< Irmiya 6 >

1 “Ku gudu neman mafaka, mutanen Benyamin! Ku gudu daga Urushalima! Ku busa ƙaho a Tekowa! Ku ba da alama a Bet-Hakkerem! Gama masifa tana zuwa daga arewa, mummunar hallaka ce kuwa.
« Fuyez en sécurité, enfants de Benjamin, hors du centre de Jérusalem! Sonnez de la trompette à Tekoa et élevez un signal sur Beth Haccherem, car le malheur vient du nord avec une grande destruction.
2 Zan hallaka Diyar Sihiyona, kyakkyawa da kuma mai laulayi.
J'extermine la belle et la délicate, la fille de Sion.
3 Makiyaya da garkunansu za su taso mata; za su kafa tentunansu kewaye da ita, kowanne yana lura da sashensa.”
Des bergers avec leurs troupeaux viendront vers elle. Ils dresseront leurs tentes tout autour d'elle. Ils feront paître chacun à sa place. »
4 “Mu shirya don yaƙi da ita! Ku tashi, bari mu fāɗa mata da tsakar rana! Amma, kaito, rana tana fāɗuwa, inuwar yamma kuwa sai ƙaran tsawo take.
« Préparez la guerre contre elle! Levez-vous! Montons à midi. Malheur à nous! Car le jour décline, car les ombres du soir s'étendent.
5 Saboda haka ku tashi, bari mu fāɗa mata da dare mu rurrushe kagaranta!”
Levez-vous! Montons de nuit, et détruisons ses palais. »
6 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ku sassare itatuwan ku tula ƙasa kewaye da Urushalima. Dole a hukunta wannan birni; saboda ya cika da zalunci.
Car Yahvé des armées a dit: « Abattez des arbres, et élevez un monticule contre Jérusalem. C'est la ville qu'il faut visiter. Elle est remplie d'oppression au-dedans d'elle-même.
7 Kamar yadda rijiya takan ba da ruwarta, haka birnin yake da muguntarsa. Ana jin labarin rikici da hallaka a cikinsa; ciwonsa da mikinsa kullum suna a gabana.
Comme un puits produit ses eaux, ainsi elle produit sa méchanceté. On entend en elle la violence et la destruction. La maladie et les plaies sont continuellement devant moi.
8 Ki ji gargaɗi, ya Urushalima, ko kuwa in juya daga gare ki in mai da ƙasarki kufai don kada wani ya zauna a cikinta.”
Sois instruite, Jérusalem, de peur que mon âme ne se sépare de toi, que je ne fasse de toi une désolation, une terre inhabitée. »
9 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Bari su yi kalan raguwar Isra’ila a yi kalan sarai yadda ake yi wa inabi; ka sāke miƙa hannunka a kan rassan, kamar mai tattara inabi.”
Yahvé des Armées dit: « Ils glaneront à fond le reste d'Israël comme une vigne. Tourne à nouveau ta main comme un vendangeur vers les paniers. »
10 Ga wa zan yi magana in kuma gargaɗar? Wa zai saurare ni? Kunnuwansu sun toshe don kada su ji. Maganar Ubangiji ta zama abin zargi a gare su; ba sa jin daɗinta.
A qui devrais-je parler et rendre témoignage, pour qu'ils entendent? Voici, leur oreille est incirconcise, et ils ne peuvent pas écouter. Voici, la parole de Yahvé est devenue pour eux un opprobre. Ils n'y trouvent aucun plaisir.
11 Amma ina cike da fushin Ubangiji, kuma ba na iya kannewa. “Ka kwararo shi a kan yara a titi da kuma a kan samarin da suka tattaru; za a kama miji da mata a cikinsa, tsofaffi da suka tsufa tukub.
C'est pourquoi je suis plein de la colère de Yahvé. Je suis fatigué de la retenir. « Versez-le sur les enfants dans la rue, et sur le rassemblement de jeunes hommes; car même le mari avec sa femme sera pris, le vieillard avec celui qui est plein de jours.
12 Za a ba da gidajensu ga waɗansu, tare da gonakinsu da matansu, sa’ad da na miƙa hannuna gāba da waɗanda suke zama a ƙasar,” in ji Ubangiji.
Leurs maisons seront confiées à d'autres, leurs champs et leurs femmes ensemble; car j'étendrai ma main sur les habitants du pays, dit Yahvé. »
13 “Daga ƙarami zuwa babba, dukansu masu haɗama ne don riba; har da annabawa da firistoci, dukansu suna aikata rashin gaskiya.
« Car, depuis le plus petit jusqu'au plus grand, tous sont livrés à la convoitise. Depuis le prophète jusqu'au prêtre, tout le monde fait du faux.
14 Sukan ɗaura mikin mutanena sai ka ce mikin ba shi da matsala. Suna cewa, ‘Lafiya, Lafiya,’ alhali kuwa ba lafiya.
Ils ont aussi guéri superficiellement la blessure de mon peuple, en disant « Paix, paix! » alors qu'il n'y a pas de paix.
15 Suna jin kunyar halinsu na banƙyama? A’a, ba sa jin kunya sam; ba su ma san yadda za su soke kai ba. Saboda haka za su fāɗi tare da fāɗaɗɗu; za a hamɓarar da su sa’ad da na hukunta su,” in ji Ubangiji.
N'ont-ils pas eu honte quand ils ont commis des abominations? Non, ils n'avaient pas du tout honte, ils ne pouvaient pas non plus rougir. Ils tomberont donc parmi ceux qui tombent. Quand je les visiterai, ils seront renversés », dit Yahvé.
16 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku tsaya kan hanyoyi, ku duba; ku nemi hanyoyin dā, ku tambaya inda hanyar mai kyau take, ku yi tafiya a kanta, za ku kuwa sami hutu wa rayukanku. Amma kun ce, ‘Ba za mu bi ta ba.’
Yahvé dit: « Tenez-vous sur les chemins et regardez, et demandez les anciens sentiers: « Où est le bon chemin? » et marchez-y, et vous trouverez le repos de vos âmes. Mais ils ont dit: « Nous n'y marcherons pas.
17 Na naɗa muku masu tsaro a kanku na kuma ce, ‘Ku saurari karan ƙaho!’ Amma kuka ce, ‘Ba za mu saurara ba.’
J'ai placé sur vous des sentinelles, en disant: « Écoutez le son de la trompette. Mais ils ont dit: « Nous n'écouterons pas ».
18 Saboda haka ku, ya al’ummai; ku lura Ya shaidu, abin da zai faru da su.
C'est pourquoi, nations, écoutez et sachez, assemblée, ce qui est au milieu d'elles.
19 Ki ji, ya duniya. Zan kawo masifa a kan waɗannan mutane, sakayyar ƙulle-ƙullensu, domin ba su saurari maganata ba suka kuma ƙi dokata.
Écoute, terre! Voici, je vais faire venir sur ce peuple le malheur, le fruit de ses pensées, parce qu'il n'a pas écouté mes paroles, et qu'il a rejeté ma loi.
20 Babu riba a kawo mini turare daga Sheba ko rake mai zaƙi daga ƙasa mai nisa? Ba zan karɓi hadayunku na ƙonawa ba; ba na jin daɗin sadakokinku.”
A quoi sert l'encens de Saba qui vient à moi, et le roseau d'un pays lointain? Vos holocaustes ne sont pas agréables, et vos sacrifices ne me plaisent pas. »
21 Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, “Zan sa abin tuntuɓe gaban mutanena. Mahaifi da’ya’yansa maza za su yi tuntuɓe a kan juna; maƙwabci da abokansa za su hallaka.”
C'est pourquoi Yahvé dit: « Voici que je vais mettre des pierres d'achoppement devant ce peuple. Les pères et les fils ensemble trébucheront contre eux. Le voisin et son ami périront. »
22 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Duba, sojoji suna zuwa daga ƙasar arewa; babbar al’umma ce ta yunƙuro daga iyakokin duniya.
Yahvé dit: « Voici qu'un peuple vient du pays du nord. Une grande nation se lève des extrémités de la terre.
23 Suna riƙe da baka da māshi; mugaye ne kuma marasa tausayi. Motsinsu kamar ƙugin teku ne yayinda suke hawan dawakansu; suna zuwa a jere kamar wanda ya yi shirin yaƙi don su fāɗa miki, ya Diyar Sihiyona.”
Ils s'emparent de l'arc et de la lance. Ils sont cruels et sans pitié. Leur voix gronde comme la mer, ils montent à cheval, tous se rangent en bataille, comme un homme, contre toi, fille de Sion. »
24 Mun ji labari a kansu, hannuwanmu kuwa suka yi laƙwas. Azaba ta kama mu, zafi kamar na mace mai naƙuda.
Nous avons entendu son rapport. Nos mains se sont affaiblies. L'angoisse s'est emparée de nous, et les douleurs comme celles d'une femme en travail.
25 Kada ku fita zuwa gonaki ko ku yi tafiya a hanyoyi, gama abokin gāba yana da takobi, kuma akwai razana ko’ina.
Ne sortez pas dans les champs et ne vous promenez pas sur le chemin, car l'épée de l'ennemi et la terreur sont de tous côtés.
26 Ya mutanena, ku sanya tufafin makoki ku yi birgima a toka; ku yi kuka mai zafi irin wanda akan yi wa ɗa tilo, gama nan da nan mai hallakarwa zai auko mana.
Fille de mon peuple, revêts-toi d'un sac, et roule-toi dans la cendre! Porte le deuil, comme pour un fils unique, des lamentations très amères, car le destructeur va venir soudainement sur nous.
27 “Na maishe ka mai jarrabawar ƙarfe mutanena ne kuwa ƙarfen, don ka lura ka kuma gwada hanyoyinsu.
« J'ai fait de toi un testeur de métaux et une forteresse au milieu de mon peuple, pour que tu connaisses et éprouves leur voie.
28 Su duka masu taurinkai ne,’yan tawaye, suna yawo suna baza jita-jita. Su tagulla ne da ƙarfe; dukansu lalatattu ne.
Ils sont tous de grands rebelles, qui vont et viennent pour calomnier. Ils sont de bronze et de fer. Ils sont tous corrompus.
29 Mazuga yana zuga da ƙarfi don yă ƙone dalma da wuta, amma tacewa yana tafiya a banza; ba a fitar da mugaye.
Le soufflet souffle avec violence, Le plomb se consume dans le feu. Le plomb se consume dans le feu. C'est en vain qu'on les affine, car les méchants ne sont pas arrachés.
30 Ana ce da su azurfar da aka ƙi, gama Ubangiji ya ƙi su.”
Les hommes les appelleront de l'argent rejeté, parce que Yahvé les a rejetés. »

< Irmiya 6 >