< Irmiya 52 >

1 Zedekiya yana da shekara ashirin da ɗaya sa’ad da ya ci sarauta. Ya yi mulki a Urushalima shekara goma sha ɗaya. Sunan uwarsa Hamutal,’yar Irmiya, wanda yake zaune a Libna.
V jedenmecítma letech byl Sedechiáš, když počal kralovati, a jedenácte let kraloval v Jeruzalémě. Jméno matky jeho bylo Chamutal, dcera Jeremiášova z Lebna.
2 Sarki Zedekiya ya aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji kamar yadda Sarki Yehohiyakim ya yi.
I činil to, což jest zlého před očima Hospodinovýma, všecko tak, jakž byl dělal Joakim.
3 Al’amarin ya zama da muni ƙwarai a cikin Isra’ila da Yahuda, don haka Ubangiji ya husata har ya sa aka kai mutanen bautar talala. Zedekiya kuwa ya tayar wa Sarkin Babilon.
Nebo se to dálo pro rozhněvání Hospodinovo proti Jeruzalému a Judovi, až je i zavrhl od tváři své. V tom zprotivil se Sedechiáš králi Babylonskému.
4 A kan rana ta goma ga watan goma, a shekara ta tara ta mulkin Zedekiya, Sarkin Yahuda, sai Nebukadnezzar, Sarkin Babilon, ya zo yaƙi da Urushalima tare da dukan sojojinsa. Suka kewaye ta da yaƙi, suka gina katanga kewaye da ita.
Stalo se pak léta devátého kralování jeho, měsíce desátého, v desátý den téhož měsíce, že přitáhl Nabuchodonozor král Babylonský se vším vojskem svým k Jeruzalému, a položili se u něho, a vzdělali proti němu hradbu vůkol.
5 An kewaye birnin da yaƙi har shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya.
A bylo město obleženo až do jedenáctého léta krále Sedechiáše.
6 A kan rana ta tara a watan huɗu na wannan shekara, yunwa ta tsananta ƙwarai a birnin. Mutane suka rasa abin da za su ci.
V kterémžto, měsíce čtvrtého, devátého dne téhož měsíce, rozmohl se hlad v městě, a neměl chleba lid země.
7 Sai aka huda katangan birnin, sojojin kuwa suka gudu, suka fita daga cikin birnin da dare ta hanyar ƙofar da take tsakanin bango biyu, kusa da gonar sarki, sa’ad da Babiloniyawa suke kewaye da birnin. Sojojin suka nufi wajen Araba.
I prolomeny jsou zdi městské, a všickni muži bojovní utekli, a vyšli z města v noci skrze bránu mezi dvěma zdmi, u zahrady královské, (Kaldejští pak leželi okolo města), a ušli cestou pouště.
8 Amma sojojin Babiloniyawa suka runtumi sarki Zedekiya, suka ci masa a filayen Yeriko. Dukan sojoji suka yashe shi.
I honilo vojsko Kaldejské krále, a postihli Sedechiáše na rovinách Jerišských, a všecko vojsko jeho rozprchlo se od něho.
9 Da aka kama Zedekiya, sai aka kai shi wurin Sarkin Babilon a Ribla a ƙasar Hamat, a nan ne Sarkin Babilon ya yanke masa shari’a.
A tak javše krále, přivedli ho k králi Babylonskému do Ribla v zemi Emat, kdežto učinil o něm soud.
10 Sarkin Babilon ya kashe’ya’yan Zedekiya a idonsa. Ya kuma kashe dukan shugabannin Yahuda a Ribla.
I zmordoval král Babylonský syny Sedechiášovy před očima jeho, ano i všecka knížata Judská zmordoval v Ribla.
11 Sa’an nan ya ƙwaƙule idanun Zedekiya, ya kuma sa masa ƙuƙumi, aka kai shi Babilon inda aka sa shi a kurkuku har ran da ya mutu.
Oči pak Sedechiášovy oslepil, a svázav ho řetězy ocelivými král Babylonský, dal jej dovésti do Babylona, a dal jej do vězení až do dne smrti jeho.
12 A kan rana ta goma ga watan biyar a shekara ta goma sha tara ta sarautar Nebukadnezzar, Sarkin Babilon, sai Nebuzaradan shugaban matsara da kuma ɗan majalisar sarki, ya zo Urushalima.
Potom měsíce pátého, desátého dne téhož měsíce, léta devatenáctého kralování Nabuchodonozora krále Babylonského, přitáhl Nebuzardan, hejtman nad žoldnéři, kterýž sloužíval králi Babylonskému, do Jeruzaléma.
13 Sai ya ƙone haikalin Ubangiji, da gidan sarki, da dukan gine-gine masu alfarman da suke Urushalima.
A zapálil dům Hospodinův, i dům královský, i všecky domy v Jeruzalémě, a tak všecky domy veliké vypálil ohněm.
14 Sojojin Babiloniyawa da suke tare da shugaban matsara, suka rushe dukan katangan Urushalima.
Všecky také zdi Jeruzalémské vůkol pobořilo všecko vojsko Kaldejské, kteréž bylo s tím hejtmanem nad žoldnéři.
15 Sa’an nan Nebuzaradan shugaban matsara ya kwashe waɗansu matalauta, da sauran mutane da aka bari a birnin, da waɗanda suka gudu zuwa wurin Sarkin Babilon, da sauran masu sana’a, ya kai su bautar talala a Babilon.
Přitom z chaterného lidu, totiž ostatek lidu, kterýž byl zůstal v městě, i poběhlce, kteříž byli ustoupili k králi Babylonskému, a jiný obecný lid zavedl Nebuzardan, hejtman nad žoldnéři.
16 Amma ya bar waɗansu matalauta na gaske a ƙasar don su yi aiki a gonakin inabi, da sauran gonaki.
Toliko něco chaterného lidu země zanechal Nebuzardan, hejtman nad žoldnéři, aby byli vinaři a oráči.
17 Babiloniyawa kuwa suka farfasa ginshiƙan tagulla, da dakalai, da babbar kwatarniya, waɗanda suke a haikalin Ubangiji. Suka kwashe tagulla duka suka kai Babilon.
Nadto sloupy měděné, kteříž byli v domě Hospodinově, i podstavky i moře měděné, kteréž bylo v domě Hospodinově, ztloukli Kaldejští, a odvezli všecku měď z nich do Babylona.
18 Suka kwashe tukwanen ƙarfe, da manyan cokula, da hantsuka, da daruna, da tasoshin ƙona turare, da kayayyakin tagulla waɗanda ake amfani da su domin hidimar haikali.
Též hrnce. lopaty a nástroje hudebné, a kotlíky a kadidlnice, i všecky nádoby měděné, jimiž sloužili, pobrali.
19 Suka kuma kwashe ƙananan kwanonin sha, da farantan wuta, da daruna, da tukwane, da alkukai, da tasoshin ƙona turare, da kwanonin miƙa hadayar sha. Duk abin da yake na zinariya da azurfa, shugaban matsara ya kwashe.
I medenice a nádoby k oharkům, s kotlíky a hrnci, a svícny, a kadidlnice a koflíky, a cožkoli zlatého a stříbrného bylo, pobral hejtman nad žoldnéři;
20 Tagullar da sarki Solomon ya yi wa haikalin Ubangiji da ita, wato, ginshiƙai biyu, da ƙaton kwano mai suna Teku na tagulla, da bijimai goma sha biyu, waɗanda suke ɗauke da kwatarniya, da dakalai, ta fi ƙarfin a auna.
Sloupy dva, moře jedno, a volů dvanáct měděných, kteříž byli pod podstavky, jichž byl nadělal král Šalomoun do domu Hospodinova. Nebylo váhy mědi všech těch nádob.
21 Tsawon kowane ginshiƙi kamu goma sha takwas ne, kewayensa kuwa kamu goma sha biyu ne, kaurinsa kuma huɗu ne. Kowannensu yana da rami a ciki.
Nebo sloupů těch, osmnácti loket byla výška sloupu jednoho, kterýž okolek měl dvanácti loktů, ztlouští pak čtyř prstů byl dutý.
22 A kan kowane ginshiƙi, an yi masa dajiyar tagulla, tsayinta kamu biyar. A bisa kan kowace dajiya akwai raga da siffofin rumman na tagulla kewaye da dajiyar. Ginshiƙi na biyu ma haka yake da siffofin rumman.
A makovice na něm měděná, a makovice jedné výška pěti loket, a mřežování i jablka zrnatá na té makovici vůkol; všecko bylo měděné. Takovýž byl i sloup druhý s zrnatými jablky.
23 Akwai siffofin rumman tasa’in da shida da ake gani a gefen. Dukan siffofin rumman da suke a kan ragar kewaye, guda ɗari ne.
A bylo jablek zrnatých devadesát a šest po každé straně; všudy jablek zrnatých bylo po stu na mřežování vůkol.
24 Shugaban matsara kuma ya ɗauki Serahiya babban firist, da Zefaniya wanda yake biye da babban firist, da mutum uku masu tsaron ƙofar, ya tafi da su.
Vzal také hejtman nad žoldnéři Saraiáše kněze předního, a Sofoniáše kněze nižšího, a tři strážné prahu.
25 Daga cikin birnin kuma ya ɗauki shugaban sojojin, da mutum bakwai’yan majalisar sarki, da magatakardan shugaban sojojin wanda yakan tara sojojin ƙasar, da mutane sittin na ƙasar, waɗanda aka same su a birnin, ya tafi da su.
A z města vzal komorníka jednoho, kterýž byl hejtmanem nad muži bojovnými, a sedm mužů, jenž bývali při králi, kteříž nalezeni byli v městě, a předního spisovatele vojska, kterýž popisoval vojsko z lidu země, a šedesáte mužů z lidu země, kteříž nalezeni byli v městě.
26 Nebuzaradan shugaban matsara ya tafi da waɗannan mutane wurin Sarkin Babilon a Ribla,
Zjímav tedy je Nebuzardan, hejtman nad žoldnéři, přivedl je k králi Babylonskému do Ribla.
27 Sarkin Babilon kuwa ya kashe su a Ribla a ƙasar Hamat. Haka aka tafi da mutanen Yahuda bautar talala, daga ƙasarta.
I pobil je král Babylonský, a zmordoval je v Ribla v zemi Emat, a tak zaveden jest Juda z země své.
28 Wannan shi ne yawan mutanen da Nebukadnezzar ya kai su bauta. A shekara ta bakwai ta sarautarsa, ya tafi da Yahudawa 3,023;
Tenť jest lid, kterýž zavedl Nabuchodonozor léta sedmého, Judských tři tisíce a třimecítma.
29 a shekara ta goma sha takwas ta sarautar Nebukadnezzar, ya tafi da Yahudawa daga Urushalima 832;
Léta osmnáctého Nabuchodonozora zavedl z Jeruzaléma duší osm set třidceti a dvě.
30 a shekara ta ashirin da uku ta sarautarsa, Nebuzaradan shugaban matsara ya tafi da Yahudawa 745. Jimillarsu duka 4,600 ne.
Léta třimecítmého Nabuchodonozora zavedl Nebuzardan, hejtman nad žoldnéři, Judské, duší sedm set čtyřidceti a pět, všech duší čtyry tisíce a šest set.
31 A shekarar da Ewil-Merodak ya zama Sarkin Babilon, sai ya nuna wa Yehohiyacin Sarkin Yahuda alheri. Ya fisshe shi daga kurkuku. Wannan ya faru ran ashirin da biyar ga watan goma sha biyu a shekara ta talatin da bakwai bayan da aka kai Yehohiyacin bauta.
Stalo se také třidcátého sedmého léta po zajetí Joachina krále Judského, dvanáctého měsíce, dvadcátého pátého dne téhož měsíce, povýšil Evilmerodach král Babylonský toho léta, když počal kralovati, Joachina krále Judského, pustiv ho z žaláře.
32 Ewil-Merodak ya nuna wa Yehohiyacin alheri, ya ba shi matsayi na daraja fiye da waɗansu sarakunan da aka kai su bautar talala a Babilon tare da shi.
A mluvil s ním dobrotivě, i stolici jeho postavil nad stolice králů, kteříž s ním byli v Babyloně.
33 Yehohiyacin ya tuɓe tufafin kurkuku, ya riƙa cin abinci kullum a teburin sarki, har dukan sauran kwanakin ransa.
Změnil též roucho jeho, kteréž měl v žaláři, a jídal chléb před ním vždycky, po všecky dny života svého.
34 Kowace rana akan ba shi kyauta bisa ga umarnin sarkin Babilon, saboda bukatarsa. Haka aka yi masa har rasuwarsa.
Nebo vyměřený pokrm ustavičně dáván byl jemu od krále Babylonského, a to na každý den, až do dne smrti jeho, po všecky dny života jeho.

< Irmiya 52 >