< Irmiya 51 >
1 Ubangiji ya ce, “Ga shi, zan zuga ruhun mai hallakarwa a kan Babilon da mutanen Leb Kamai.
diz Yahweh: “Eis que eu me levantarei contra a Babilônia”, e contra aqueles que habitam em Lebkamai, um vento destruidor.
2 Zan aika da baƙi zuwa Babilon su casa ta su kuma yi kaca-kaca da ƙasarta; za su yi hamayya da ita a kowane gefe a ranar masifarta.
Enviarei a estranhos da Babilônia, que a conhecerão. Eles vão esvaziar suas terras; pois no dia dos problemas, eles estarão contra ela em todos os lugares.
3 Kada ku bar maharbi yă ja bakansa, kada kuma ku bari yă sa kayan yaƙinsa. Kada ku rage samarinta, ku hallaka sojojinta ƙaf.
Contra aquele que se dobra, deixe o arqueiro dobrar seu arco, também contra aquele que se ergue em seu casaco de correio. Não poupe os seus jovens! Destruir totalmente todo o seu exército!
4 Za su fāɗi matattu a ƙasar Babilon, da munanan raunuka a titunanta.
Eles cairão mortos na terra dos caldeus, e empurrar através de suas ruas.
5 Gama Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila da Yahuda bai yashe su ba, ko da yake ƙasarsu cike da take da laifi a gaban Mai Tsarki na Isra’ila.
Pois Israel não é abandonado, nem Judá, por seu Deus, por Yahweh dos Exércitos; embora suas terras estejam cheias de culpas contra o Santo de Israel.
6 “Ku gudu daga cikin Babilon! Bari kowa yă ceci ransa! Kada a hallaka saboda zunubanta. Gama lokaci ne don ramuwar Ubangiji, zai sāka mata bisa ga alhakinta.
“Fuja do meio da Babilônia! Cada um salva sua própria vida! Não seja cortado em sua iniqüidade, pois é a época da vingança de Yahweh. Ele lhe dará uma recompensa.
7 Babilon ta zama ƙoƙon zinariya a hannun Ubangiji, ta sa dukan duniya ta yi maye. Ƙasashe sun sha ruwan inabinta, saboda haka yanzu sun haukace.
A Babilônia tem sido um copo de ouro na mão de Iavé, que embebedou toda a terra. As nações beberam de seu vinho; portanto, as nações enlouqueceram.
8 Farat ɗaya Babilon za tă fāɗi ta farfashe. Ku yi kuka dominta! Ku samo mata magani saboda azabarta; wataƙila za a iya warkar da ita.
A Babilônia caiu e foi destruída de repente! Lamento por ela! Tome bálsamo para a dor dela. Talvez ela possa ser curada.
9 “‘Da mun warkar da Babilon, amma ba za tă warke ba; mu ƙyale ta kowane yă koma garinsu, gama hukuncinta ya kai sammai, ya yi tsawo kamar gizagizai.’
“Teríamos curado a Babilônia, mas ela não está curada. Abandone-a, e vamos cada um para seu próprio país; pois seu julgamento chega ao céu, e é erguido até os céus.
10 “‘Ubangiji ya baratar da mu; zo mu tafi mu yi shelarsa a Sihiyona mu faɗa abin da Ubangiji Allahnmu ya yi.’
'Yahweh produziu nossa retidão. Venha, e vamos declarar em Zion o trabalho de Javé nosso Deus”.
11 “Ku wasa kibiyoyi, ku ɗauko garkuwoyi! Ubangiji ya zuga sarakunan Medes, domin niyyarsa ce yă hallaka Babilon. Ubangiji zai yi ramuwa, zai yi ramuwa saboda haikalinsa.
“Faça as setas afiadas! Segurem os escudos firmemente! Yahweh despertou o espírito dos reis dos medos, porque seu propósito é contra a Babilônia, para destruí-la; pois é a vingança de Yahweh, a vingança de seu templo.
12 Ku tā da tuta gāba da katangan Babilon! Ku ƙara matsara, ku kafa masu tsaro, ku shirya kwanto! Ga shi, Ubangiji zai aikata abin da ya faɗa umarninsa a kan mutanen Babilon.
Estabeleça um padrão contra as paredes da Babilônia! Faça o relógio forte! Colocar os guardas, e preparar as emboscadas; para Yahweh tem feito e feito de propósito o que ele falou a respeito dos habitantes da Babilônia.
13 Ke da kike zama kusa da ruwaye da kike kuma wadatar dukiya, ƙarshenki ya zo, lokaci ya yi da za a kau da ke.
Você que mora em muitas águas, abundante em tesouros, seu fim chegou, a medida de sua cobiça.
14 Ubangiji Maɗaukaki ya rantse da zatinsa, ya ce Tabbatacce zan cika ka da mutane kamar fāra, za su kuwa yi sowa don nasara a kanka.
Yahweh dos Exércitos jurou por si mesmo, dizendo, “Certamente eu vou enchê-lo de homens, como com os gafanhotos, e eles levantarão um grito contra você”.
15 “Ya halicci ƙasa ta wurin ikonsa; ya kafa duniya ta wurin hikimarsa, ya kuma shimfiɗa sammai ta wurin fahiminsa.
“Ele fez a terra pelo seu poder. Ele estabeleceu o mundo por sua sabedoria. Pelo seu entendimento, ele estendeu os céus.
16 Sa’ad da ya yi tsawa ruwan da suke sammai sukan yi ruri; yakan sa gizagizai su tashi daga ƙarshen duniya. Yakan tura walƙiya tare da ruwan sama yakan kuma saki iska daga cikin taskokinsa.
Quando ele profere sua voz, há um barulho de águas nos céus, e ele faz com que os vapores subam das extremidades da terra. Ele faz relâmpagos para a chuva, e traz o vento para fora de seus tesouros.
17 “Kowane mutum marar azanci ne kuma ba shi da sani; kowane maƙerin zinariya yakan sha kunya daga wurin gumakansa. Siffofinsa na ƙarya ne; babu numfashi a cikinsu.
“Todo homem se tornou estúpido e sem conhecimento. Todo ourives está decepcionado com sua imagem, por suas imagens derretidas são falsas, e não há fôlego nelas.
18 Su marasa amfani ne, abubuwan ba’a ne kawai; sa’ad da lokacin hukuncinsu ya kai, za su hallaka.
Eles são vaidade, um trabalho de ilusão. No momento de sua visita, eles perecerão.
19 Wanda yake na wajen Yaƙub ba kamar waɗannan ba ne, gama shi ne Mahalicci dukan abu, har da kabilar abin gādonsa, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
A porção de Jacob não é como estas, pois ele formou todas as coisas, incluindo a tribo de sua herança. Yahweh dos Exércitos é seu nome.
20 “Kai ne kulkin yaƙina, kayan yaƙina, da kai ne na ragargaza ƙasashe, da kai ne na hallaka mulkoki,
“Vocês são meu eixo de batalha e minhas armas de guerra. Com vocês, eu quebrarei as nações em pedaços. Com vocês, destruirei os reinos.
21 da kai ne na ragargaza doki da mahayi, da kai ne na ragargaza keken yaƙin da matuƙi,
Com você eu vou quebrar em pedaços o cavalo e seu cavaleiro.
22 da kai ne na ragargaza miji da mata, da kai ne na ragargaza tsoho da saurayi, da kai ne na ragargaza saurayi da budurwa,
Com você eu vou quebrar em pedaços a carruagem e aquele que nela viaja. Com você eu vou quebrar em pedaços homem e mulher. Com você eu vou quebrar em pedaços o velho e os jovens. Com você eu vou quebrar em pedaços o jovem e a virgem.
23 da kai ne na ragargaza makiyayi da garke, da kai ne na ragargaza manoma da dawakan noma, da kai ne na ragargaza masu mulki da shugabanni.
With você eu vou quebrar em pedaços o pastor e seu rebanho. Com você eu vou quebrar em pedaços o fazendeiro e seu jugo. Com você eu vou quebrar em pedaços governadores e deputados.
24 “Zan sāka wa Babilon da dukan mazaunan Babilon a idanunku saboda dukan muguntar da suka aikata a Sihiyona,” in ji Ubangiji.
“Eu vou entregar à Babilônia e a todos os habitantes da Caldéia todo o mal que eles fizeram em Sião à sua vista”, diz Yahweh.
25 “Ga shi, ina gāba da kai, ya ke dutse mai hallakarwa, wadda ta hallaka duniya duka,” in ji Ubangiji. “Zan miƙa hannuna gāba da ke, zan mirgina ƙasa daga ƙwanƙolin dutse, zan maishe ki ƙonannen dutse.
“Eis que estou contra ti, destruindo a montanha”, diz Javé, “que destrói toda a terra”. Estenderei minha mão sobre você, rolar você das rochas, e fará de você uma montanha queimada.
26 Ba za a ɗauki dutsen yin kusurwa daga gare ki ba ko na kafa harsashen gini, gama za ki zama marar amfani har abada,” in ji Ubangiji.
Eles não lhe tirarão uma pedra angular, nem uma pedra para fundações; mas você ficará desolado para sempre”, diz Yahweh.
27 “Ku tā da tuta a ƙasa! Ku busa ƙahoni a cikin ƙasashe! Ku shirya ƙasashe don yaƙi da ita, ku kira waɗannan mulkokin gāba da ita. Ararat, Minni, da Ashkenaz. A naɗa shugaba gāba da ita; ku shirya dawakai kamar fāra.
“Estabeleça um padrão na terra! Tocar a trombeta entre as nações! Prepare as nações contra ela! Chamem juntos contra ela os reinos de Ararat, Minni, e Ashkenaz! Nomeie um marechal contra ela! Porque os cavalos devem aparecer como os gafanhotos enxameadores!
28 Ku shirya ƙasashe don yaƙi da ita, sarakunan Medes, gwamnoninsu da dukan masu shugabancinsu da kowace ƙasar da take ƙarƙashin mulkinsu.
Preparar contra ela as nações, os reis dos medos, seus governadores, e todos os seus deputados, e toda a terra de seu domínio!
29 Ƙasa ta girgiza tana makyarkyata saboda nufin Ubangiji na gāba da Babilon ya tabbata, nufinsa na mai da ƙasar Babilon kufai don kada kowa yă zauna a can.
A terra treme e está em sofrimento; para os propósitos de Yahweh contra a banca de Babilônia, para tornar a terra da Babilônia uma desolação, sem habitantes.
30 Sojojin Babilon sun daina yaƙi, suna zaune a cikin kagaransu. Ƙarfinsu ya ƙare, sun zama mata. An sa wa wuraren zamanta wuta, an karya ƙyamaren ƙofofin garinta.
Os poderosos homens da Babilônia pararam de lutar, eles permanecem em suas fortalezas. O poder deles falhou. Elas se tornaram como mulheres. Seus locais de moradia são incendiados. Suas barras estão quebradas.
31 Maguji yana biye da maguji a guje, jakada yana biye da jakada, don su faɗa wa sarkin Babilon, cewa an ci birninsa a kowane gefe.
Um corredor correrá para encontrar outro, e um mensageiro para encontrar outro, para mostrar ao rei da Babilônia que sua cidade é tomada a cada trimestre.
32 An ƙwace mashigai aka ƙone fadamu da wuta, sojoji kuma suka giggice.”
Assim, as passagens são apreendidas. Eles queimaram os canaviais com fogo. Os homens de guerra estão assustados”.
33 Ni Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila na ce, “’Yar Babilon kamar daɓen masussuka a lokacin da ake sussuka, ba da daɗewa ba lokacin girbe ta zai zo.”
Para Iavé dos Exércitos, diz o Deus de Israel: “A filha da Babilônia é como uma eira no momento em que é pisada. Ainda um pouco, e a hora da colheita chega para ela”.
34 “Nebukadnezzar sarkin Babilon ya cinye mu, ya sa muka rikice, ya maishe mu kamar tulun da babu kome a cikinsa. Ya cinye mu kamar yadda dodon ruwa yakan yi ya kuma cika cikinsa da kayan marmarinmu, sa’an nan kuma ya yi amanmu.
“Nabucodonosor, o rei da Babilônia, me devorou. Ele me esmagou. Ele me fez um recipiente vazio. Ele, como um monstro, me engoliu. Ele encheu sua boca com minhas iguarias. Ele me expulsou.
35 Bari abin da aka yi wa jikinmu yă kasance a bisa Babilon,” in ji mazaunan Sihiyona. “Bari jininmu yă kasance a kan waɗanda suke zama a Babilon,” in ji Urushalima.
May a violência feita a mim e à minha carne seja na Babilônia”! o habitante de Sião dirá; e, “Que meu sangue caia sobre os habitantes da Caldéia!” dirá Jerusalém.
36 Saboda haka ga abin da Ubangiji ya ce, “Duba, zan tsaya muku, zan ɗaukar muku fansa, zan sa tekunta kafe in kuma sa maɓulɓulanta su ƙafe.
Portanto, diz Yahweh: “Eis que eu defenderei sua causa, e se vingar por você. Eu vou secar o mar dela, e fazer sua fonte secar.
37 Babilon za tă zama tarin juji, wurin zaman diloli, abin ƙyama da abar ba’a, inda ba kowa.
A Babilônia se transformará em montões, uma morada para chacais, um espanto, e um assobio, sem habitante.
38 Mutanenta duk suna ruri kamar zakoki, suna gurnani kamar’ya’yan zaki.
Eles irão rugir juntos como leões jovens. Eles rosnarão como filhotes de leões.
39 Amma sa’ad da aka farkar da su, zan yi musu biki in sa su sha su bugu, domin yi sowa da dariya, sa’an nan su shiga barcin da ba za su farka ba,” in ji Ubangiji.
Quando eles estiverem inflamados, farei seu banquete, e eu os deixarei bêbados, que eles possam se regozijar, e dormir um sono perpétuo, e não acordar”, diz Yahweh.
40 “Zan sauko da su kamar tumaki zuwa mayanka, kamar raguna da bunsurai.
“Vou derrubá-los como cordeiros para o abate, como carneiros com caprinos machos.
41 “Yadda za a ci Sheshak, taƙamar duniya duka za tă daina! Babilon za tă zama abar ƙyama a cikin al’ummai!
“Como Sheshach é tomado! Como o elogio de toda a terra é apreendido! Como a Babilônia se tornou uma desolação entre as nações!
42 Teku zai malalo a kan Babilon, raƙumansa masu hauka za su rufe ta.
O mar subiu sobre a Babilônia. Ela está coberta com a multidão de suas ondas.
43 Garuruwanta sun zama abin kufai, za tă zama hamada inda ba ruwa, ƙasar da ba mazauna, ba kuma mutumin da zai ratsa ta cikinta.
Suas cidades se tornaram uma desolação, uma terra seca, e um deserto, uma terra em que nenhum homem habita. Nenhum filho do homem passa por ela.
44 Zan hukunta Bel a Babilon, in sa ya yi aman abin da ya haɗiye. Ƙasashe ba za su ƙara bumbuntowa wurinsa ba. Katangan Babilon kuwa za tă rushe!
Vou executar o julgamento sobre Bel in Babylon, e tirarei de sua boca aquilo que ele engoliu. As nações não fluirão mais para ele. Sim, a parede da Babilônia vai cair.
45 “Ku fito daga cikinta, jama’ata! Ku tsere da ranku! Ku tsere daga zafin fushin Ubangiji.
“Meu povo, vá para longe do meio dela, e cada um de vocês se salvem da raiva feroz de Yahweh.
46 Kada zuciyarku tă yi suwu ko ku ji tsoro sa’ad da aka ji labarin a ƙasar, labari guda a wannan shekara, wani kuma a ta biye, labarin hargitsi a ƙasar mai mulki ya tasar wa mai mulki.
Don não deixe seu coração desmaiar. Não temam pelas notícias que serão ouvidas na terra. Para notícias virá um ano, e depois disso, em mais um ano, virão notícias, e a violência na terra, governante contra governante.
47 Gama kwanaki tabbatacce suna zuwa, sa’ad da zan hukunta gumakan Babilon, zan kunyatar da dukan ƙasar kuma matattunta duk za su kwanta a cikinta.
Portanto, eis que vêm os dias em que executarei o julgamento sobre as imagens gravadas da Babilônia; e toda sua terra será confundida. Todos os seus mortos cairão no meio dela.
48 Sa’an nan sama da ƙasa da dukan abin da yake cikinsu, za su yi sowa ta murna a kan Babilon, gama daga arewa masu hallakarwa su auko mata,” in ji Ubangiji.
Depois, os céus e a terra, e tudo o que aí está, cantará de alegria sobre a Babilônia; pois os destruidores virão até ela do norte”, diz Yahweh.
49 “Babilon za tă fāɗi saboda kisassun mutanen Isra’ila, kamar dai yadda kisassu dukan duniya suka fāɗi saboda Babilon.
“Como a Babilônia causou a queda dos mortos de Israel, Assim, os mortos de toda a terra cairão na Babilônia.
50 Ku waɗanda kuka tsere wa takobi, ku gudu kada ku tsaya! Ku tuna da Ubangiji a ƙasa mai nesa, ku kuma yi ta tunani a kan Urushalima.”
Você que escapou da espada, vá! Não fique parado! Lembre-se de Yahweh de longe, e deixar Jerusalém entrar em sua mente”.
51 “Mun sha kunya saboda zargin da ake yi mana kunya ta rufe mu, domin baƙi sun shiga tsarkakan wurare na gidan Ubangiji.”
“Estamos confusos porque ouvimos censuras. A confusão cobriu nossos rostos, para estranhos entraram nos santuários da casa de Yahweh”.
52 “Amma kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan hukunta gumakanta, da kuma a dukan ƙasarta waɗanda aka yi wa rauni, za su yi nishi.
“Portanto, eis que vêm os dias”, diz Yahweh, “que executarei o julgamento sobre suas imagens gravadas”; e através de todas as suas terras os feridos gemerão.
53 Ko da Babilon za tă kai sararin sama ne, ta gina kagaranta mai ƙarfi, duk da haka zan aiki masu hallakarwa a kanta,” in ji Ubangiji.
Embora a Babilônia deva se montar até o céu, e embora ela deva fortificar a altura de sua força, mas os destruidores virão até ela da minha parte”, diz Yahweh.
54 “Ku ji muryar kuka daga Babilon, Da hargowar babbar hallakarwa daga ƙasar Babiloniyawa!
“O som de um grito vem da Babilônia, e de grande destruição da terra dos caldeus!
55 Gama Ubangiji zai rushe Babilon, zai sa ta ƙame bakinta na alfarma. Sojoji za su yi ta kutsawa kamar raƙuman ruwa; suna tā da muryoyinsu.
Para Yahweh, o desperdício de Babilônia, e destrói dela a grande voz! Suas ondas bramem como muitas águas. O ruído de sua voz é pronunciado.
56 Gama mai hallakarwa ya auka wa Babilon, a kama sojojinta, a kuma kakkarya bakkunansu. Gama Ubangiji shi Allah ne mai sakayya; zai yi sakayya sosai.
Pois o contratorpedeiro veio sobre ela, mesmo na Babilônia. Seus poderosos homens são levados. Seus arcos estão quebrados em pedaços, pois Yahweh é um Deus de retribuição. Ele certamente irá pagar.
57 Zan sa mahukuntanta da masu hikimarta, gwamnoninta, shugabanninta da sojojinta su sha su bugu; za su dinga yin barcin da ba za su farka ba,” in ji Sarkin, mai suna Ubangiji Maɗaukaki.
Vou fazer dela príncipes, seus sábios, seus governadores, seus deputados e seus poderosos homens bêbados. Eles dormirão um sono perpétuo, e não acordar”. diz o Rei, cujo nome é Yahweh dos Exércitos.
58 Ni Ubangiji Maɗaukaki, na ce, “Za a baje katangan nan na Babilon mai kauri za a kuma ƙone dogayen ƙyamarenta da wuta; mutane sun wahalar da kansu a banza, al’umma sun yi wahala kawai domin wutar lalata.”
diz Yahweh dos Exércitos: “As amplas paredes da Babilônia serão totalmente derrubadas”. Seus portões altos serão queimados com fogo. Os povos trabalharão por vaidade, e as nações para o fogo; e eles ficarão cansados”.
59 Jawabin da annabi Irmiya ya ba Serahiya, ɗan Neriya, wato, jikan Ma’asehiya, lokacin da ya tafi tare da Zedekiya, Sarkin Yahuda, zuwa Babilon a shekara ta huɗu ta mulkinsa. Serahiya shi ne shugaba mai lura da gidajen saukar baƙi.
A palavra que Jeremias o profeta ordenou a Seraías, filho de Nerias, filho de Maquias, quando ele foi com Zedequias, rei de Judá, à Babilônia, no quarto ano de seu reinado. Agora Seraías era o chefe de quarto mestre.
60 Irmiya ya rubuta a littafi dukan masifun da za su auko wa Babilon, wato, dukan wannan magana da aka rubuta a kan Babilon.
Jeremias escreveu em um livro todo o mal que deveria vir sobre a Babilônia, mesmo todas estas palavras que estão escritas a respeito da Babilônia.
61 Irmiya kuwa ya ce wa Serahiya, “Lokacin da ka kai Babilon, sai ka karanta dukan maganan nan.
Jeremias disse a Seraías: “Quando você vier à Babilônia, então veja que leu todas estas palavras,
62 Ka kuma ce, ‘Ya Ubangiji, kai ne ka yi magana a kan wannan wuri, cewa za ka lalatar da shi, har ba abin da zai zauna a ciki, mutum ko dabba. Wurin zai zama kufai har abada.’
e diga: 'Javé, você falou a respeito deste lugar, para cortá-lo, que ninguém habitará nele, nem homem nem animal, mas que ficará desolado para sempre'.
63 Sa’ad da ka gama karanta wannan littafi, sai ka ɗaura wa littafin dutse, sa’an nan ka jefar da shi tsakiyar Kogin Yuferites.
Será, quando terminar de ler este livro, que você deve amarrar uma pedra a ele, e lançá-lo no meio do Eufrates.
64 Sa’an nan ka ce, ‘Haka Babilon za tă nutse, ba za tă ƙara tashi ba saboda masifar da zan kawo mata. Mutanenta kuwa za su fāɗi.’” Wannan shi ne ƙarshen kalmomin Irmiya.
Então dirás: 'Assim a Babilônia se afundará, e não se levantará novamente por causa do mal que eu a trarei; e eles se cansarão'”. Até agora, são as palavras de Jeremias.