< Irmiya 52 >
1 Zedekiya yana da shekara ashirin da ɗaya sa’ad da ya ci sarauta. Ya yi mulki a Urushalima shekara goma sha ɗaya. Sunan uwarsa Hamutal,’yar Irmiya, wanda yake zaune a Libna.
Сущу двадесяти и единому лету Седекии, внегда нача царствовати, и царствова во Иерусалиме единонадесять лет: и имя матери его Амиталь, дщи Иеремиина, от Ловны.
2 Sarki Zedekiya ya aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji kamar yadda Sarki Yehohiyakim ya yi.
И сотвори лукавое пред очима Господнима по всему, елико творяше Иоаким:
3 Al’amarin ya zama da muni ƙwarai a cikin Isra’ila da Yahuda, don haka Ubangiji ya husata har ya sa aka kai mutanen bautar talala. Zedekiya kuwa ya tayar wa Sarkin Babilon.
яко ярость Господня бысть на Иерусалим и на Иуду, дондеже отверже их от лица Своего: и отступи Седекиа от царя Вавилонска.
4 A kan rana ta goma ga watan goma, a shekara ta tara ta mulkin Zedekiya, Sarkin Yahuda, sai Nebukadnezzar, Sarkin Babilon, ya zo yaƙi da Urushalima tare da dukan sojojinsa. Suka kewaye ta da yaƙi, suka gina katanga kewaye da ita.
И бысть в девятое лето царства его, в десятый месяц, в десятый день месяца, прииде Навуходоносор царь Вавилонский и вся сила его на Иерусалим, и облегоша его и сотвориша окрест его острог от четвероуголных камений.
5 An kewaye birnin da yaƙi har shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya.
И бысть во облежении град даже до первагонадесяте лета царства Седекиина.
6 A kan rana ta tara a watan huɗu na wannan shekara, yunwa ta tsananta ƙwarai a birnin. Mutane suka rasa abin da za su ci.
Месяца же четвертаго в девятый день, утвердися глад во граде, и не бяше хлеба людем земли.
7 Sai aka huda katangan birnin, sojojin kuwa suka gudu, suka fita daga cikin birnin da dare ta hanyar ƙofar da take tsakanin bango biyu, kusa da gonar sarki, sa’ad da Babiloniyawa suke kewaye da birnin. Sojojin suka nufi wajen Araba.
И просекоша град, и вси мужие воинстии изыдоша нощию путем врат, иже есть между двема стенама, иже бяше прямо вертограду цареву, Халдее же добываху град окрест лежаще, и отидоша путем в пустыню.
8 Amma sojojin Babiloniyawa suka runtumi sarki Zedekiya, suka ci masa a filayen Yeriko. Dukan sojoji suka yashe shi.
И погна сила Халдейска вслед царя и постиже его об ону страну Иерихона, и вси отроцы его разсыпашася от него.
9 Da aka kama Zedekiya, sai aka kai shi wurin Sarkin Babilon a Ribla a ƙasar Hamat, a nan ne Sarkin Babilon ya yanke masa shari’a.
И яша царя и приведоша и ко царю Вавилонскому в Девлаф, иже есть в земли Емаф, и глагола ему с судом.
10 Sarkin Babilon ya kashe’ya’yan Zedekiya a idonsa. Ya kuma kashe dukan shugabannin Yahuda a Ribla.
И изсече царь Вавилонский сыны Седекиины пред очима его, и вся князи Иудины изсече в Девлафе.
11 Sa’an nan ya ƙwaƙule idanun Zedekiya, ya kuma sa masa ƙuƙumi, aka kai shi Babilon inda aka sa shi a kurkuku har ran da ya mutu.
Очи же Седекии изят, и связа его оковами, и приведе его царь Вавилонский в Вавилон и вдаде его в дом жерновный до дне, в оньже умре.
12 A kan rana ta goma ga watan biyar a shekara ta goma sha tara ta sarautar Nebukadnezzar, Sarkin Babilon, sai Nebuzaradan shugaban matsara da kuma ɗan majalisar sarki, ya zo Urushalima.
В десятый же день пятаго месяца (лето сие девятоенадесять Навуходоносору царю Вавилонску) прииде Навузардан архимагир, стоящь пред лицем царя Вавилонска, во Иерусалим,
13 Sai ya ƙone haikalin Ubangiji, da gidan sarki, da dukan gine-gine masu alfarman da suke Urushalima.
и сожже храм Господень и дом царев, и вся домы градския и всяк дом велик сожже огнем,
14 Sojojin Babiloniyawa da suke tare da shugaban matsara, suka rushe dukan katangan Urushalima.
и всяку стену Иерусалимлю окрест разори сила Халдейска, яже бяше со архимагиром.
15 Sa’an nan Nebuzaradan shugaban matsara ya kwashe waɗansu matalauta, da sauran mutane da aka bari a birnin, da waɗanda suka gudu zuwa wurin Sarkin Babilon, da sauran masu sana’a, ya kai su bautar talala a Babilon.
И от убогих людий, и останок людий, и оставшихся во граде и избегших, иже убежаша ко царю Вавилонску, и прочий народ пресели Навузардан воевода:
16 Amma ya bar waɗansu matalauta na gaske a ƙasar don su yi aiki a gonakin inabi, da sauran gonaki.
прочиих же остави людий убогих в делатели винограда и земледелцев.
17 Babiloniyawa kuwa suka farfasa ginshiƙan tagulla, da dakalai, da babbar kwatarniya, waɗanda suke a haikalin Ubangiji. Suka kwashe tagulla duka suka kai Babilon.
Столпы же медяныя, иже во храме Господни, и подставы, и море медяное, еже во храме Господни, сокрушиша Халдее, и взяша медь их, и отнесоша в Вавилон:
18 Suka kwashe tukwanen ƙarfe, da manyan cokula, da hantsuka, da daruna, da tasoshin ƙona turare, da kayayyakin tagulla waɗanda ake amfani da su domin hidimar haikali.
и венец и чашы, и вилицы и вся сосуды медяныя, в нихже служаху,
19 Suka kuma kwashe ƙananan kwanonin sha, da farantan wuta, da daruna, da tukwane, da alkukai, da tasoshin ƙona turare, da kwanonin miƙa hadayar sha. Duk abin da yake na zinariya da azurfa, shugaban matsara ya kwashe.
и фимиамники и чашы, и умывалницы и свещники, и кадилницы и чашицы, яже бяху златая и яже бяху сребряная, взя архимагир.
20 Tagullar da sarki Solomon ya yi wa haikalin Ubangiji da ita, wato, ginshiƙai biyu, da ƙaton kwano mai suna Teku na tagulla, da bijimai goma sha biyu, waɗanda suke ɗauke da kwatarniya, da dakalai, ta fi ƙarfin a auna.
И столпа два и море едино, и телцев дванадесять медяных под морем, яже сотвори царь Соломон во храме Господни, не бе веса меди сосуд тех.
21 Tsawon kowane ginshiƙi kamu goma sha takwas ne, kewayensa kuwa kamu goma sha biyu ne, kaurinsa kuma huɗu ne. Kowannensu yana da rami a ciki.
Столп же кийждо осминадесяти лактей бе в высоту, вервь же дванадесяти лактей окрест его обдержаше, и толстота его четырех перст окрест,
22 A kan kowane ginshiƙi, an yi masa dajiyar tagulla, tsayinta kamu biyar. A bisa kan kowace dajiya akwai raga da siffofin rumman na tagulla kewaye da dajiyar. Ginshiƙi na biyu ma haka yake da siffofin rumman.
и глава на них медяна, пять лакот высота главы единыя, и мрежа, и шипки на венце окрест, все бяше медяно: такожде бысть и вторый столп.
23 Akwai siffofin rumman tasa’in da shida da ake gani a gefen. Dukan siffofin rumman da suke a kan ragar kewaye, guda ɗari ne.
И бяше шипков девятьдесят и шесть едина страна, и бяше всех шипков над мрежею окрест сто.
24 Shugaban matsara kuma ya ɗauki Serahiya babban firist, da Zefaniya wanda yake biye da babban firist, da mutum uku masu tsaron ƙofar, ya tafi da su.
И взя архимагир Сареа жерца старейшаго и жерца Софонию втораго и триех стрегущих путь.
25 Daga cikin birnin kuma ya ɗauki shugaban sojojin, da mutum bakwai’yan majalisar sarki, da magatakardan shugaban sojojin wanda yakan tara sojojin ƙasar, da mutane sittin na ƙasar, waɗanda aka same su a birnin, ya tafi da su.
И от града взя каженика единаго, иже бе приставник людий воинских, и седмь мужей нарочитых, иже пред лицем царевым обретошася во граде, и книгочия сил учащаго людий земли, и шестьдесят мужей от людий земли, иже обретошася среде града:
26 Nebuzaradan shugaban matsara ya tafi da waɗannan mutane wurin Sarkin Babilon a Ribla,
и взя их Навузардан архимагир и приведе я ко царю Вавилонску в Девлаф.
27 Sarkin Babilon kuwa ya kashe su a Ribla a ƙasar Hamat. Haka aka tafi da mutanen Yahuda bautar talala, daga ƙasarta.
И изби я царь Вавилонский в Девлафе в земли Емаф: и преселен бысть Иуда от земли своея.
28 Wannan shi ne yawan mutanen da Nebukadnezzar ya kai su bauta. A shekara ta bakwai ta sarautarsa, ya tafi da Yahudawa 3,023;
Сии суть людие, ихже пресели Навуходоносор в седмое лето, Иудеев три тысящы и двадесять и три:
29 a shekara ta goma sha takwas ta sarautar Nebukadnezzar, ya tafi da Yahudawa daga Urushalima 832;
во осмоенадесять лето Навуходоносор из Иерусалима душ осмь сот тридесять и две пресели.
30 a shekara ta ashirin da uku ta sarautarsa, Nebuzaradan shugaban matsara ya tafi da Yahudawa 745. Jimillarsu duka 4,600 ne.
В двадесять третие лето Навуходоносора пресели Навузардан архимагир Иудеев душ седмь сот и четыредесять пять, всех же душ четыре тысящы и шесть сот.
31 A shekarar da Ewil-Merodak ya zama Sarkin Babilon, sai ya nuna wa Yehohiyacin Sarkin Yahuda alheri. Ya fisshe shi daga kurkuku. Wannan ya faru ran ashirin da biyar ga watan goma sha biyu a shekara ta talatin da bakwai bayan da aka kai Yehohiyacin bauta.
И бысть в тридесять седмое лето преселения Иоакима царя Иудина, в двадесять пятый день месяца вторагонадесять, вознесе Евилмеродах царь Вавилонский в первое лето царства своего главу Иоакима царя Иудина, и изведе его из храма, в немже стрежашеся, и глагола ему благая:
32 Ewil-Merodak ya nuna wa Yehohiyacin alheri, ya ba shi matsayi na daraja fiye da waɗansu sarakunan da aka kai su bautar talala a Babilon tare da shi.
и даде престол его выше царей, иже с ним, в Вавилоне,
33 Yehohiyacin ya tuɓe tufafin kurkuku, ya riƙa cin abinci kullum a teburin sarki, har dukan sauran kwanakin ransa.
и измени ризы его темничныя, и ядяше хлеб всегда пред лицем его во вся дни живота своего:
34 Kowace rana akan ba shi kyauta bisa ga umarnin sarkin Babilon, saboda bukatarsa. Haka aka yi masa har rasuwarsa.
и урок ему даяшеся всегда от царя Вавилонска, даже до дне, в оньже умре, во вся дни живота его.