< Irmiya 52 >

1 Zedekiya yana da shekara ashirin da ɗaya sa’ad da ya ci sarauta. Ya yi mulki a Urushalima shekara goma sha ɗaya. Sunan uwarsa Hamutal,’yar Irmiya, wanda yake zaune a Libna.
Sédécias était âgé de vingt et un ans lorsqu’il devint roi, et il régna onze ans à Jérusalem. Sa mère s’appelait Amital, fille de Jérémie, de Lobna.
2 Sarki Zedekiya ya aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji kamar yadda Sarki Yehohiyakim ya yi.
Il fit ce qui est mal aux yeux de Yahweh, imitant tout ce qu’avait fait Joakim.
3 Al’amarin ya zama da muni ƙwarai a cikin Isra’ila da Yahuda, don haka Ubangiji ya husata har ya sa aka kai mutanen bautar talala. Zedekiya kuwa ya tayar wa Sarkin Babilon.
Cela arriva à Jérusalem et en Juda, à cause de la colère de Yahweh, jusqu’à ce qu’il les rejette de devant sa face. Et Sédécias se révolta contre le roi de Babylone.
4 A kan rana ta goma ga watan goma, a shekara ta tara ta mulkin Zedekiya, Sarkin Yahuda, sai Nebukadnezzar, Sarkin Babilon, ya zo yaƙi da Urushalima tare da dukan sojojinsa. Suka kewaye ta da yaƙi, suka gina katanga kewaye da ita.
La neuvième année du règne de Sédécias, le dixième mois, le dixième jour du mois, Nabuchodonosor, roi de Babylone, vint avec toute son armée contre Jérusalem; ils campèrent devant elle et construisirent tout autour des murs d’approche.
5 An kewaye birnin da yaƙi har shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya.
La ville fut assiégée jusqu’à la onzième année du roi Sédécias.
6 A kan rana ta tara a watan huɗu na wannan shekara, yunwa ta tsananta ƙwarai a birnin. Mutane suka rasa abin da za su ci.
Au quatrième mois, le neuvième jour du mois, comme la famine était grande dans la ville, et qu’il n’y avait plus de pain pour le peuple du pays,
7 Sai aka huda katangan birnin, sojojin kuwa suka gudu, suka fita daga cikin birnin da dare ta hanyar ƙofar da take tsakanin bango biyu, kusa da gonar sarki, sa’ad da Babiloniyawa suke kewaye da birnin. Sojojin suka nufi wajen Araba.
une brèche fut faite à la ville, et tous les gens de guerre s’enfuirent et sortirent de la ville pendant la nuit, par la porte entre les deux murs, près du jardin du roi, pendant que les Chaldéens environnaient la ville; et ils prirent le chemin de la plaine.
8 Amma sojojin Babiloniyawa suka runtumi sarki Zedekiya, suka ci masa a filayen Yeriko. Dukan sojoji suka yashe shi.
Mais l’armée des chaldéens poursuivit le roi; ils atteignirent Sédécias dans les plaines de Jéricho, et toute son armée se dispersa loin de lui.
9 Da aka kama Zedekiya, sai aka kai shi wurin Sarkin Babilon a Ribla a ƙasar Hamat, a nan ne Sarkin Babilon ya yanke masa shari’a.
Ayant saisi roi, ils le firent monter vers le roi de Babylone, à Rébla, dans le pays de d’Émath, et il prononça sur lui des sentences.
10 Sarkin Babilon ya kashe’ya’yan Zedekiya a idonsa. Ya kuma kashe dukan shugabannin Yahuda a Ribla.
Le roi de Babylone égorgea les fils de Sédécias sous les yeux de leur père; il égorgea aussi tous les chefs de Juda à Rébla.
11 Sa’an nan ya ƙwaƙule idanun Zedekiya, ya kuma sa masa ƙuƙumi, aka kai shi Babilon inda aka sa shi a kurkuku har ran da ya mutu.
Puis il creva les yeux à Sédécias et le lia avec deux chaînes d’airain; et le roi de Babylone le mena à Babylone, et le tint en prison jusqu’au jour de sa mort.
12 A kan rana ta goma ga watan biyar a shekara ta goma sha tara ta sarautar Nebukadnezzar, Sarkin Babilon, sai Nebuzaradan shugaban matsara da kuma ɗan majalisar sarki, ya zo Urushalima.
Le cinquième mois, le dixième jour du mois, — c’était la dix-neuvième année du règne de Nabuchodonosor, roi de Babylone, — Nabuzardan, capitaine des gardes, qui était ministre du roi de Babylone, vint à Jérusalem.
13 Sai ya ƙone haikalin Ubangiji, da gidan sarki, da dukan gine-gine masu alfarman da suke Urushalima.
Il brûla la maison de Yahweh, la maison du roi, et toutes les maisons de Jérusalem; il livra au feu toutes les grandes maisons.
14 Sojojin Babiloniyawa da suke tare da shugaban matsara, suka rushe dukan katangan Urushalima.
Toute l’armée des chaldéens qui était avec le capitaine des gardes démolit les murailles formant l’enceinte de Jérusalem.
15 Sa’an nan Nebuzaradan shugaban matsara ya kwashe waɗansu matalauta, da sauran mutane da aka bari a birnin, da waɗanda suka gudu zuwa wurin Sarkin Babilon, da sauran masu sana’a, ya kai su bautar talala a Babilon.
Nabuzardan, capitaine des gardes, emmena captifs une partie des plus pauvres du peuple, avec le reste du peuple qui était demeuré dans la ville, les transfuges qui s’étaient rendus au roi de Babylone, et le reste des artisans.
16 Amma ya bar waɗansu matalauta na gaske a ƙasar don su yi aiki a gonakin inabi, da sauran gonaki.
Mais Nabuzardan, capitaine des gardes, laissa comme vignerons et comme laboureurs quelques-uns des pauvres du pays.
17 Babiloniyawa kuwa suka farfasa ginshiƙan tagulla, da dakalai, da babbar kwatarniya, waɗanda suke a haikalin Ubangiji. Suka kwashe tagulla duka suka kai Babilon.
Les Chaldéens brisèrent les colonnes d’airain qui appartenaient à la maison de Yahweh, ainsi que les bases et la mer d’airain qui étaient dans la maison de Yahweh, et ils en emportèrent l’airain à Babylone.
18 Suka kwashe tukwanen ƙarfe, da manyan cokula, da hantsuka, da daruna, da tasoshin ƙona turare, da kayayyakin tagulla waɗanda ake amfani da su domin hidimar haikali.
Ils prirent les pots, les pelles, les couteaux, les tasses, les coupes et tous les ustensiles d’airain avec lesquels on faisait le service.
19 Suka kuma kwashe ƙananan kwanonin sha, da farantan wuta, da daruna, da tukwane, da alkukai, da tasoshin ƙona turare, da kwanonin miƙa hadayar sha. Duk abin da yake na zinariya da azurfa, shugaban matsara ya kwashe.
Le capitaine des gardes prit encore les bassins, les encensoirs, les tasses, les pots, les chandeliers, les cuillers et les urnes, ce qui était d’or et ce qui était d’argent.
20 Tagullar da sarki Solomon ya yi wa haikalin Ubangiji da ita, wato, ginshiƙai biyu, da ƙaton kwano mai suna Teku na tagulla, da bijimai goma sha biyu, waɗanda suke ɗauke da kwatarniya, da dakalai, ta fi ƙarfin a auna.
Quant aux deux colonnes, à la mer et aux douze bœufs d’airain qui étaient dessous, et aux bases que le roi Salomon avait faites dans la maison de Yahweh, il n’y avait pas à peser l’airain de tous ces ustensiles.
21 Tsawon kowane ginshiƙi kamu goma sha takwas ne, kewayensa kuwa kamu goma sha biyu ne, kaurinsa kuma huɗu ne. Kowannensu yana da rami a ciki.
Quant aux colonnes, la hauteur d’une colonne était de dix-huit coudées, et un cordon de douze coudées en mesurait le tour; son épaisseur était de quatre doigts, et elle était creuse.
22 A kan kowane ginshiƙi, an yi masa dajiyar tagulla, tsayinta kamu biyar. A bisa kan kowace dajiya akwai raga da siffofin rumman na tagulla kewaye da dajiyar. Ginshiƙi na biyu ma haka yake da siffofin rumman.
Il y avait au-dessus un chapiteau d’airain, et la hauteur d’un chapiteau était de cinq coudées; et il y avait tout autour du chapiteaux un treillis et des grenades, le tout d’airain. Il en était de même de la seconde colonne; avec les grenades.
23 Akwai siffofin rumman tasa’in da shida da ake gani a gefen. Dukan siffofin rumman da suke a kan ragar kewaye, guda ɗari ne.
Il y avait quatre-vingt-seize grenades sur les faces, et toutes les grenades étaient au nombre de cent sur le treillis, tout autour.
24 Shugaban matsara kuma ya ɗauki Serahiya babban firist, da Zefaniya wanda yake biye da babban firist, da mutum uku masu tsaron ƙofar, ya tafi da su.
Le capitaine des gardes prit Saraïas, le grand-prêtre, Sophonie, prêtre de second ordre, et les trois gardiens de la porte.
25 Daga cikin birnin kuma ya ɗauki shugaban sojojin, da mutum bakwai’yan majalisar sarki, da magatakardan shugaban sojojin wanda yakan tara sojojin ƙasar, da mutane sittin na ƙasar, waɗanda aka same su a birnin, ya tafi da su.
De la ville il prit un officier qui commandait aux gens de guerre, sept hommes faisant partie du conseil privé du roi et qui furent trouvés dans la ville, le secrétaire du chef de l’armée chargé d’enrôler le peuple du pays, et soixante hommes du peuple du pays qui se trouvaient dans la ville.
26 Nebuzaradan shugaban matsara ya tafi da waɗannan mutane wurin Sarkin Babilon a Ribla,
Les ayant pris, Nabuzardan, capitaine des gardes, les conduisit vers le roi de Babylone à Rébla.
27 Sarkin Babilon kuwa ya kashe su a Ribla a ƙasar Hamat. Haka aka tafi da mutanen Yahuda bautar talala, daga ƙasarta.
Et le roi de Babylone les frappa et les fit mourir à Rébla, dans le pays de d’Emath. Ainsi Juda fut emmené captif loin de sa patrie.
28 Wannan shi ne yawan mutanen da Nebukadnezzar ya kai su bauta. A shekara ta bakwai ta sarautarsa, ya tafi da Yahudawa 3,023;
Voici le nombre des hommes que Nabuchodonosor emmena captifs: la septième année, trois mille vingt-trois hommes de Juda;
29 a shekara ta goma sha takwas ta sarautar Nebukadnezzar, ya tafi da Yahudawa daga Urushalima 832;
la dix-huitième année de Nabuchodonosor, huit cent trente-deux personnes de la population de Jérusalem;
30 a shekara ta ashirin da uku ta sarautarsa, Nebuzaradan shugaban matsara ya tafi da Yahudawa 745. Jimillarsu duka 4,600 ne.
la vingt-troisième année de Nabuchodonosor, Nabuzardan, capitaine des gardes, emmena encore captifs sept cent quarante-cinq hommes de Juda; en tout quatre mille six cents personnes.
31 A shekarar da Ewil-Merodak ya zama Sarkin Babilon, sai ya nuna wa Yehohiyacin Sarkin Yahuda alheri. Ya fisshe shi daga kurkuku. Wannan ya faru ran ashirin da biyar ga watan goma sha biyu a shekara ta talatin da bakwai bayan da aka kai Yehohiyacin bauta.
La trente-septième année de la captivité de Joachin, roi de Juda, le douzième mois, le vingt-cinquième jour du mois, Evil-Mérodach, roi de Babylone, en l’année de son avènement, releva la tête de Joachin, roi de Juda, et le fit sortir de prison.
32 Ewil-Merodak ya nuna wa Yehohiyacin alheri, ya ba shi matsayi na daraja fiye da waɗansu sarakunan da aka kai su bautar talala a Babilon tare da shi.
Il lui parla avec bonté et mit son trône au-dessus du trône des rois qui étaient avec lui à Babylone.
33 Yehohiyacin ya tuɓe tufafin kurkuku, ya riƙa cin abinci kullum a teburin sarki, har dukan sauran kwanakin ransa.
Il lui fit changer ses vêtements de prison, et Joachin mangea en sa présence, toujours, tous les jours de sa vie.
34 Kowace rana akan ba shi kyauta bisa ga umarnin sarkin Babilon, saboda bukatarsa. Haka aka yi masa har rasuwarsa.
Quant à son entretien, son entretien perpétuel, le roi de Babylone y pourvut chaque jour, jusqu’au jour de sa mort, tous les jours de sa vie.

< Irmiya 52 >