< Irmiya 52 >
1 Zedekiya yana da shekara ashirin da ɗaya sa’ad da ya ci sarauta. Ya yi mulki a Urushalima shekara goma sha ɗaya. Sunan uwarsa Hamutal,’yar Irmiya, wanda yake zaune a Libna.
Sedekíja je bil star enaindvajset let, ko je začel kraljevati in v Jeruzalemu je kraljeval enajst let. Ime njegove matere je bilo Hamutála, hči Jeremija iz Libne.
2 Sarki Zedekiya ya aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji kamar yadda Sarki Yehohiyakim ya yi.
Počel je to, kar je bilo zlo v Gospodovih očeh, glede na vse, kar je storil Jojakím.
3 Al’amarin ya zama da muni ƙwarai a cikin Isra’ila da Yahuda, don haka Ubangiji ya husata har ya sa aka kai mutanen bautar talala. Zedekiya kuwa ya tayar wa Sarkin Babilon.
Kajti zaradi Gospodove jeze se je to zgodilo v Jeruzalemu in v Judu, dokler jih ni zavrgel izpred svoje prisotnosti, da se je Sedekíja uprl zoper babilonskega kralja.
4 A kan rana ta goma ga watan goma, a shekara ta tara ta mulkin Zedekiya, Sarkin Yahuda, sai Nebukadnezzar, Sarkin Babilon, ya zo yaƙi da Urushalima tare da dukan sojojinsa. Suka kewaye ta da yaƙi, suka gina katanga kewaye da ita.
Pripetilo se je v devetem letu njegovega kraljevanja, v desetem mesecu, na deseti dan meseca, da je prišel babilonski kralj Nebukadnezar, on in vsa njegova vojska, zoper [prestolnico] Jeruzalem in se utaboril zoper njo in zoper njo naokoli zgradil trdnjave.
5 An kewaye birnin da yaƙi har shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya.
Tako je bilo mesto oblegano do enajstega leta kralja Sedekíja.
6 A kan rana ta tara a watan huɗu na wannan shekara, yunwa ta tsananta ƙwarai a birnin. Mutane suka rasa abin da za su ci.
In v četrtem mesecu, na deveti dan meseca, je bila huda lakota v mestu, tako da ni bilo kruha za ljudstvo dežele.
7 Sai aka huda katangan birnin, sojojin kuwa suka gudu, suka fita daga cikin birnin da dare ta hanyar ƙofar da take tsakanin bango biyu, kusa da gonar sarki, sa’ad da Babiloniyawa suke kewaye da birnin. Sojojin suka nufi wajen Araba.
Potem je bilo mesto predrto in vsi bojevniki so pobegnili in ponoči odšli ven iz mesta, po poti velikih vrat med dvema zidovoma, kar je bilo poleg kraljevega vrta; (torej Kaldejci so bili pri mestu naokoli) in odšli so po poti ravnine.
8 Amma sojojin Babiloniyawa suka runtumi sarki Zedekiya, suka ci masa a filayen Yeriko. Dukan sojoji suka yashe shi.
Toda vojska Kaldejcev je zasledovala kralja in Sedekíja dohitela na ravninah Jerihe; in vsa njegova vojska je bila razkropljena od njega.
9 Da aka kama Zedekiya, sai aka kai shi wurin Sarkin Babilon a Ribla a ƙasar Hamat, a nan ne Sarkin Babilon ya yanke masa shari’a.
Potem so prijeli kralja in ga odvedli gor k babilonskemu kralju v Riblo, v deželo Hamát; kjer je izrekel sodbo nad njim.
10 Sarkin Babilon ya kashe’ya’yan Zedekiya a idonsa. Ya kuma kashe dukan shugabannin Yahuda a Ribla.
Babilonski kralj je Sedekíjeve sinove usmrtil pred njegovimi očmi. Usmrtil je tudi vse Judove prince v Ribli.
11 Sa’an nan ya ƙwaƙule idanun Zedekiya, ya kuma sa masa ƙuƙumi, aka kai shi Babilon inda aka sa shi a kurkuku har ran da ya mutu.
Potem je iztaknil Sedekíjeve oči; in babilonski kralj ga je zvezal v verige in ga odvedel v Babilon in ga vtaknil v ječo do dneva njegove smrti.
12 A kan rana ta goma ga watan biyar a shekara ta goma sha tara ta sarautar Nebukadnezzar, Sarkin Babilon, sai Nebuzaradan shugaban matsara da kuma ɗan majalisar sarki, ya zo Urushalima.
Torej v petem mesecu, na deseti dan meseca, kar je bilo devetnajsto leto babilonskega kralja Nebukadnezarja je prišel Nebuzaradán, poveljnik straže, ki je služil babilonskemu kralju, v Jeruzalem.
13 Sai ya ƙone haikalin Ubangiji, da gidan sarki, da dukan gine-gine masu alfarman da suke Urushalima.
Požgal je Gospodovo hišo, kraljevo hišo, vse jeruzalemske hiše in vse hiše velikih mož je požgal z ognjem.
14 Sojojin Babiloniyawa da suke tare da shugaban matsara, suka rushe dukan katangan Urushalima.
Vsa vojska Kaldejcev, ki je bila s poveljnikom straže, je porušila vse zidove naokoli Jeruzalema.
15 Sa’an nan Nebuzaradan shugaban matsara ya kwashe waɗansu matalauta, da sauran mutane da aka bari a birnin, da waɗanda suka gudu zuwa wurin Sarkin Babilon, da sauran masu sana’a, ya kai su bautar talala a Babilon.
Potem je Nebuzaradán, poveljnik straže, odvedel proč ujetništvo, nekatere izmed revnega ljudstva in preostanek ljudstva, ki je ostalo v mestu in tiste, ki so pobegnili proč, ki so pobegnili k babilonskemu kralju in preostanek množice.
16 Amma ya bar waɗansu matalauta na gaske a ƙasar don su yi aiki a gonakin inabi, da sauran gonaki.
Toda Nebuzaradán, poveljnik straže, je pustil nekatere izmed revnih dežele za obrezovalce trte in za poljedelce.
17 Babiloniyawa kuwa suka farfasa ginshiƙan tagulla, da dakalai, da babbar kwatarniya, waɗanda suke a haikalin Ubangiji. Suka kwashe tagulla duka suka kai Babilon.
Tudi stebre iz brona, ki so bili v Gospodovi hiši in podnožja in bronasto morje, ki je bilo v Gospodovi hiši, so Kaldejci zlomili in ves bron od tega odnesli v Babilon.
18 Suka kwashe tukwanen ƙarfe, da manyan cokula, da hantsuka, da daruna, da tasoshin ƙona turare, da kayayyakin tagulla waɗanda ake amfani da su domin hidimar haikali.
Tudi kotle in lopate in utrinjala in skledice in žlice in vse posode iz brona, s katerimi so služili, so vzeli proč.
19 Suka kuma kwashe ƙananan kwanonin sha, da farantan wuta, da daruna, da tukwane, da alkukai, da tasoshin ƙona turare, da kwanonin miƙa hadayar sha. Duk abin da yake na zinariya da azurfa, shugaban matsara ya kwashe.
In umivalnike in ponve za žerjavico in skledice in kotle in svečnike in žlice in čaše; to, kar je bilo iz zlata, v zlatu in to, kar je bilo iz srebra, v srebru, je vzel proč poveljnik straže.
20 Tagullar da sarki Solomon ya yi wa haikalin Ubangiji da ita, wato, ginshiƙai biyu, da ƙaton kwano mai suna Teku na tagulla, da bijimai goma sha biyu, waɗanda suke ɗauke da kwatarniya, da dakalai, ta fi ƙarfin a auna.
Dva stebra, eno morje in dvanajst bronastih bikov, ki so bili pod podnožji, ki jih je kralj Salomon naredil v Gospodovi hiši: brona vseh teh posod je bilo brez teže.
21 Tsawon kowane ginshiƙi kamu goma sha takwas ne, kewayensa kuwa kamu goma sha biyu ne, kaurinsa kuma huɗu ne. Kowannensu yana da rami a ciki.
In glede stebrov, višina enega stebra je bila osemnajst komolcev; in obdajal ga je okrasni trak dvanajstih komolcev; in njegova debelina je bila štiri prste; bil je votel.
22 A kan kowane ginshiƙi, an yi masa dajiyar tagulla, tsayinta kamu biyar. A bisa kan kowace dajiya akwai raga da siffofin rumman na tagulla kewaye da dajiyar. Ginshiƙi na biyu ma haka yake da siffofin rumman.
Na njem je bil kapitel iz brona; in višina enega kapitela je bila pet komolcev, z mrežo in granatnimi jabolki naokoli na kapitelih, vsi iz brona. Tudi drugi steber in granatna jabolka so bili podobni tem.
23 Akwai siffofin rumman tasa’in da shida da ake gani a gefen. Dukan siffofin rumman da suke a kan ragar kewaye, guda ɗari ne.
In tam je bilo šestindevetdeset granatnih jabolk na eni strani; in vseh granatnih jabolk na mreži je bilo sto naokoli.
24 Shugaban matsara kuma ya ɗauki Serahiya babban firist, da Zefaniya wanda yake biye da babban firist, da mutum uku masu tsaron ƙofar, ya tafi da su.
In poveljnik straže je vzel vélikega duhovnika Serajája in drugega duhovnika Cefanjája in tri čuvaje vrat.
25 Daga cikin birnin kuma ya ɗauki shugaban sojojin, da mutum bakwai’yan majalisar sarki, da magatakardan shugaban sojojin wanda yakan tara sojojin ƙasar, da mutane sittin na ƙasar, waɗanda aka same su a birnin, ya tafi da su.
Iz mesta je vzel tudi evnuha, ki je bil zadolžen za bojevnike in sedem mož izmed njih, ki so bili blizu kraljevi osebi, ki so bili najdeni v mestu; in glavnega pisarja vojske, ki je nabiral ljudstvo dežele; in šestdeset mož izmed ljudstva dežele, ki so bili najdeni v sredi mesta.
26 Nebuzaradan shugaban matsara ya tafi da waɗannan mutane wurin Sarkin Babilon a Ribla,
Tako jih je Nebuzaradán, poveljnik straže, vzel in jih privedel k babilonskemu kralju v Riblo.
27 Sarkin Babilon kuwa ya kashe su a Ribla a ƙasar Hamat. Haka aka tafi da mutanen Yahuda bautar talala, daga ƙasarta.
Babilonski kralj jih je udaril in jih usmrtil v Ribli, v deželi Hamát. Tako je bil Juda ujet odveden proč iz svoje lastne dežele.
28 Wannan shi ne yawan mutanen da Nebukadnezzar ya kai su bauta. A shekara ta bakwai ta sarautarsa, ya tafi da Yahudawa 3,023;
To je ljudstvo, ki ga je Nebukadnezar odvedel proč ujete: v sedmem letu tri tisoč triindvajset Judov;
29 a shekara ta goma sha takwas ta sarautar Nebukadnezzar, ya tafi da Yahudawa daga Urushalima 832;
v osemnajstem letu Nebukadnezarja je iz Jeruzalema odvedel zajetih osemsto dvaintrideset oseb;
30 a shekara ta ashirin da uku ta sarautarsa, Nebuzaradan shugaban matsara ya tafi da Yahudawa 745. Jimillarsu duka 4,600 ne.
v triindvajsetem letu Nebukadnezarja je Nebuzaradán, poveljnik straže, odvedel proč judovske ujetnike, sedemsto petinštirideset oseb. Vseh oseb je bilo štiri tisoč šeststo.
31 A shekarar da Ewil-Merodak ya zama Sarkin Babilon, sai ya nuna wa Yehohiyacin Sarkin Yahuda alheri. Ya fisshe shi daga kurkuku. Wannan ya faru ran ashirin da biyar ga watan goma sha biyu a shekara ta talatin da bakwai bayan da aka kai Yehohiyacin bauta.
Pripetilo se je v sedemintridesetem letu ujetništva Judovega kralja Jojahína, v dvanajstem mesecu, na petindvajseti dan meseca, da je babilonski kralj Evíl Merodáh v prvem letu svojega kraljevanja povzdignil glavo Judovega kralja Jojahína in ga privedel iz ječe.
32 Ewil-Merodak ya nuna wa Yehohiyacin alheri, ya ba shi matsayi na daraja fiye da waɗansu sarakunan da aka kai su bautar talala a Babilon tare da shi.
Prijazno je govoril z njim in njegov prestol postavil nad prestole kraljev, ki so bili z njim v Babilonu.
33 Yehohiyacin ya tuɓe tufafin kurkuku, ya riƙa cin abinci kullum a teburin sarki, har dukan sauran kwanakin ransa.
Spremenil je njegove jetniške obleke in nenehno je jedel kruh pred njim, vse dni svojega življenja.
34 Kowace rana akan ba shi kyauta bisa ga umarnin sarkin Babilon, saboda bukatarsa. Haka aka yi masa har rasuwarsa.
Glede njegove prehrane mu je bil od babilonskega kralja dan nenehen delež hrane, vsak dan obrok do dneva njegove smrti, vse dni njegovega življenja.