci baƙo, maraya ko gwauruwa ba kuma in ba ku zub da jinin marar laifi a wannan wuri ba, in kuma ba ku bi waɗansu alloli da za su cuce ku ba,
And oppresse not the stranger, the fatherlesse and the widow and shed no innocent blood in this place, neither walke after other gods to your destruction,
7 to, zan bar ku ku zauna a wannan wuri, a ƙasar da na ba kakanninku har abada abadin.
Then will I let you dwell in this place in the lande that I gaue vnto your fathers, for euer and euer.
8 Amma ga shi, kuna dogara ga maganganu na ruɗami marasa amfani.
Beholde, you trust in lying woordes, that can not profite.
9 “‘Za ku yi sata da kisa, ku yi zina da rantsuwar ƙarya, kuna ƙone turare wa Ba’al kuna kuma bin waɗansu allolin da ba ku sani ba,
Will you steale, murder, and commit adulterie, and sweare falsely and burne incense vnto Baal, and walke after other gods whome yee knowe not?
10 sa’an nan ku zo ku tsaya a gabana a wannan gida, wanda ake kira da Sunana, kuna cewa, “An cece mu,” mun dace mu aikata waɗannan abubuwa banƙyama?
And come and stande before mee in this House, whereupon my Name is called, and saye, We are deliuered, though we haue done all these abominations?
11 Wannan gidan da ake kira da Sunana ya zama kogon’yan fashi ne a gare ku? Amma ina kallo! In ji Ubangiji.
Is this House become a denne of theeues, whereupon my Name is called before your eyes? Beholde, euen I see it, sayeth the Lord.
12 “‘Yanzu ku fita zuwa Shilo inda na fara maishe shi wurin zama don Sunana, ku ga abin da na yi masa saboda muguntar mutanen Isra’ila.
But go ye nowe vnto my place which was in Shilo, where I set my Name at the beginning, and beholde, what I did to it for the wickednesse of my people Israel.
13 Yayinda kuke yin dukan waɗannan abubuwa, in ji Ubangiji, na yi muku magana sau da sau, amma ba ku ji ba; na kira ku, amma ba ku amsa ba.
Therefore nowe because yee haue done all these woorkes, sayeth the Lord, (and I rose vp earely and spake vnto you: but when I spake, yee would not heare me, neither when I called, would yee answere).
14 Saboda haka, abin da na yi wa Shilo shi ne yanzu zan yi wa gidan da ake kira da Sunana, haikalin da kuka dogara a kai, wurin da na ba ku da kuma kakanninku.
Therefore will I do vnto this House, wherupon my Name is called, wherein also yee trust, euen vnto the place that I gaue to you and to your fathers, as I haue done vnto Shilo.
15 Zan kore ku daga gabana, kamar yadda na yi ga dukan’yan’uwanku, mutanen Efraim.’
And I will cast you out of my sight, as I haue cast out all your brethren, euen the whole seede of Ephraim.
16 “Saboda haka kada ka yi addu’a don wannan mutane ko ka yi wani kuka ko roƙo dominsu, gama ba zan ji ka ba.
Therfore thou shalt not pray for this people, neither lift vp crie or praier for them neither intreat me, for I will not heare thee.
17 Ba ka gani abin da suke yi a biranen Yahuda da kuma a titunan Urushalima?
Seest thou not what they doe in the cities of Iudah and in the streetes of Ierusalem?
18 Yara sukan tara itace, iyaye suka hura wuta, mata kuma sukan kwaɓa kullu don su yi wa Sarauniyar Sama waina. Sukan miƙa hadayun sha ga waɗansu alloli don su tsokane ni in yi fushi.
The children gather wood, and the fathers kindle the fire, and the women knede the dough to make cakes to the Queene of heauen and to powre out drinke offrings vnto other gods, that they may prouoke me vnto anger.
19 Amma ni ne suke tsokana? In ji Ubangiji Ashe, ba kansu ne suke cuta, suna kunyata kansu ba?
Doe they prouoke me to anger, sayeth the Lord, and not themselues to the confusion of their owne faces?
20 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa fushina da hasalata za su kwarara a wannan wuri, a kan mutum da dabba, a kan itatuwan fili da a kan amfanin gona, za su yi ta kuna, ba kuwa za a kashe ba.
Therefore thus sayeth the Lord God, Beholde, mine anger and my wrath shall be powred vpon this place, vpon man and vpon beast, and vpon the tree of the fielde, and vpon the fruite of the grounde, and it shall burne and not bee quenched.
21 “‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa ci gaba, ku ƙara hadayun ƙonawarku da sauran sadakoki ku kuma yi ta cin naman!
Thus sayth the Lord of hostes, the God of Israel, Put your burnt offerings vnto your sacrifices, and eat the flesh.
22 Gama sa’ad da na fitar da kakanninku daga Masar na kuma yi musu magana, ban ba su dokoki kawai game da hadayun ƙonawa da sadakoki ba,
For I spake not vnto your fathers, nor commanded them, when I brought them out of the land of Egypt, concerning burnt offrings and sacrifices.
23 amma na ba su wannan umarni cewa ku yi mini biyayya, zan kuwa zama Allahnku ku kuma ku zama mutanena. Ku yi tafiya cikin dukan hanyoyin da na umarce ku, don ku zauna lafiya.
But this thing commanded I them, saying, Obey my voyce, and I will be your God, and yee shalbe my people: and walke yee in all the wayes which I haue commanded you, that it may be well vnto you.
24 Amma ba su saurara ba, ba su kuwa kula ba; a maimako, suka bi shawarar kansu da ta taurare muguwar zukatansu. Su ja da baya a maimakon yin gaba.
But they would not obey, nor incline their eare, but went after the counsels and the stubbernesse of their wicked heart, and went backewarde and not forwarde.
25 Daga lokacin da kakanninku suka bar Masar har yă zuwa yau, kullum na yi ta aikan bayina annabawa.
Since the day that your fathers came vp out of the lande of Egypt, vnto this day, I haue euen sent vnto you al my seruants the Prophets, rising vp earely euery day, and sending them.
26 Amma ba su saurare ni ba, ba su kula ba. Sai suka taurare zukatansu suka aikata mugun abu fiye da na kakanninsu.’
Yet would they not heare me nor encline their eare, but hardened their necke and did worse then their fathers.
27 “Sa’ad da ka faɗa musu wannan duka, ba za su saurare ka ba; sa’ad da ka kira su, ba za su amsa ba.
Therefore shalt thou speake al these words vnto them, but they will not heare thee: thou shalt also crie vnto them, but they will not answere thee.
28 Saboda haka ka faɗa musu cewa, ‘Wannan ce al’ummar da ba tă yi biyayya ga Ubangiji Allahnta ba, ba kuwa ta karɓi gyara ba. Gaskiya ta ƙare; ta ɓace gaba ɗaya daga leɓunansu.
But thou shalt say vnto them, This is a nation that heareth not the voice of the Lord their God, nor receiueth discipline: trueth is perished, and is cleane gone out of their mouth.
29 “‘Ku aske gashin kanku ku zubar; ku yi makoki a filayen tuddai, gama Ubangiji ya ƙi’yan zamanin nan ya kuma rabu da su saboda fushin da suka ba shi.
Cut off thine heare, O Ierusalem, and cast it away, and take vp a complaint on the hie places: for the Lord hath reiected and forsaken the generation of his wrath.
30 “‘Mutanen Yahuda sun yi mugunta a gabana, in ji Ubangiji. Sun kafa gumakansu masu banƙyama a gidan da ake kira da Sunana suka ƙazantar da shi.
For the children of Iudah haue done euill in my sight, sayth the Lord: they haue set their abominations in the House, whereupon my Name is called, to pollute it.
31 Sun gida masujadan Tofet a Kwarin Ben Hinnom don miƙa’ya’yansu maza da mata a wuta, abin da ban yi umarni ba, ba kuwa yi tunaninsa ba.
And they haue built the hie place of Topheth, which is in the valley of Ben-Hinnom to burne their sonnes and their daughters in the fire, which I commanded them not, neither came it in mine heart.
32 Saboda haka ku yi hankali, kwanaki suna zuwa in ji Ubangiji, sa’ad da mutane ba za su ƙara kira wurin Tofet ko Kwarin Ben Hinnom ba, amma Kwarin Kisa, gama za su binne matattu a Tofet sai har ba sauran wuri.
Therefore beholde, the dayes come, sayeth the Lord, that it shall no more be called Topheth, nor the valley of Ben-Hinnom, but the valley of slaughter: for they shall burie in Topheth til there be no place.
33 Sa’an nan gawawwakin wannan mutane za su zama abinci ga tsuntsayen sama da kuma namun jeji, ba za a kuwa sami wani da zai kore su ba.
And ye carkeises of this people shalbe meat for the foules of the heauen and for the beastes of the earth, and none shall fraie them away.
34 Zan kawo ƙarshen muryar murna da farin ciki da muryar amarya da ango a garuruwan Yahuda da kuma a titunan Urushalima, gama ƙasar za tă zama kufai.
Then I will cause to cease from the cities of Iudah and from the streetes of Ierusalem the voice of mirth and the voice of gladnesse, the voice of the bridegrom and the voice of the bride: for the lande shalbe desolate.

< Irmiya 7 >