< Irmiya 7 >

1 Maganar da ta zo wa Irmiya ke nan daga Ubangiji.
Ovo je riječ što dođe Jeremiji od Gospodina:
2 “Ka tsaya a ƙofar gidan Ubangiji, a can kuwa ka yi shelar wannan saƙo. “‘Ku ji maganar Ubangiji, dukanku mutanen Yahuda waɗanda suke shiga ta waɗannan ƙofofi don yin sujada ga Ubangiji.
“Stani pred vrata Doma Jahvina, objavi ondje ovu riječ. Reci: Čujte riječ Jahvinu, svi Judejci koji ulazite na ova vrata da se poklonite Jahvi.
3 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allahna Isra’ila, yana cewa ku gyara hanyoyinku da ayyukanku, zan kuwa bar ku ku zauna a wannan wuri.
Ovako govori Jahve nad Vojskama, Bog Izraelov: 'Popravite svoje putove i djela svoja, pa ću boraviti s vama na ovome mjestu.
4 Kada ku dogara ga maganganun nan na ruɗarwa cewa, “Wannan shi ne haikalin Ubangiji, haikalin Ubangiji, haikalin Ubangiji!”
Ne uzdajte se u lažne riječi: 'Svetište Jahvino! Svetište Jahvino! Svetište Jahvino!'
5 In dai kuka canja hanyoyinku da ayyukanku kuma kuna aikata adalci da junanku,
Ali ako zaista popravite svoje putove i djela svoja i ako zaista budete činili što je pravo, svatko prema bližnjemu svome,
6 in ba ku zalunci baƙo, maraya ko gwauruwa ba kuma in ba ku zub da jinin marar laifi a wannan wuri ba, in kuma ba ku bi waɗansu alloli da za su cuce ku ba,
ako ne budete tlačili stranca, sirote i udovice i ne budete prolijevali krvi nedužne na ovome mjestu, ako ne budete trčali za tuđim bogovima na svoju nesreću -
7 to, zan bar ku ku zauna a wannan wuri, a ƙasar da na ba kakanninku har abada abadin.
boravit ću s vama na ovome mjestu, u zemlji koju sam dao vašim ocima zauvijek.
8 Amma ga shi, kuna dogara ga maganganu na ruɗami marasa amfani.
Ali se vi uzdate u lažne i beskorisne riječi!
9 “‘Za ku yi sata da kisa, ku yi zina da rantsuwar ƙarya, kuna ƙone turare wa Ba’al kuna kuma bin waɗansu allolin da ba ku sani ba,
Zar da kradete, ubijate, činite preljub, krivo se zaklinjete, palite tamjan Baalu i trčite za tuđim bogovima kojih ne poznajete,
10 sa’an nan ku zo ku tsaya a gabana a wannan gida, wanda ake kira da Sunana, kuna cewa, “An cece mu,” mun dace mu aikata waɗannan abubuwa banƙyama?
a onda da dolazite i stojite preda mnom u Domu ovome koji nosi moje ime i govorite: 'Spašeni smo!' i da nakon toga opet činite nedjela i opačine?
11 Wannan gidan da ake kira da Sunana ya zama kogon’yan fashi ne a gare ku? Amma ina kallo! In ji Ubangiji.
Zar je Dom ovaj, koji se zove mojim imenom, u vašim očima pećina razbojnička? Ali ja dobro vidim” - riječ je Jahvina.
12 “‘Yanzu ku fita zuwa Shilo inda na fara maishe shi wurin zama don Sunana, ku ga abin da na yi masa saboda muguntar mutanen Isra’ila.
“Pođite, dakle, na moje mjesto koje je u Šilu, gdje nekoć nastanih ime svoje, i pogledajte što od njega učinih zbog opačina naroda svoga izraelskoga.
13 Yayinda kuke yin dukan waɗannan abubuwa, in ji Ubangiji, na yi muku magana sau da sau, amma ba ku ji ba; na kira ku, amma ba ku amsa ba.
Kako činite sva ona ista nedjela - riječ je Jahvina - i premda vas neumorno opominjem, vi ne slušate, a kad vas zovem, vi se ne odazivate:
14 Saboda haka, abin da na yi wa Shilo shi ne yanzu zan yi wa gidan da ake kira da Sunana, haikalin da kuka dogara a kai, wurin da na ba ku da kuma kakanninku.
od ovoga Doma što se zove mojim imenom, u koje se vi uzdate, i od ovoga mjesta što ga dadoh vama i ocima vašim učinit ću isto što sam učinio i od Šila.
15 Zan kore ku daga gabana, kamar yadda na yi ga dukan’yan’uwanku, mutanen Efraim.’
Odbacit ću vas od lica svojega kao što odbacih svu braću vašu, sve potomstvo Efrajimovo.”
16 “Saboda haka kada ka yi addu’a don wannan mutane ko ka yi wani kuka ko roƙo dominsu, gama ba zan ji ka ba.
“A ti ne moli milosti za narod ovaj, ne diži glasa za njih i ne moli, ne navaljuj na me jer te neću uslišiti.
17 Ba ka gani abin da suke yi a biranen Yahuda da kuma a titunan Urushalima?
Ne vidiš li što čine po gradovima judejskim i po ulicama jeruzalemskim?
18 Yara sukan tara itace, iyaye suka hura wuta, mata kuma sukan kwaɓa kullu don su yi wa Sarauniyar Sama waina. Sukan miƙa hadayun sha ga waɗansu alloli don su tsokane ni in yi fushi.
Djeca kupe drva, oci pale vatru, žene mijese tijesto da ispeku kolače 'kraljici neba' i lijevaju ljevanice tuđim bogovima da me pogrde.
19 Amma ni ne suke tsokana? In ji Ubangiji Ashe, ba kansu ne suke cuta, suna kunyata kansu ba?
Zar mene tim pogrđuju - riječ je Jahvina - a ne sebe na svoju sramotu?”
20 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa fushina da hasalata za su kwarara a wannan wuri, a kan mutum da dabba, a kan itatuwan fili da a kan amfanin gona, za su yi ta kuna, ba kuwa za a kashe ba.
I stoga ovako govori Jahve Gospod: “Evo, gnjev svoj i jarost svoju izlit ću na ovo mjesto, na ljude i na stoku, na poljsko drveće i na plodove zemlje, rasplamtjet će se i neće se ugasiti.”
21 “‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa ci gaba, ku ƙara hadayun ƙonawarku da sauran sadakoki ku kuma yi ta cin naman!
Ovako govori Jahve nad Vojskama, Bog Izraelov: “Paljenicama dometnite još i klanice, i jedite meso.
22 Gama sa’ad da na fitar da kakanninku daga Masar na kuma yi musu magana, ban ba su dokoki kawai game da hadayun ƙonawa da sadakoki ba,
Ja ništa ne rekoh ocima vašim o paljenicama i klanicama, niti im što o tom zapovjedih kad ih izvedoh iz zemlje egipatske.
23 amma na ba su wannan umarni cewa ku yi mini biyayya, zan kuwa zama Allahnku ku kuma ku zama mutanena. Ku yi tafiya cikin dukan hanyoyin da na umarce ku, don ku zauna lafiya.
Ovo im ja zapovjedih: 'Slušajte glas moj, pa ću ja biti vaš Bog, a vi ćete biti moj narod. Idite putem kojim vam zapovjedih, da vam dobro bude.'
24 Amma ba su saurara ba, ba su kuwa kula ba; a maimako, suka bi shawarar kansu da ta taurare muguwar zukatansu. Su ja da baya a maimakon yin gaba.
A oni ne poslušaše, uho svoje ne prignuše, već pođoše po savjetu i okorjelosti zloga srca svojega; okrenuše mi leđa, a ne lice.
25 Daga lokacin da kakanninku suka bar Masar har yă zuwa yau, kullum na yi ta aikan bayina annabawa.
Od dana kad oci vaši iziđoše iz zemlje egipatske pa do dana današnjeg slao sam vam tolike sluge svoje, proroke, iz dana u dan, neumorno.
26 Amma ba su saurare ni ba, ba su kula ba. Sai suka taurare zukatansu suka aikata mugun abu fiye da na kakanninsu.’
Ali me oni nisu slušali, uho svoje nisu prignuli, nego otvrdnuše, gori od otaca svojih.
27 “Sa’ad da ka faɗa musu wannan duka, ba za su saurare ka ba; sa’ad da ka kira su, ba za su amsa ba.
Možeš im sve to reći, ali te neće poslušati; zovi ih, neće ti se odazvati.
28 Saboda haka ka faɗa musu cewa, ‘Wannan ce al’ummar da ba tă yi biyayya ga Ubangiji Allahnta ba, ba kuwa ta karɓi gyara ba. Gaskiya ta ƙare; ta ɓace gaba ɗaya daga leɓunansu.
Zato im reci: 'Ovo je narod koji ne sluša glasa Jahve, Boga svojega, i ne prima opomenÄe. Nestade istine, nestade je iz usta njihovih.'”
29 “‘Ku aske gashin kanku ku zubar; ku yi makoki a filayen tuddai, gama Ubangiji ya ƙi’yan zamanin nan ya kuma rabu da su saboda fushin da suka ba shi.
Ostriži svoju dugu kosu, baci je. Po goletima protuži tužaljkom, jer Jahve odbaci i odvrgnu rod na koji se razgnjevio.
30 “‘Mutanen Yahuda sun yi mugunta a gabana, in ji Ubangiji. Sun kafa gumakansu masu banƙyama a gidan da ake kira da Sunana suka ƙazantar da shi.
“Da, sinovi Judini čine što je zlo u očima mojim” - riječ je Jahvina. “Postaviše grozote u Dom koji se mojim zove imenom, da ga oskvrnu;
31 Sun gida masujadan Tofet a Kwarin Ben Hinnom don miƙa’ya’yansu maza da mata a wuta, abin da ban yi umarni ba, ba kuwa yi tunaninsa ba.
podigoše uzvišice tofetske u Dolini Ben Hinomu i spaljuju vatrom svoje sinove i kćeri - što im ja nikad ne zapovjedih niti mi to ikada na um pade.
32 Saboda haka ku yi hankali, kwanaki suna zuwa in ji Ubangiji, sa’ad da mutane ba za su ƙara kira wurin Tofet ko Kwarin Ben Hinnom ba, amma Kwarin Kisa, gama za su binne matattu a Tofet sai har ba sauran wuri.
Stoga evo dolaze dani - riječ je Jahvina - kad se više neće reći Tofet ni Dolina Ben Hinom, nego Dolina klanja. U Tofetu će se pokapati mrtvi, jer drugdje neće biti mjesta.
33 Sa’an nan gawawwakin wannan mutane za su zama abinci ga tsuntsayen sama da kuma namun jeji, ba za a kuwa sami wani da zai kore su ba.
A mrtva tijela ovoga naroda bit će hrana pticama nebeskim i zvjeradi zemaljskoj, i nitko se neće naći da ih poplaši i otjera.
34 Zan kawo ƙarshen muryar murna da farin ciki da muryar amarya da ango a garuruwan Yahuda da kuma a titunan Urushalima, gama ƙasar za tă zama kufai.
Uklonit ću iz gradova judejskih i s ulica jeruzalemskih radost i veselje: jer će se zemlja ta pretvoriti u pustinju.”

< Irmiya 7 >