< Irmiya 52 >
1 Zedekiya yana da shekara ashirin da ɗaya sa’ad da ya ci sarauta. Ya yi mulki a Urushalima shekara goma sha ɗaya. Sunan uwarsa Hamutal,’yar Irmiya, wanda yake zaune a Libna.
Sedechie was a sone of oon and twenti yeer, whanne he bigan to regne, and he regnede enleuene yeer in Jerusalem; and the name of his modir was Amychal, the douyter of Jeremye of Lobna.
2 Sarki Zedekiya ya aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji kamar yadda Sarki Yehohiyakim ya yi.
And he dide yuels bifore the iyen of the Lord, bi alle thingis whiche Joachym hadde do.
3 Al’amarin ya zama da muni ƙwarai a cikin Isra’ila da Yahuda, don haka Ubangiji ya husata har ya sa aka kai mutanen bautar talala. Zedekiya kuwa ya tayar wa Sarkin Babilon.
For the stronge veniaunce of the Lord was in Jerusalem, and in Juda, til he castide hem awey fro his face. And Sedechie yede awei fro the kyng of Babiloyne.
4 A kan rana ta goma ga watan goma, a shekara ta tara ta mulkin Zedekiya, Sarkin Yahuda, sai Nebukadnezzar, Sarkin Babilon, ya zo yaƙi da Urushalima tare da dukan sojojinsa. Suka kewaye ta da yaƙi, suka gina katanga kewaye da ita.
Forsothe it was don in the nynthe yeer of his rewme, in the tenthe monethe, in the tenthe dai of the monethe, Nabugodonosor, the kyng of Babiloyne, cam, he and al his oost, ayens Jerusalem; and thei bisegiden it, and bildiden ayens it strengthis in cumpas.
5 An kewaye birnin da yaƙi har shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya.
And the citee was bisegid, til to the enleuenthe yeer of the rewme of Sedechie.
6 A kan rana ta tara a watan huɗu na wannan shekara, yunwa ta tsananta ƙwarai a birnin. Mutane suka rasa abin da za su ci.
Forsothe in the fourthe monethe, in the nynthe dai of the monethe, hungur helde the citee; and foodis weren not to the puple of the lond.
7 Sai aka huda katangan birnin, sojojin kuwa suka gudu, suka fita daga cikin birnin da dare ta hanyar ƙofar da take tsakanin bango biyu, kusa da gonar sarki, sa’ad da Babiloniyawa suke kewaye da birnin. Sojojin suka nufi wajen Araba.
And the citee was brokun, and alle men werriouris therof fledden; and thei yeden out of the citee in the niyt, bi the weie of the yate, which is bitwixe twei wallis, and ledith to the gardyn of the kyng, while Caldeis bisegiden the citee in cumpas; and thei yeden forth bi the weie that ledith in to desert.
8 Amma sojojin Babiloniyawa suka runtumi sarki Zedekiya, suka ci masa a filayen Yeriko. Dukan sojoji suka yashe shi.
Sotheli the oost of Caldeis pursuede the kyng; and thei token Sedechie in desert, which is bisidis Jerico, and al his felouschipe fledde awei fro hym.
9 Da aka kama Zedekiya, sai aka kai shi wurin Sarkin Babilon a Ribla a ƙasar Hamat, a nan ne Sarkin Babilon ya yanke masa shari’a.
And whanne thei hadden take the kyng, thei brouyten hym to the kyng of Babiloyne in Reblatha, which is in the lond of Emath; and the kyng of Babiloyne spak domes to hym.
10 Sarkin Babilon ya kashe’ya’yan Zedekiya a idonsa. Ya kuma kashe dukan shugabannin Yahuda a Ribla.
And the kyng of Babiloyne stranglide the sones of Sedechie bifore hise iyen; but also he killide alle the princes of Juda in Rablatha.
11 Sa’an nan ya ƙwaƙule idanun Zedekiya, ya kuma sa masa ƙuƙumi, aka kai shi Babilon inda aka sa shi a kurkuku har ran da ya mutu.
And he puttide out the iyen of Sedechie, and boond hym in stockis; and the kyng of Babiloyne brouyte hym in to Babiloyne, and puttide hym in the hous of prisoun, til to the dai of his deth.
12 A kan rana ta goma ga watan biyar a shekara ta goma sha tara ta sarautar Nebukadnezzar, Sarkin Babilon, sai Nebuzaradan shugaban matsara da kuma ɗan majalisar sarki, ya zo Urushalima.
Forsothe in the nynthe monethe, in the tenthe dai of the monethe, thilke is the nyntenthe yeer of the kyng of Babiloyne, Nabusardan, the prince of chyualrie, that stood bifore the kyng of Babiloyne, cam in to Jerusalem.
13 Sai ya ƙone haikalin Ubangiji, da gidan sarki, da dukan gine-gine masu alfarman da suke Urushalima.
And he brente the hous of the Lord, and the hous of the kyng, and alle the housis of Jerusalem; and he brente with fier ech greet hous.
14 Sojojin Babiloniyawa da suke tare da shugaban matsara, suka rushe dukan katangan Urushalima.
And al the ost of Caldeis, that was with the maistir of chyualrie, distriede al the wal of Jerusalem bi cumpas.
15 Sa’an nan Nebuzaradan shugaban matsara ya kwashe waɗansu matalauta, da sauran mutane da aka bari a birnin, da waɗanda suka gudu zuwa wurin Sarkin Babilon, da sauran masu sana’a, ya kai su bautar talala a Babilon.
Sotheli Nabusardan, the prince of chyualrie, translatide of the pore men of the puple, and of the residue comyn puple, that was left in the citee, and of the fleeris ouer, that fledden ouer to the kyng of Babiloyne; and he translatide other men of the multitude.
16 Amma ya bar waɗansu matalauta na gaske a ƙasar don su yi aiki a gonakin inabi, da sauran gonaki.
But Nabusardan, the prince of chyualrie, lefte of the pore men of the lond vyne tilers, and erthe tilers.
17 Babiloniyawa kuwa suka farfasa ginshiƙan tagulla, da dakalai, da babbar kwatarniya, waɗanda suke a haikalin Ubangiji. Suka kwashe tagulla duka suka kai Babilon.
Also Caldeis brakun the brasun pilers, that weren in the hous of the Lord, and the foundementis, and the brasun waischyng vessel, that was in the hous of the Lord; and thei token al the metal of tho in to Babiloyne.
18 Suka kwashe tukwanen ƙarfe, da manyan cokula, da hantsuka, da daruna, da tasoshin ƙona turare, da kayayyakin tagulla waɗanda ake amfani da su domin hidimar haikali.
And thei tokun cawdruns, and fleischokis, and sautrees, and violis, and morteris, and alle brasun vessels, that weren in seruyce;
19 Suka kuma kwashe ƙananan kwanonin sha, da farantan wuta, da daruna, da tukwane, da alkukai, da tasoshin ƙona turare, da kwanonin miƙa hadayar sha. Duk abin da yake na zinariya da azurfa, shugaban matsara ya kwashe.
thei token also `watir pottis, and vessels of encense, and pottis, and basyns, and candilstikis, and morters, and litle cuppis; hou manye euere goldun, goldun, and hou manye euere siluerne, siluerne.
20 Tagullar da sarki Solomon ya yi wa haikalin Ubangiji da ita, wato, ginshiƙai biyu, da ƙaton kwano mai suna Teku na tagulla, da bijimai goma sha biyu, waɗanda suke ɗauke da kwatarniya, da dakalai, ta fi ƙarfin a auna.
The maister of chyualrie took twei pilers, and o waischyng vessel, and twelue brasun caluys, that weren vndur the foundementis, whiche kyng Salomon hadde maad in the hous of the Lord. No weiyte was of the metal of alle these vessels.
21 Tsawon kowane ginshiƙi kamu goma sha takwas ne, kewayensa kuwa kamu goma sha biyu ne, kaurinsa kuma huɗu ne. Kowannensu yana da rami a ciki.
Forsothe of the pilers, eiytene cubitis of heiythe weren in o piler, and a roop of twelue cubitis cumpasside it; certis the thickenesse therof was of foure fyngris, and was holowe withynne.
22 A kan kowane ginshiƙi, an yi masa dajiyar tagulla, tsayinta kamu biyar. A bisa kan kowace dajiya akwai raga da siffofin rumman na tagulla kewaye da dajiyar. Ginshiƙi na biyu ma haka yake da siffofin rumman.
And brasun pomels weren on euer either; and the heiythe of a pomel was of fyue cubitis; and werkis lijk nettis and pumgranatis weren on the coroun `in cumpas.
23 Akwai siffofin rumman tasa’in da shida da ake gani a gefen. Dukan siffofin rumman da suke a kan ragar kewaye, guda ɗari ne.
And the pumgranatis weren nynti and sixe hangynge doun, and alle pumgranatis weren cumpassid with an hundred werkis lijk nettis.
24 Shugaban matsara kuma ya ɗauki Serahiya babban firist, da Zefaniya wanda yake biye da babban firist, da mutum uku masu tsaron ƙofar, ya tafi da su.
And the maister of the chyualrie took Saraie, the firste preest, and Sophonye, the secounde preest, and three keperis of the vestiarie.
25 Daga cikin birnin kuma ya ɗauki shugaban sojojin, da mutum bakwai’yan majalisar sarki, da magatakardan shugaban sojojin wanda yakan tara sojojin ƙasar, da mutane sittin na ƙasar, waɗanda aka same su a birnin, ya tafi da su.
And of the citee he took o chast seruaunt and onest, that was souereyn on the men werriours; and seuene men of hem that sien the face of the kyng, whiche weren foundun in the citees; and a scryuen, prince of knyytis, that preuyde yonge knyytis; and sixti men of the puple of the lond, that weren foundun in the myddis of the citee.
26 Nebuzaradan shugaban matsara ya tafi da waɗannan mutane wurin Sarkin Babilon a Ribla,
Forsothe Nabusardan, the maistir of chyualrie, took hem, and brouyte hem to the kyng of Babiloyne in Reblatha.
27 Sarkin Babilon kuwa ya kashe su a Ribla a ƙasar Hamat. Haka aka tafi da mutanen Yahuda bautar talala, daga ƙasarta.
And the kyng of Babiloyne smoot hem, and killide hem in Reblatha, in the lond of Emath; and Juda was translatid fro his lond.
28 Wannan shi ne yawan mutanen da Nebukadnezzar ya kai su bauta. A shekara ta bakwai ta sarautarsa, ya tafi da Yahudawa 3,023;
This is the puple, whom Nabugodonosor translatide in the seuenthe yeer; Jewis, thre thousynde and thre and twenti.
29 a shekara ta goma sha takwas ta sarautar Nebukadnezzar, ya tafi da Yahudawa daga Urushalima 832;
In the eiytenthe yeer, Nabugodonosor translatide fro Jerusalem eiyte hundrid and two and thritti persoones.
30 a shekara ta ashirin da uku ta sarautarsa, Nebuzaradan shugaban matsara ya tafi da Yahudawa 745. Jimillarsu duka 4,600 ne.
In the thre and twentithe yeer of Nabugodonosor, Nabusardan, the maister of chyualrie, translatide seuene hundrid and fyue and fourti persoones of Jewis. Therfor alle the persoones weren foure thousynde and sixe hundrid.
31 A shekarar da Ewil-Merodak ya zama Sarkin Babilon, sai ya nuna wa Yehohiyacin Sarkin Yahuda alheri. Ya fisshe shi daga kurkuku. Wannan ya faru ran ashirin da biyar ga watan goma sha biyu a shekara ta talatin da bakwai bayan da aka kai Yehohiyacin bauta.
And it was doon, in the seuene and threttithe yeer of the passyng ouer of Joachym, kyng of Juda, in the tweluethe monethe, in the fyue and twentithe dai of the monethe, Euylmerodach, kyng of Babiloyne, reiside in that yeer of his rewme the heed of Joachym, kyng of Juda; and ledde hym out of the hous of the prisoun,
32 Ewil-Merodak ya nuna wa Yehohiyacin alheri, ya ba shi matsayi na daraja fiye da waɗansu sarakunan da aka kai su bautar talala a Babilon tare da shi.
and spak good thingis with hym. And he settide the trone of him aboue the trones of kyngis, that weren after hym in Babiloyne,
33 Yehohiyacin ya tuɓe tufafin kurkuku, ya riƙa cin abinci kullum a teburin sarki, har dukan sauran kwanakin ransa.
and chaungide the clothis of his prisoun. And Joachym eet breed bifore hym euere, in alle the daies of his lijf;
34 Kowace rana akan ba shi kyauta bisa ga umarnin sarkin Babilon, saboda bukatarsa. Haka aka yi masa har rasuwarsa.
and hise metis, euerlastynge metis weren youun to hym of the kyng of Babiloyne, ordeyned bi ech dai, til to the dai of his deth, in alle the daies of his lijf. And it was don, aftir that Israel was led in to caitiftee, and Jerusalem was distried, Jeremye, the profete, sat wepinge, and biweilide Jerusalem with this lamentacioun; and he siyyide, and weilide with bitter soule, and seide.