< Irmiya 6 >

1 “Ku gudu neman mafaka, mutanen Benyamin! Ku gudu daga Urushalima! Ku busa ƙaho a Tekowa! Ku ba da alama a Bet-Hakkerem! Gama masifa tana zuwa daga arewa, mummunar hallaka ce kuwa.
Flytt bort, I Benjamins barn, ut av Jerusalem, og støt i basun i Tekoa og reis op et tegn over Bet-Hakkerem! For ulykke truer fra nord med stor ødeleggelse.
2 Zan hallaka Diyar Sihiyona, kyakkyawa da kuma mai laulayi.
Den fagre og forkjælede, Sions datter, gjør jeg til intet.
3 Makiyaya da garkunansu za su taso mata; za su kafa tentunansu kewaye da ita, kowanne yana lura da sashensa.”
Til henne skal hyrder komme med sine hjorder; de slår op telt mot henne rundt omkring, de beiter av hver sitt stykke.
4 “Mu shirya don yaƙi da ita! Ku tashi, bari mu fāɗa mata da tsakar rana! Amma, kaito, rana tana fāɗuwa, inuwar yamma kuwa sai ƙaran tsawo take.
Innvi eder til krig mot henne! Stå op og la oss dra op om middagen! Ve oss! For dagen heller, og aftenens skygger blir lange.
5 Saboda haka ku tashi, bari mu fāɗa mata da dare mu rurrushe kagaranta!”
Stå op og la oss dra op om natten, og la oss ødelegge hennes palasser!
6 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ku sassare itatuwan ku tula ƙasa kewaye da Urushalima. Dole a hukunta wannan birni; saboda ya cika da zalunci.
For så sier Herren, hærskarenes Gud: Fell trær og kast op en voll mot Jerusalem! Det er byen som skal hjemsøkes; den er aldeles full av undertrykkelse i sitt indre.
7 Kamar yadda rijiya takan ba da ruwarta, haka birnin yake da muguntarsa. Ana jin labarin rikici da hallaka a cikinsa; ciwonsa da mikinsa kullum suna a gabana.
Som en brønn lar sitt vann velle ut, således lar den sin ondskap velle ut; vold og ødeleggelse høres i den, sår og slag er alltid for mitt åsyn.
8 Ki ji gargaɗi, ya Urushalima, ko kuwa in juya daga gare ki in mai da ƙasarki kufai don kada wani ya zauna a cikinta.”
La dig advare, Jerusalem, så ikke min sjel skal vende sig fra dig, så jeg ikke skal gjøre dig til en ørken, til et ubygget land!
9 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Bari su yi kalan raguwar Isra’ila a yi kalan sarai yadda ake yi wa inabi; ka sāke miƙa hannunka a kan rassan, kamar mai tattara inabi.”
Så sier Herren, hærskarenes Gud: En efterhøst skal de holde på det som er blitt igjen av Israel, likesom på et vintre. Rekk atter og atter ut din hånd, likesom vinhøsteren til rankene!
10 Ga wa zan yi magana in kuma gargaɗar? Wa zai saurare ni? Kunnuwansu sun toshe don kada su ji. Maganar Ubangiji ta zama abin zargi a gare su; ba sa jin daɗinta.
Hvem skal jeg tale og vidne for, så de hører? Se, deres øre er uomskåret, så de ikke kan gi akt; se, Herrens ord er blitt til spott blandt dem, de liker det ikke;
11 Amma ina cike da fushin Ubangiji, kuma ba na iya kannewa. “Ka kwararo shi a kan yara a titi da kuma a kan samarin da suka tattaru; za a kama miji da mata a cikinsa, tsofaffi da suka tsufa tukub.
men jeg er fylt av Herrens vrede, jeg er trett av å holde den hos mig. Utøs den over barnet på gaten og over de unge menns fortrolige krets! Ja, både mann og kvinne skal rammes, både den gamle og den eldgamle,
12 Za a ba da gidajensu ga waɗansu, tare da gonakinsu da matansu, sa’ad da na miƙa hannuna gāba da waɗanda suke zama a ƙasar,” in ji Ubangiji.
og deres hus skal gå over til andre, og likeså deres marker og deres hustruer; for jeg vil rekke ut min hånd mot landets innbyggere, sier Herren.
13 “Daga ƙarami zuwa babba, dukansu masu haɗama ne don riba; har da annabawa da firistoci, dukansu suna aikata rashin gaskiya.
For både små og store søker alle sammen urettferdig vinning; både profet og prest gjør alle sammen svik,
14 Sukan ɗaura mikin mutanena sai ka ce mikin ba shi da matsala. Suna cewa, ‘Lafiya, Lafiya,’ alhali kuwa ba lafiya.
og de læger mitt folks skade på lettferdig vis, idet de sier: Fred! Fred! Og det er dog ingen fred.
15 Suna jin kunyar halinsu na banƙyama? A’a, ba sa jin kunya sam; ba su ma san yadda za su soke kai ba. Saboda haka za su fāɗi tare da fāɗaɗɗu; za a hamɓarar da su sa’ad da na hukunta su,” in ji Ubangiji.
De skal bli til skamme, for de har gjort vederstyggelige ting. De hverken skammer sig eller kjenner til blygsel; derfor skal de falle blandt dem som faller; på den tid jeg hjemsøker dem, skal de snuble, sier Herren.
16 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku tsaya kan hanyoyi, ku duba; ku nemi hanyoyin dā, ku tambaya inda hanyar mai kyau take, ku yi tafiya a kanta, za ku kuwa sami hutu wa rayukanku. Amma kun ce, ‘Ba za mu bi ta ba.’
Så sa Herren: Stå på veiene og se til, og spør efter de gamle stier, spør hvor veien går til det gode, og vandre på den! Så skal I finne hvile for eders sjeler. Men de sa: Vi vil ikke vandre på den.
17 Na naɗa muku masu tsaro a kanku na kuma ce, ‘Ku saurari karan ƙaho!’ Amma kuka ce, ‘Ba za mu saurara ba.’
Og jeg satte vektere over eder og sa: Gi akt på basunens lyd! Men de sa: Vi vil ikke gi akt.
18 Saboda haka ku, ya al’ummai; ku lura Ya shaidu, abin da zai faru da su.
Derfor hør, I hedningefolk, og vit, du menighet, hvad som skjer iblandt dem!
19 Ki ji, ya duniya. Zan kawo masifa a kan waɗannan mutane, sakayyar ƙulle-ƙullensu, domin ba su saurari maganata ba suka kuma ƙi dokata.
Hør, du jord: Se, jeg lar ulykke komme over dette folk, frukten av deres onde råd; for på mine ord har de ikke gitt akt, og min lov har de forkastet.
20 Babu riba a kawo mini turare daga Sheba ko rake mai zaƙi daga ƙasa mai nisa? Ba zan karɓi hadayunku na ƙonawa ba; ba na jin daɗin sadakokinku.”
Hvad skal jeg med virak fra Sjeba og med den beste kalmus fra et fjernt land? Eders brennoffer er ikke til velbehag for mig, og eders slaktoffer vil jeg ikke ha.
21 Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, “Zan sa abin tuntuɓe gaban mutanena. Mahaifi da’ya’yansa maza za su yi tuntuɓe a kan juna; maƙwabci da abokansa za su hallaka.”
Derfor sier Herren så: Se, jeg setter støtestener for dette folk, og både fedre og barn skal snuble over dem; granne med granne skal omkomme.
22 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Duba, sojoji suna zuwa daga ƙasar arewa; babbar al’umma ce ta yunƙuro daga iyakokin duniya.
Så sier Herren: Se, et folk kommer fra landet i nord, et stort folk skal bryte op fra jordens ytterste ende.
23 Suna riƙe da baka da māshi; mugaye ne kuma marasa tausayi. Motsinsu kamar ƙugin teku ne yayinda suke hawan dawakansu; suna zuwa a jere kamar wanda ya yi shirin yaƙi don su fāɗa miki, ya Diyar Sihiyona.”
Bue og spyd holder de i hånden; de er grusomme og skåner ingen; deres røst bruser som havet, og på hester kommer de ridende, rustet som krigsmenn, mot dig, Sions datter!
24 Mun ji labari a kansu, hannuwanmu kuwa suka yi laƙwas. Azaba ta kama mu, zafi kamar na mace mai naƙuda.
Vi har hørt ryktet om det, våre hender er blitt kraftløse; angst har grepet oss, smerter som den fødende kvinnes.
25 Kada ku fita zuwa gonaki ko ku yi tafiya a hanyoyi, gama abokin gāba yana da takobi, kuma akwai razana ko’ina.
Gå ikke ut på marken og vandre ikke på veien! For fienden har sverd, det er redsel rundt omkring.
26 Ya mutanena, ku sanya tufafin makoki ku yi birgima a toka; ku yi kuka mai zafi irin wanda akan yi wa ɗa tilo, gama nan da nan mai hallakarwa zai auko mana.
Mitt folks datter! Omgjord dig med sekk og velt dig i aske, hold sorg som over det eneste barn, bitter veklage! Brått kommer ødeleggeren over oss.
27 “Na maishe ka mai jarrabawar ƙarfe mutanena ne kuwa ƙarfen, don ka lura ka kuma gwada hanyoyinsu.
Til en prøver har jeg satt dig blandt mitt folk, til en fast borg, forat du skal kjenne og prøve deres vei.
28 Su duka masu taurinkai ne,’yan tawaye, suna yawo suna baza jita-jita. Su tagulla ne da ƙarfe; dukansu lalatattu ne.
De er alle sammen de stridigste gjenstridige, de går omkring som baktalere, de er kobber og jern; de gjør alle det som er til skade.
29 Mazuga yana zuga da ƙarfi don yă ƙone dalma da wuta, amma tacewa yana tafiya a banza; ba a fitar da mugaye.
Blåsebelgen er opbrent av ilden, blyet er fortært; forgjeves har de smeltet og smeltet, og de onde er ikke skilt ut.
30 Ana ce da su azurfar da aka ƙi, gama Ubangiji ya ƙi su.”
Vraket sølv kalles de; for Herren har vraket dem.

< Irmiya 6 >