< Irmiya 7 >

1 Maganar da ta zo wa Irmiya ke nan daga Ubangiji.
2 “Ka tsaya a ƙofar gidan Ubangiji, a can kuwa ka yi shelar wannan saƙo. “‘Ku ji maganar Ubangiji, dukanku mutanen Yahuda waɗanda suke shiga ta waɗannan ƙofofi don yin sujada ga Ubangiji.
Hear you the word of the Lord, all Judea.
3 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allahna Isra’ila, yana cewa ku gyara hanyoyinku da ayyukanku, zan kuwa bar ku ku zauna a wannan wuri.
Thus says the Lord God of Israel, Correct your ways and your devices, and I will cause you to dwell in this place.
4 Kada ku dogara ga maganganun nan na ruɗarwa cewa, “Wannan shi ne haikalin Ubangiji, haikalin Ubangiji, haikalin Ubangiji!”
Trust not in yourselves with lying words, for they shall not profit you at all, saying, It is the temple of the Lord, the temple of the Lord.
5 In dai kuka canja hanyoyinku da ayyukanku kuma kuna aikata adalci da junanku,
For if you thoroughly correct your ways and your practices, and do indeed execute judgement between a man and his neighbour;
6 in ba ku zalunci baƙo, maraya ko gwauruwa ba kuma in ba ku zub da jinin marar laifi a wannan wuri ba, in kuma ba ku bi waɗansu alloli da za su cuce ku ba,
and oppress not the stranger, and the orphan, and the widow, and shed not innocent blood in this place, and go not after strange gods to your hurt:
7 to, zan bar ku ku zauna a wannan wuri, a ƙasar da na ba kakanninku har abada abadin.
then will I cause you to dwell in this place, in the land which I gave to your fathers of old and for ever.
8 Amma ga shi, kuna dogara ga maganganu na ruɗami marasa amfani.
But whereas you have trusted in lying words, whereby you shall not be profited;
9 “‘Za ku yi sata da kisa, ku yi zina da rantsuwar ƙarya, kuna ƙone turare wa Ba’al kuna kuma bin waɗansu allolin da ba ku sani ba,
and you murder, and commit adultery, and steal, and swear falsely, and burn incense to Baal, and are gone after strange gods whom you know not,
10 sa’an nan ku zo ku tsaya a gabana a wannan gida, wanda ake kira da Sunana, kuna cewa, “An cece mu,” mun dace mu aikata waɗannan abubuwa banƙyama?
so that it is evil with you; yet have you come, and stood before me in the house, whereon my name is called, and you have said, We have refrained from doing all these abominations.
11 Wannan gidan da ake kira da Sunana ya zama kogon’yan fashi ne a gare ku? Amma ina kallo! In ji Ubangiji.
Is my house, whereon my name is called, a den of robbers in your eyes? And, behold, I have seen [it], says the Lord.
12 “‘Yanzu ku fita zuwa Shilo inda na fara maishe shi wurin zama don Sunana, ku ga abin da na yi masa saboda muguntar mutanen Isra’ila.
For go you to my place with is in Selo, where I caused my name to dwell before, and see what I did to it because of the wickedness of my people Israel.
13 Yayinda kuke yin dukan waɗannan abubuwa, in ji Ubangiji, na yi muku magana sau da sau, amma ba ku ji ba; na kira ku, amma ba ku amsa ba.
And now, because you have done all these deeds, and I spoke to you, but you listened not to me; and I called you, but you answered not;
14 Saboda haka, abin da na yi wa Shilo shi ne yanzu zan yi wa gidan da ake kira da Sunana, haikalin da kuka dogara a kai, wurin da na ba ku da kuma kakanninku.
therefore I also will do to the house whereon my name is called, wherein you trust, and to the place which I gave to you and to your fathers, as I did to Selo.
15 Zan kore ku daga gabana, kamar yadda na yi ga dukan’yan’uwanku, mutanen Efraim.’
And I will cast you out of my sight, as I cast away your brethren, all the seed of Ephraim.
16 “Saboda haka kada ka yi addu’a don wannan mutane ko ka yi wani kuka ko roƙo dominsu, gama ba zan ji ka ba.
Therefore pray not you for this people, and intercede not for them to be pitied, yes, pray not, and approach me not for them: for I will not listen [to you].
17 Ba ka gani abin da suke yi a biranen Yahuda da kuma a titunan Urushalima?
Seest you not what they do in the cities of Juda, and in the streets of Jerusalem?
18 Yara sukan tara itace, iyaye suka hura wuta, mata kuma sukan kwaɓa kullu don su yi wa Sarauniyar Sama waina. Sukan miƙa hadayun sha ga waɗansu alloli don su tsokane ni in yi fushi.
Their children gather wood, and their fathers kindle a fire, and their women knead dough, to make cakes to the host of heaven; and they have poured out drink-offerings to strange gods, that they might provoke me to anger.
19 Amma ni ne suke tsokana? In ji Ubangiji Ashe, ba kansu ne suke cuta, suna kunyata kansu ba?
Do they provoke me to anger? says the Lord: do they not [provoke] themselves, that their faces may be ashamed?
20 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa fushina da hasalata za su kwarara a wannan wuri, a kan mutum da dabba, a kan itatuwan fili da a kan amfanin gona, za su yi ta kuna, ba kuwa za a kashe ba.
Therefore thus says the Lord; Behold, my anger and wrath shall be poured out upon this place, and upon the men, and upon the cattle, and upon every tree of their field, and upon the fruits of the land; and it shall burn, and not be quenched.
21 “‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa ci gaba, ku ƙara hadayun ƙonawarku da sauran sadakoki ku kuma yi ta cin naman!
Thus says the Lord, Gather your whole burnt offerings with your meat-offerings, and eat flesh.
22 Gama sa’ad da na fitar da kakanninku daga Masar na kuma yi musu magana, ban ba su dokoki kawai game da hadayun ƙonawa da sadakoki ba,
For I spoke not to your fathers, and commanded them not in the day wherein I brought them up out of the land of Egypt, concerning whole burnt offerings and sacrifice:
23 amma na ba su wannan umarni cewa ku yi mini biyayya, zan kuwa zama Allahnku ku kuma ku zama mutanena. Ku yi tafiya cikin dukan hanyoyin da na umarce ku, don ku zauna lafiya.
but I commanded them this thing, saying, Hear you my voice, and I will be to you a God, and you shall be to me a people: and walk you in all my ways which I shall command you, that it may be well with you.
24 Amma ba su saurara ba, ba su kuwa kula ba; a maimako, suka bi shawarar kansu da ta taurare muguwar zukatansu. Su ja da baya a maimakon yin gaba.
But they listened not to me, and their ear gave no heed, but they walked in the imaginations of their evil heart, and went backward, and not forward;
25 Daga lokacin da kakanninku suka bar Masar har yă zuwa yau, kullum na yi ta aikan bayina annabawa.
from the day that their fathers went forth out of the land of Egypt, even until this day. And I sent to you all my servants, the prophets, by day and early in the morning: yes, I sent [them],
26 Amma ba su saurare ni ba, ba su kula ba. Sai suka taurare zukatansu suka aikata mugun abu fiye da na kakanninsu.’
but they listened not to me, and their ear gave no heed; and they made their neck harder than their fathers.
27 “Sa’ad da ka faɗa musu wannan duka, ba za su saurare ka ba; sa’ad da ka kira su, ba za su amsa ba.
Therefore you shall speak this word to them;
28 Saboda haka ka faɗa musu cewa, ‘Wannan ce al’ummar da ba tă yi biyayya ga Ubangiji Allahnta ba, ba kuwa ta karɓi gyara ba. Gaskiya ta ƙare; ta ɓace gaba ɗaya daga leɓunansu.
This is the nation which has not listened to the voice of the Lord, nor received correction: truth has failed from their mouth.
29 “‘Ku aske gashin kanku ku zubar; ku yi makoki a filayen tuddai, gama Ubangiji ya ƙi’yan zamanin nan ya kuma rabu da su saboda fushin da suka ba shi.
Cut off your hair, and cast it away, and take up a lamentation on your lips; for the Lord has reprobated and rejected the generation that does these things.
30 “‘Mutanen Yahuda sun yi mugunta a gabana, in ji Ubangiji. Sun kafa gumakansu masu banƙyama a gidan da ake kira da Sunana suka ƙazantar da shi.
For the children of Juda have wrought evil before me, says the Lord; they have set their abominations in the house on which my name is called, to defile it.
31 Sun gida masujadan Tofet a Kwarin Ben Hinnom don miƙa’ya’yansu maza da mata a wuta, abin da ban yi umarni ba, ba kuwa yi tunaninsa ba.
And they have built the altar of Taphes, which is in the valley of the son of Ennom, to burn their sons and their daughters with fire; which I did not command them [to do], neither did I design it in my heart.
32 Saboda haka ku yi hankali, kwanaki suna zuwa in ji Ubangiji, sa’ad da mutane ba za su ƙara kira wurin Tofet ko Kwarin Ben Hinnom ba, amma Kwarin Kisa, gama za su binne matattu a Tofet sai har ba sauran wuri.
Therefore, behold, the days come, says the Lord, when they shall no more say, The altar of Taphes, and the valley of the son of Ennom, but, The valley of the slain; and they shall bury in Taphes, for lack of room.
33 Sa’an nan gawawwakin wannan mutane za su zama abinci ga tsuntsayen sama da kuma namun jeji, ba za a kuwa sami wani da zai kore su ba.
And the dead bodies of this people shall be for food to the birds of the sky, and to the wild beasts of the earth; and there shall be none to drive [them] away.
34 Zan kawo ƙarshen muryar murna da farin ciki da muryar amarya da ango a garuruwan Yahuda da kuma a titunan Urushalima, gama ƙasar za tă zama kufai.
And I will destroy out of the cities of Juda, and the streets of Jerusalem, the voice of them that make merry, and the voice of them that rejoice, the voice of the bridegroom, and the voice of the bride; for the whole land shall become a desolation.

< Irmiya 7 >