< Irmiya 6 >

1 “Ku gudu neman mafaka, mutanen Benyamin! Ku gudu daga Urushalima! Ku busa ƙaho a Tekowa! Ku ba da alama a Bet-Hakkerem! Gama masifa tana zuwa daga arewa, mummunar hallaka ce kuwa.
Fortifiez-vous, fils de Benjamin, au milieu de Jérusalem, et dans Thécua sonnez de la trompette, et sur Bethacarem levez l’étendard; parce qu’un mal a été vu du côté de l’aquilon, ainsi qu’une grande destruction.
2 Zan hallaka Diyar Sihiyona, kyakkyawa da kuma mai laulayi.
À une femme belle et délicate j’ai comparé la fille de Sion.
3 Makiyaya da garkunansu za su taso mata; za su kafa tentunansu kewaye da ita, kowanne yana lura da sashensa.”
Vers elle viendront les pasteurs et leurs troupeaux; ils ont dressé leurs tentes à l’entour; chacun d’eux fera paître ceux qui sont sous sa main.
4 “Mu shirya don yaƙi da ita! Ku tashi, bari mu fāɗa mata da tsakar rana! Amma, kaito, rana tana fāɗuwa, inuwar yamma kuwa sai ƙaran tsawo take.
Consacrez contre elle une guerre; levez-vous, et montons au milieu du jour; malheur à nous, parce que le jour décline, parce que les ombres du soir sont allongées.
5 Saboda haka ku tashi, bari mu fāɗa mata da dare mu rurrushe kagaranta!”
Levez-vous et montons pendant la nuit, et renversons ses maisons.
6 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ku sassare itatuwan ku tula ƙasa kewaye da Urushalima. Dole a hukunta wannan birni; saboda ya cika da zalunci.
Parce que voici ce que dit le Seigneur des armées: Coupez ses arbres, et faites autour de Jérusalem un rempart; c’est la cité de la Visitation; toute sorte de violence est au milieu d’elle.
7 Kamar yadda rijiya takan ba da ruwarta, haka birnin yake da muguntarsa. Ana jin labarin rikici da hallaka a cikinsa; ciwonsa da mikinsa kullum suna a gabana.
Comme la citerne rend froide son eau, ainsi cette cité a commis froidement ses méchancetés; iniquité et ravage, c’est ce qui sera ouï en elle; devant moi elle est toujours infirmité et plaie.
8 Ki ji gargaɗi, ya Urushalima, ko kuwa in juya daga gare ki in mai da ƙasarki kufai don kada wani ya zauna a cikinta.”
Instruis-toi, Jérusalem, de peur que mon âme ne se retire de toi, et que je ne fasse de toi un désert, une terre inhabitable.
9 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Bari su yi kalan raguwar Isra’ila a yi kalan sarai yadda ake yi wa inabi; ka sāke miƙa hannunka a kan rassan, kamar mai tattara inabi.”
Voici ce que dit le Seigneur des armées: On rassemblera les restes d’Israël comme dans une vigne jusqu’à la dernière grappe; reporte ta main comme le vendangeur dans la corbeille.
10 Ga wa zan yi magana in kuma gargaɗar? Wa zai saurare ni? Kunnuwansu sun toshe don kada su ji. Maganar Ubangiji ta zama abin zargi a gare su; ba sa jin daɗinta.
À qui parlerai-je? et qui prendrai-je à témoin pour qu’il entende? voici que leurs oreilles sont incirconcises, et qu’ils ne peuvent entendre. Voici que la parole du Seigneur leur est devenue un opprobre; et ils ne la recevront pas.
11 Amma ina cike da fushin Ubangiji, kuma ba na iya kannewa. “Ka kwararo shi a kan yara a titi da kuma a kan samarin da suka tattaru; za a kama miji da mata a cikinsa, tsofaffi da suka tsufa tukub.
C’est pour cela que je suis plein de la fureur du Seigneur et que j’ai peine à la supporter; répandez-la sur le petit enfant au dehors, et sur le conseil des jeunes gens assemblés; car l’homme sera pris avec la femme, le vieillard avec celui qui est plein de jours.
12 Za a ba da gidajensu ga waɗansu, tare da gonakinsu da matansu, sa’ad da na miƙa hannuna gāba da waɗanda suke zama a ƙasar,” in ji Ubangiji.
Et leurs maisons passeront à des étrangers, leurs champs, et leurs femmes également, parce que j’étendrai ma main sur ceux qui habitent la terre, dit le Seigneur.
13 “Daga ƙarami zuwa babba, dukansu masu haɗama ne don riba; har da annabawa da firistoci, dukansu suna aikata rashin gaskiya.
Depuis le plus petit jusqu’au plus grand, tous se livrent à l’avarice; et depuis le prophète jusqu’au prêtre, tous agissent avec tromperie.
14 Sukan ɗaura mikin mutanena sai ka ce mikin ba shi da matsala. Suna cewa, ‘Lafiya, Lafiya,’ alhali kuwa ba lafiya.
Et ils guérissaient la plaie de la fille de mon peuple avec ignominie, disant: Paix, paix; et il n’y avait point de paix.
15 Suna jin kunyar halinsu na banƙyama? A’a, ba sa jin kunya sam; ba su ma san yadda za su soke kai ba. Saboda haka za su fāɗi tare da fāɗaɗɗu; za a hamɓarar da su sa’ad da na hukunta su,” in ji Ubangiji.
Ils ont été confus, parce qu’ils ont fait des abominations; et encore ne l’ont-ils pas été entièrement, et n’ont-ils pas su rougir; à cause de cela ils tomberont parmi ceux qui sont renversés; au temps de leur Visitation, ils seront renversés tous ensemble, dit le Seigneur.
16 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku tsaya kan hanyoyi, ku duba; ku nemi hanyoyin dā, ku tambaya inda hanyar mai kyau take, ku yi tafiya a kanta, za ku kuwa sami hutu wa rayukanku. Amma kun ce, ‘Ba za mu bi ta ba.’
Voici ce que dit le Seigneur: Tenez-vous sur les voies et voyez; demandez, touchant les sentiers anciens, quelle est la bonne voie, et marchez-y; et vous trouverez un rafraîchissement pour vos âmes. Et ils ont dit: Nous n’y marcherons pas.
17 Na naɗa muku masu tsaro a kanku na kuma ce, ‘Ku saurari karan ƙaho!’ Amma kuka ce, ‘Ba za mu saurara ba.’
Et j’ai établi sur vous des sentinelles. Ecoutez la voix de la trompette. Et ils ont dit: Nous ne l’écouterons pas.
18 Saboda haka ku, ya al’ummai; ku lura Ya shaidu, abin da zai faru da su.
C’est pourquoi, écoutez, nations, et apprenez, assemblée des peuples, les grandes choses que je ferai contre eux.
19 Ki ji, ya duniya. Zan kawo masifa a kan waɗannan mutane, sakayyar ƙulle-ƙullensu, domin ba su saurari maganata ba suka kuma ƙi dokata.
Ecoute, terre: Voilà que moi j’amènerai sur ce peuple des maux, fruit de ses pensées, parce qu’ils n’ont point écouté mes paroles et qu’ils ont rejeté ma loi.
20 Babu riba a kawo mini turare daga Sheba ko rake mai zaƙi daga ƙasa mai nisa? Ba zan karɓi hadayunku na ƙonawa ba; ba na jin daɗin sadakokinku.”
Pourquoi m’apportez-vous de l’encens de Saba, et la canne à l’odeur suave d’une terre éloignée? Vos holocaustes ne me sont pas agréables, et vos victimes ne m’ont pas plu.
21 Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, “Zan sa abin tuntuɓe gaban mutanena. Mahaifi da’ya’yansa maza za su yi tuntuɓe a kan juna; maƙwabci da abokansa za su hallaka.”
À cause de cela, voici ce que dit le Seigneur: Voilà que je ferai fondre sur ce peuple des ruines; les pères y tomberont et les fils en même temps; les voisins et les proches y périront.
22 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Duba, sojoji suna zuwa daga ƙasar arewa; babbar al’umma ce ta yunƙuro daga iyakokin duniya.
Voici ce que dit le Seigneur: Voilà qu’un peuple vient de la terre de l’aquilon, et une grande nation s’élèvera des confins de la terre.
23 Suna riƙe da baka da māshi; mugaye ne kuma marasa tausayi. Motsinsu kamar ƙugin teku ne yayinda suke hawan dawakansu; suna zuwa a jere kamar wanda ya yi shirin yaƙi don su fāɗa miki, ya Diyar Sihiyona.”
Elle saisira la flèche et le bouclier; elle est cruelle et elle n’aura pas de pitié; sa voix comme la mer retentira; et ils monteront sur leurs chevaux, et préparés comme un homme qui va au combat, ils marcheront contre toi, fille de Sion.
24 Mun ji labari a kansu, hannuwanmu kuwa suka yi laƙwas. Azaba ta kama mu, zafi kamar na mace mai naƙuda.
Nous avons ouï la nouvelle de son dessein, nos mains ont défailli; la tribulation nous a saisis, et les douleurs comme la femme en travail.
25 Kada ku fita zuwa gonaki ko ku yi tafiya a hanyoyi, gama abokin gāba yana da takobi, kuma akwai razana ko’ina.
Ne sortez point dans les champs, et dans la voie ne marchez point, parce que le glaive de l’ennemi et l’épouvante sont à l’entour.
26 Ya mutanena, ku sanya tufafin makoki ku yi birgima a toka; ku yi kuka mai zafi irin wanda akan yi wa ɗa tilo, gama nan da nan mai hallakarwa zai auko mana.
Fille de mon peuple, ceins-toi d’un cilice, couvre-toi de cendre; sois en deuil comme d’un fils unique, pousse des plaintes amères, parce que tout d’un coup viendra le dévastateur sur nous.
27 “Na maishe ka mai jarrabawar ƙarfe mutanena ne kuwa ƙarfen, don ka lura ka kuma gwada hanyoyinsu.
Je t’ai établi au milieu de mon peuple comme un fondeur robuste; tu sauras, et tu éprouveras leur voie.
28 Su duka masu taurinkai ne,’yan tawaye, suna yawo suna baza jita-jita. Su tagulla ne da ƙarfe; dukansu lalatattu ne.
Tous ses princes ont dévié, marchant frauduleusement; c’est de l’airain et du fer; tous se sont corrompus.
29 Mazuga yana zuga da ƙarfi don yă ƙone dalma da wuta, amma tacewa yana tafiya a banza; ba a fitar da mugaye.
Le soufflet a manqué, dans le feu s’est consumé le plomb; en vain le fondeur les a mis dans le fourneau; car leurs méchancetés n’ont pas été consumées.
30 Ana ce da su azurfar da aka ƙi, gama Ubangiji ya ƙi su.”
Appelez-les un argent réprouvé, parce que le Seigneur les a rejetés.

< Irmiya 6 >