< Irmiya 6 >
1 “Ku gudu neman mafaka, mutanen Benyamin! Ku gudu daga Urushalima! Ku busa ƙaho a Tekowa! Ku ba da alama a Bet-Hakkerem! Gama masifa tana zuwa daga arewa, mummunar hallaka ce kuwa.
Flee, O ye sons of Benjamin, from Jerusalem, And blow ye the trumpet in Tekoa, And lift up the banner in Beth-haccerem! For evil threateneth from the North; Yea, great destruction.
2 Zan hallaka Diyar Sihiyona, kyakkyawa da kuma mai laulayi.
O daughter of Zion, the comely and delicate, Thee have I doomed to destruction!
3 Makiyaya da garkunansu za su taso mata; za su kafa tentunansu kewaye da ita, kowanne yana lura da sashensa.”
The shepherds with their flocks shall come to her; They shall pitch their tents against her round about; They shall feed each one in his place.
4 “Mu shirya don yaƙi da ita! Ku tashi, bari mu fāɗa mata da tsakar rana! Amma, kaito, rana tana fāɗuwa, inuwar yamma kuwa sai ƙaran tsawo take.
“Prepare ye war against her, [[shall they say; ]] Arise, and let us go up at noonday; Alas for us! for the day goeth away, For the shadows of evening are lengthened.
5 Saboda haka ku tashi, bari mu fāɗa mata da dare mu rurrushe kagaranta!”
Arise, and let us go up by night, And let us destroy her palaces!”
6 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ku sassare itatuwan ku tula ƙasa kewaye da Urushalima. Dole a hukunta wannan birni; saboda ya cika da zalunci.
For thus saith Jehovah of hosts: Hew ye down trees, And raise a mound against Jerusalem! She is a city to be punished; She is full of oppression.
7 Kamar yadda rijiya takan ba da ruwarta, haka birnin yake da muguntarsa. Ana jin labarin rikici da hallaka a cikinsa; ciwonsa da mikinsa kullum suna a gabana.
As a fountain sendeth forth its waters, So she sendeth forth her wickedness. Violence and rapine are heard within her; Before me continually are bruises and wounds.
8 Ki ji gargaɗi, ya Urushalima, ko kuwa in juya daga gare ki in mai da ƙasarki kufai don kada wani ya zauna a cikinta.”
Receive correction, O Jerusalem, Lest my soul be alienated from thee, Lest I make thee a desolation, A land not inhabited!
9 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Bari su yi kalan raguwar Isra’ila a yi kalan sarai yadda ake yi wa inabi; ka sāke miƙa hannunka a kan rassan, kamar mai tattara inabi.”
Thus saith Jehovah of hosts: They shall thoroughly glean the remnant of Israel as a vine; Turn thy hand like a grape-gatherer again to the baskets!
10 Ga wa zan yi magana in kuma gargaɗar? Wa zai saurare ni? Kunnuwansu sun toshe don kada su ji. Maganar Ubangiji ta zama abin zargi a gare su; ba sa jin daɗinta.
To whom shall I speak? To whom give warning, so that they shall hear? Behold, their ear is uncircumcised, so that they cannot hearken; Behold, the word of Jehovah is to them a derision; They have no delight in it.
11 Amma ina cike da fushin Ubangiji, kuma ba na iya kannewa. “Ka kwararo shi a kan yara a titi da kuma a kan samarin da suka tattaru; za a kama miji da mata a cikinsa, tsofaffi da suka tsufa tukub.
Therefore I am full of the fury of Jehovah; I am weary of holding it; I will pour it out alike upon the children in the street, And upon the assembly of the young men. Yea, also the husband with the wife shall be taken, The old man, and he that is full of days.
12 Za a ba da gidajensu ga waɗansu, tare da gonakinsu da matansu, sa’ad da na miƙa hannuna gāba da waɗanda suke zama a ƙasar,” in ji Ubangiji.
Their houses also shall be transferred to others, Their fields and their wives together, For I will stretch out my hand over the inhabitants of the land, saith Jehovah.
13 “Daga ƙarami zuwa babba, dukansu masu haɗama ne don riba; har da annabawa da firistoci, dukansu suna aikata rashin gaskiya.
For from the least of them even to the greatest, Every one is greedy of gain; Prophet and priest alike, Every one of them practiseth deceit.
14 Sukan ɗaura mikin mutanena sai ka ce mikin ba shi da matsala. Suna cewa, ‘Lafiya, Lafiya,’ alhali kuwa ba lafiya.
They heal the wound of my people slightly, Saying, Peace! peace! when there is no peace.
15 Suna jin kunyar halinsu na banƙyama? A’a, ba sa jin kunya sam; ba su ma san yadda za su soke kai ba. Saboda haka za su fāɗi tare da fāɗaɗɗu; za a hamɓarar da su sa’ad da na hukunta su,” in ji Ubangiji.
Are they ashamed that they have done abominable things? Nay, they are not at all ashamed; They know not how to blush; Therefore shall they fall with them that fall; At the time when I punish them, They shall be cast down, saith Jehovah.
16 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku tsaya kan hanyoyi, ku duba; ku nemi hanyoyin dā, ku tambaya inda hanyar mai kyau take, ku yi tafiya a kanta, za ku kuwa sami hutu wa rayukanku. Amma kun ce, ‘Ba za mu bi ta ba.’
Thus saith Jehovah: Stand ye upon the ways and look; And ask for the old paths, “Where is the good way?” Walk ye in it, and ye shall find for yourselves rest. But they say, We will not walk in it.
17 Na naɗa muku masu tsaro a kanku na kuma ce, ‘Ku saurari karan ƙaho!’ Amma kuka ce, ‘Ba za mu saurara ba.’
I have also set watchmen over you, [[saying, ]] Hearken to the sound of the trumpet! But they say, We will not hearken.
18 Saboda haka ku, ya al’ummai; ku lura Ya shaidu, abin da zai faru da su.
Therefore hear, O ye nations, And know, ye assembled multitude, What shall come upon them!
19 Ki ji, ya duniya. Zan kawo masifa a kan waɗannan mutane, sakayyar ƙulle-ƙullensu, domin ba su saurari maganata ba suka kuma ƙi dokata.
Hear thou, O earth! Behold, I bring evil upon this people, The fruit of their devices; Because they have not hearkened to my words, And have even rejected my law.
20 Babu riba a kawo mini turare daga Sheba ko rake mai zaƙi daga ƙasa mai nisa? Ba zan karɓi hadayunku na ƙonawa ba; ba na jin daɗin sadakokinku.”
To what purpose is incense brought to me from Sheba, And the sweet-smelling reed from a far country? Your burnt-offerings are not acceptable, Nor are your sacrifices sweet to me.
21 Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, “Zan sa abin tuntuɓe gaban mutanena. Mahaifi da’ya’yansa maza za su yi tuntuɓe a kan juna; maƙwabci da abokansa za su hallaka.”
Therefore thus saith Jehovah: Behold, I lay stumbling-blocks before this people, Upon which fathers and sons shall stumble together, The neighbor and his friend, and shall perish.
22 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Duba, sojoji suna zuwa daga ƙasar arewa; babbar al’umma ce ta yunƙuro daga iyakokin duniya.
Thus saith Jehovah: Behold, a people cometh from the land of the North; A great nation riseth up from the extremities of the earth.
23 Suna riƙe da baka da māshi; mugaye ne kuma marasa tausayi. Motsinsu kamar ƙugin teku ne yayinda suke hawan dawakansu; suna zuwa a jere kamar wanda ya yi shirin yaƙi don su fāɗa miki, ya Diyar Sihiyona.”
They bear the bow and the spear; They are cruel and show no mercy; Their voice roareth like the sea; And upon horses do they ride, Arrayed as a warrior against thee, O daughter of Zion.
24 Mun ji labari a kansu, hannuwanmu kuwa suka yi laƙwas. Azaba ta kama mu, zafi kamar na mace mai naƙuda.
We have heard the report thereof; Our hands lose their strength; Anguish hath taken hold of us, Pain, as of a woman in travail.
25 Kada ku fita zuwa gonaki ko ku yi tafiya a hanyoyi, gama abokin gāba yana da takobi, kuma akwai razana ko’ina.
Go not forth into the field, Nor walk ye in the highway! For the sword of the enemy And terror are on every side.
26 Ya mutanena, ku sanya tufafin makoki ku yi birgima a toka; ku yi kuka mai zafi irin wanda akan yi wa ɗa tilo, gama nan da nan mai hallakarwa zai auko mana.
O daughter of my people, gird thee with sackcloth, And roll thyself in ashes! Make thee mourning as for an only son, Most bitter lamentation! For suddenly shall the spoiler come upon us.
27 “Na maishe ka mai jarrabawar ƙarfe mutanena ne kuwa ƙarfen, don ka lura ka kuma gwada hanyoyinsu.
I have set thee, like a tower, for an assayer among my people, That thou mayst know and try their way.
28 Su duka masu taurinkai ne,’yan tawaye, suna yawo suna baza jita-jita. Su tagulla ne da ƙarfe; dukansu lalatattu ne.
They are all stubborn revolters, Slanderers are they, brass and iron; They are all corrupt.
29 Mazuga yana zuga da ƙarfi don yă ƙone dalma da wuta, amma tacewa yana tafiya a banza; ba a fitar da mugaye.
The bellows burn; The lead is consumed by the fire; The refiner hath melted in vain, For the bad are not separated.
30 Ana ce da su azurfar da aka ƙi, gama Ubangiji ya ƙi su.”
Rejected silver shall men call them, Because Jehovah hath rejected them.