< Irmiya 51 >
1 Ubangiji ya ce, “Ga shi, zan zuga ruhun mai hallakarwa a kan Babilon da mutanen Leb Kamai.
Voici ce que dit le Seigneur: Voilà que moi je susciterai sur Babylone et sur ses habitants, qui ont élevé leur cœur contre moi, comme un vent pestilentiel.
2 Zan aika da baƙi zuwa Babilon su casa ta su kuma yi kaca-kaca da ƙasarta; za su yi hamayya da ita a kowane gefe a ranar masifarta.
Et j’enverrai contre Babylone des gens le van à la main; et ils la vanneront, et ils ruineront sa terre. De tous côtés ils sont venus sur elle au jour de son affliction.
3 Kada ku bar maharbi yă ja bakansa, kada kuma ku bari yă sa kayan yaƙinsa. Kada ku rage samarinta, ku hallaka sojojinta ƙaf.
Que celui qui tend son arc ne le tende pas, et que nul ne monte cuirassé; n’épargnez point ses jeunes hommes; tuez toute sa milice.
4 Za su fāɗi matattu a ƙasar Babilon, da munanan raunuka a titunanta.
Et les tués tomberont dans la terre des Chaldéens, et les blessés dans ses provinces.
5 Gama Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila da Yahuda bai yashe su ba, ko da yake ƙasarsu cike da take da laifi a gaban Mai Tsarki na Isra’ila.
Parce qu’Israël et Juda ne sont pas veufs de leur Dieu, le Seigneur des armées; mais leur terre a été remplie de crimes contre le saint d’Israël.
6 “Ku gudu daga cikin Babilon! Bari kowa yă ceci ransa! Kada a hallaka saboda zunubanta. Gama lokaci ne don ramuwar Ubangiji, zai sāka mata bisa ga alhakinta.
Fuyez du milieu de Babylone, et que chacun sauve son âme; ne vous taisez point sur son iniquité; car c’est le temps de la vengeance du Seigneur; lui-même la rétribuera.
7 Babilon ta zama ƙoƙon zinariya a hannun Ubangiji, ta sa dukan duniya ta yi maye. Ƙasashe sun sha ruwan inabinta, saboda haka yanzu sun haukace.
Babylone a été une coupe d’or dans la main du Seigneur; elle a enivré toute la terre; les nations ont bu de son vin, c’est pour cela qu’elles ont chancelé.
8 Farat ɗaya Babilon za tă fāɗi ta farfashe. Ku yi kuka dominta! Ku samo mata magani saboda azabarta; wataƙila za a iya warkar da ita.
Babylone est tombée subitement, et elle a été brisée; poussez des hurlements sur elle; prenez de la résine pour sa douleur, afin de voir si elle guérira.
9 “‘Da mun warkar da Babilon, amma ba za tă warke ba; mu ƙyale ta kowane yă koma garinsu, gama hukuncinta ya kai sammai, ya yi tsawo kamar gizagizai.’
Nous avons soigné Babylone, et elle n’a pas été guérie; abandonnons-la et allons chacun en notre terre, parce que jusqu’aux cieux est parvenu son jugement, et qu’il s’est élevé jusqu’aux nues.
10 “‘Ubangiji ya baratar da mu; zo mu tafi mu yi shelarsa a Sihiyona mu faɗa abin da Ubangiji Allahnmu ya yi.’
Le Seigneur a fait ressortir notre justice; venez, et racontons dans Sion l’ouvrage du Seigneur, notre Dieu.
11 “Ku wasa kibiyoyi, ku ɗauko garkuwoyi! Ubangiji ya zuga sarakunan Medes, domin niyyarsa ce yă hallaka Babilon. Ubangiji zai yi ramuwa, zai yi ramuwa saboda haikalinsa.
Aiguisez les flèches, remplissez les carquois; le Seigneur a suscité l’esprit des rois des Mèdes, et sa pensée est contre Babylone afin de la perdre; parce que c’est la vengeance du Seigneur, la vengeance de son temple.
12 Ku tā da tuta gāba da katangan Babilon! Ku ƙara matsara, ku kafa masu tsaro, ku shirya kwanto! Ga shi, Ubangiji zai aikata abin da ya faɗa umarninsa a kan mutanen Babilon.
Sur les murs de Babylone levez l’étendard, augmentez la garde, posez des sentinelles, préparez les embuscades, parce que le Seigneur a résolu et il a accompli tout ce qu’il a dit contre les habitants de Babylone.
13 Ke da kike zama kusa da ruwaye da kike kuma wadatar dukiya, ƙarshenki ya zo, lokaci ya yi da za a kau da ke.
Toi qui habites sur de grandes eaux, riche en trésors, ta fin est venue, c’est le fondement de ta destruction.
14 Ubangiji Maɗaukaki ya rantse da zatinsa, ya ce Tabbatacce zan cika ka da mutane kamar fāra, za su kuwa yi sowa don nasara a kanka.
Le Seigneur des armées a juré par son âme, disant: Je te remplirai d’hommes comme de bruchus, et on entonnera sur toi un chant de joie.
15 “Ya halicci ƙasa ta wurin ikonsa; ya kafa duniya ta wurin hikimarsa, ya kuma shimfiɗa sammai ta wurin fahiminsa.
C’est lui qui a fait la terre par sa puissance, préparé l’univers par sa sagesse, et par sa prudence étendu les cieux.
16 Sa’ad da ya yi tsawa ruwan da suke sammai sukan yi ruri; yakan sa gizagizai su tashi daga ƙarshen duniya. Yakan tura walƙiya tare da ruwan sama yakan kuma saki iska daga cikin taskokinsa.
Lorsqu’il fait entendre sa voix, les eaux s’amassent dans le ciel; c’est lui qui fait monter les nuées des extrémités de la terre; il a converti les éclairs en pluie, et il a tiré les vents de ses trésors.
17 “Kowane mutum marar azanci ne kuma ba shi da sani; kowane maƙerin zinariya yakan sha kunya daga wurin gumakansa. Siffofinsa na ƙarya ne; babu numfashi a cikinsu.
Tout homme est devenu insensé par sa propre science; tout fondeur a été confondu par son image taillée au ciseau, parce que c’est une chose mensongère qu’il a fondue, et que la vie n’y est pas.
18 Su marasa amfani ne, abubuwan ba’a ne kawai; sa’ad da lokacin hukuncinsu ya kai, za su hallaka.
Vaines sont leurs œuvres et dignes de risée; au temps de leur visite elles périront.
19 Wanda yake na wajen Yaƙub ba kamar waɗannan ba ne, gama shi ne Mahalicci dukan abu, har da kabilar abin gādonsa, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
Il n’en est pas ainsi de la part de Jacob, parce que celui qui a fait toutes ces choses est lui-même son partage; et Israël est le sceptre de son héritage; le Seigneur des armées est son nom.
20 “Kai ne kulkin yaƙina, kayan yaƙina, da kai ne na ragargaza ƙasashe, da kai ne na hallaka mulkoki,
Tu brises pour moi des instruments de guerre, et je briserai par toi des nations, et je perdrai entièrement par toi des royaumes;
21 da kai ne na ragargaza doki da mahayi, da kai ne na ragargaza keken yaƙin da matuƙi,
Et je briserai par toi le cheval et celui qui le monte; et je briserai par toi le char et celui qui le monte;
22 da kai ne na ragargaza miji da mata, da kai ne na ragargaza tsoho da saurayi, da kai ne na ragargaza saurayi da budurwa,
Et je briserai par toi l’homme et la femme; et je briserai par toi le vieillard et l’enfant; et je briserai par toi le jeune homme et la vierge;
23 da kai ne na ragargaza makiyayi da garke, da kai ne na ragargaza manoma da dawakan noma, da kai ne na ragargaza masu mulki da shugabanni.
Et je briserai par toi le pasteur et son troupeau; et je briserai par toi le laboureur et ses bœufs attachés au joug; et je briserai par toi les chefs et les magistrats.
24 “Zan sāka wa Babilon da dukan mazaunan Babilon a idanunku saboda dukan muguntar da suka aikata a Sihiyona,” in ji Ubangiji.
Et je rendrai à Babylone et à tous les habitants de la Chaldée tout leur mal, qu’ils ont fait dans Sion, à vos yeux, dit le Seigneur.
25 “Ga shi, ina gāba da kai, ya ke dutse mai hallakarwa, wadda ta hallaka duniya duka,” in ji Ubangiji. “Zan miƙa hannuna gāba da ke, zan mirgina ƙasa daga ƙwanƙolin dutse, zan maishe ki ƙonannen dutse.
Et voilà que je viens à toi, montagne pernicieuse, dit le Seigneur, qui corromps toute la terre; et j’étendrai ma main sur toi, et je t’arracherai d’entre les rochers, et je ferai de toi une montagne en combustion.
26 Ba za a ɗauki dutsen yin kusurwa daga gare ki ba ko na kafa harsashen gini, gama za ki zama marar amfani har abada,” in ji Ubangiji.
Et on ne tirera pas de toi une pierre pour un angle, ni une pierre pour des fondements; mais tu seras éternellement détruite, dit le Seigneur.
27 “Ku tā da tuta a ƙasa! Ku busa ƙahoni a cikin ƙasashe! Ku shirya ƙasashe don yaƙi da ita, ku kira waɗannan mulkokin gāba da ita. Ararat, Minni, da Ashkenaz. A naɗa shugaba gāba da ita; ku shirya dawakai kamar fāra.
Levez l’étendard sur la terre; sonnez la trompette parmi des nations; consacrez contre elle des nations; annoncez aux rois d’Ararat, de Menni et d’Ascenez de marcher contre elle; dénombrez contre elle les soldats du Taphsar; amenez contre elle le cheval, comme le bruchus armé d’un aiguillon.
28 Ku shirya ƙasashe don yaƙi da ita, sarakunan Medes, gwamnoninsu da dukan masu shugabancinsu da kowace ƙasar da take ƙarƙashin mulkinsu.
Consacrez contre elle des nations, les rois de Médie, ses chefs et tous ses magistrats, et toute la terre soumise à sa puissance.
29 Ƙasa ta girgiza tana makyarkyata saboda nufin Ubangiji na gāba da Babilon ya tabbata, nufinsa na mai da ƙasar Babilon kufai don kada kowa yă zauna a can.
Et la terre sera agitée et troublée; parce que contre Babylone s’éveillera la pensée du Seigneur, afin de rendre la terre de Babylone déserte et inhabitable.
30 Sojojin Babilon sun daina yaƙi, suna zaune a cikin kagaransu. Ƙarfinsu ya ƙare, sun zama mata. An sa wa wuraren zamanta wuta, an karya ƙyamaren ƙofofin garinta.
Les forts de Babylone ont cessé le combat; ils sont demeurés dans les citadelles: leur force a été dévorée, et ils sont devenus comme des femmes; leurs tabernacles ont été brûlés, leurs verrous ont été brisés.
31 Maguji yana biye da maguji a guje, jakada yana biye da jakada, don su faɗa wa sarkin Babilon, cewa an ci birninsa a kowane gefe.
Un coureur viendra au-devant d’un coureur, et un messager à la rencontre d’un messager, afin d’annoncer au roi de Babylone que sa ville a été prise d’un bout à l’autre;
32 An ƙwace mashigai aka ƙone fadamu da wuta, sojoji kuma suka giggice.”
Et que les gués sont occupés, et que le feu a été mis aux marais, et que les hommes de guerre ont été bouleversés.
33 Ni Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila na ce, “’Yar Babilon kamar daɓen masussuka a lokacin da ake sussuka, ba da daɗewa ba lokacin girbe ta zai zo.”
Parce que voici ce que dit le Seigneur des armées, Dieu d’Israël: La fille de Babylone est comme une aire: c’est le temps de son battage; encore un peu et viendra le temps de sa moisson.
34 “Nebukadnezzar sarkin Babilon ya cinye mu, ya sa muka rikice, ya maishe mu kamar tulun da babu kome a cikinsa. Ya cinye mu kamar yadda dodon ruwa yakan yi ya kuma cika cikinsa da kayan marmarinmu, sa’an nan kuma ya yi amanmu.
Il m’a mangée; il m’a dévorée, Nabuchodonosor, roi de Babylone, il m’a rendue comme un vase vide, il m’a engloutie comme un dragon, il a rempli son ventre de ce que j’avais de plus délicieux, et il m’a rejetée.
35 Bari abin da aka yi wa jikinmu yă kasance a bisa Babilon,” in ji mazaunan Sihiyona. “Bari jininmu yă kasance a kan waɗanda suke zama a Babilon,” in ji Urushalima.
L’iniquité commise contre moi et ma chair est retombée sur Babylone, dit l’habitation de Sion, et mon sang sur les habitants de la Chaldée, dit Jérusalem.
36 Saboda haka ga abin da Ubangiji ya ce, “Duba, zan tsaya muku, zan ɗaukar muku fansa, zan sa tekunta kafe in kuma sa maɓulɓulanta su ƙafe.
À cause de cela, voici ce que dit le Seigneur: Voilà que moi je jugerai ta cause, et j’exercerai ta vengeance: je sécherai sa mer, et je tarirai sa source.
37 Babilon za tă zama tarin juji, wurin zaman diloli, abin ƙyama da abar ba’a, inda ba kowa.
Et Babylone sera un monceau de pierres, une demeure de dragons, un objet de stupeur et de sifflement, parce qu’il n’y a point d’habitant.
38 Mutanenta duk suna ruri kamar zakoki, suna gurnani kamar’ya’yan zaki.
Tous ensemble ils rugiront comme des lions, ils secoueront leur crinière comme de petits bons.
39 Amma sa’ad da aka farkar da su, zan yi musu biki in sa su sha su bugu, domin yi sowa da dariya, sa’an nan su shiga barcin da ba za su farka ba,” in ji Ubangiji.
Dans leur chaleur je leur donnerai leurs boissons, et je les enivrerai, afin qu’ils s’assoupissent, et qu’ils dorment un sommeil éternel, et qu’ils ne se relèvent point, dit le Seigneur.
40 “Zan sauko da su kamar tumaki zuwa mayanka, kamar raguna da bunsurai.
Je les conduirai comme des agneaux pour servir de victimes, comme des béliers avec des chevreaux.
41 “Yadda za a ci Sheshak, taƙamar duniya duka za tă daina! Babilon za tă zama abar ƙyama a cikin al’ummai!
Comment a été prise Sésach? et comment a été emportée la ville illustre dans toute la terre? comment Babylone est-elle devenue un objet de stupeur parmi les nations?
42 Teku zai malalo a kan Babilon, raƙumansa masu hauka za su rufe ta.
La mer est montée sur Babylone; par la multitude de ses efforts elle a été couverte.
43 Garuruwanta sun zama abin kufai, za tă zama hamada inda ba ruwa, ƙasar da ba mazauna, ba kuma mutumin da zai ratsa ta cikinta.
Ses cités sont devenues un objet de stupeur, une terre inhabitable et déserte, une terre dans laquelle nul n’habite, et où ne passe pas le fils d’un homme.
44 Zan hukunta Bel a Babilon, in sa ya yi aman abin da ya haɗiye. Ƙasashe ba za su ƙara bumbuntowa wurinsa ba. Katangan Babilon kuwa za tă rushe!
Et je visiterai Bel à Babylone, et je ferai sortir de sa bouche ce qu’il avait absorbé; et les nations n’afflueront plus vers lui, puisque le mur même de Babylone croulera.
45 “Ku fito daga cikinta, jama’ata! Ku tsere da ranku! Ku tsere daga zafin fushin Ubangiji.
Sortez d’au milieu d’elle, mon peuple, afin que chacun sauve son âme de la colère du Seigneur;
46 Kada zuciyarku tă yi suwu ko ku ji tsoro sa’ad da aka ji labarin a ƙasar, labari guda a wannan shekara, wani kuma a ta biye, labarin hargitsi a ƙasar mai mulki ya tasar wa mai mulki.
Et pour que votre cœur ne mollisse pas, et que vous ne craigniez pas le bruit qui s’entendra sur la terre; car dans une année viendra une nouvelle; et après cette année, une autre nouvelle; et l’iniquité sur la terre, et dominateur sur dominateur.
47 Gama kwanaki tabbatacce suna zuwa, sa’ad da zan hukunta gumakan Babilon, zan kunyatar da dukan ƙasar kuma matattunta duk za su kwanta a cikinta.
À cause de cela, voilà que des jours viennent, et je visiterai les images taillées au ciseau de Babylone; et toute sa terre sera couverte de confusion, et tous ses tués tomberont au milieu d’elle.
48 Sa’an nan sama da ƙasa da dukan abin da yake cikinsu, za su yi sowa ta murna a kan Babilon, gama daga arewa masu hallakarwa su auko mata,” in ji Ubangiji.
Et les cieux et la terre et tout ce qui est en eux loueront le Seigneur au sujet de Babylone; parce que ses spoliateurs viendront de l’aquilon, dit le Seigneur.
49 “Babilon za tă fāɗi saboda kisassun mutanen Isra’ila, kamar dai yadda kisassu dukan duniya suka fāɗi saboda Babilon.
Et comme Babylone a fait que des tués sont tombés en Israël, ainsi de Babylone tomberont des tués dans toute la terre.
50 Ku waɗanda kuka tsere wa takobi, ku gudu kada ku tsaya! Ku tuna da Ubangiji a ƙasa mai nesa, ku kuma yi ta tunani a kan Urushalima.”
Vous qui avez fui le glaive, venez, ne vous arrêtez point; souvenez-vous de loin du Seigneur, et que Jérusalem monte dans votre cœur.
51 “Mun sha kunya saboda zargin da ake yi mana kunya ta rufe mu, domin baƙi sun shiga tsarkakan wurare na gidan Ubangiji.”
Nous avons été confondus, parce que nous avons entendu l’opprobre; l’ignominie a couvert nos faces, parce que sont venus des étrangers contre le sanctuaire de la maison du Seigneur.
52 “Amma kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan hukunta gumakanta, da kuma a dukan ƙasarta waɗanda aka yi wa rauni, za su yi nishi.
À cause de cela, voilà que des jours viennent, dit le Seigneur, et je visiterai ses images taillées au ciseau; et dans toute sa terre mugiront des blessés.
53 Ko da Babilon za tă kai sararin sama ne, ta gina kagaranta mai ƙarfi, duk da haka zan aiki masu hallakarwa a kanta,” in ji Ubangiji.
Quand Babylone serait montée jusqu’au ciel, et qu’elle aurait affermi en haut sa force, de moi lui viendront ses dévastateurs, dit le Seigneur.
54 “Ku ji muryar kuka daga Babilon, Da hargowar babbar hallakarwa daga ƙasar Babiloniyawa!
Voix de clameur qui s’élève de Babylone, et grande destruction de la terre des Chaldéens;
55 Gama Ubangiji zai rushe Babilon, zai sa ta ƙame bakinta na alfarma. Sojoji za su yi ta kutsawa kamar raƙuman ruwa; suna tā da muryoyinsu.
Parce que le Seigneur a ravagé Babylone, et détruit en elle une grande voix; et leurs flots retentiront comme de grandes eaux; leur voix a eu un retentissement;
56 Gama mai hallakarwa ya auka wa Babilon, a kama sojojinta, a kuma kakkarya bakkunansu. Gama Ubangiji shi Allah ne mai sakayya; zai yi sakayya sosai.
Parce qu’il est venu sur elle, c’est-à-dire sur Babylone, un spoliateur, et que ses braves ont été pris, et que leur arc a perdu sa force; parce que le Seigneur, puissant vengeur, la rétribuera très certainement.
57 Zan sa mahukuntanta da masu hikimarta, gwamnoninta, shugabanninta da sojojinta su sha su bugu; za su dinga yin barcin da ba za su farka ba,” in ji Sarkin, mai suna Ubangiji Maɗaukaki.
Et j’enivrerai ses princes, et ses sages, et ses chefs, et ses magistrats, et ses braves; et ils dormiront un sommeil éternel; et ils ne se réveilleront pas, dit le roi; le Seigneur des armées est son nom.
58 Ni Ubangiji Maɗaukaki, na ce, “Za a baje katangan nan na Babilon mai kauri za a kuma ƙone dogayen ƙyamarenta da wuta; mutane sun wahalar da kansu a banza, al’umma sun yi wahala kawai domin wutar lalata.”
Voici ce que dit le Seigneur des armées: Ce mur très large de Babylone sera sapé entièrement; et ses portes élevées seront brûlées par le feu; les travaux des peuples seront réduits au néant, et ceux des nations seront livrés au feu et périront entièrement.
59 Jawabin da annabi Irmiya ya ba Serahiya, ɗan Neriya, wato, jikan Ma’asehiya, lokacin da ya tafi tare da Zedekiya, Sarkin Yahuda, zuwa Babilon a shekara ta huɗu ta mulkinsa. Serahiya shi ne shugaba mai lura da gidajen saukar baƙi.
Ordre que donna Jérémie, le prophète, à Saraïas, fils de Nérias, lorsqu’il allait avec le roi Sédécias, à Babylone, la quatrième année de son règne; or Saraïas était prince de la prophétie.
60 Irmiya ya rubuta a littafi dukan masifun da za su auko wa Babilon, wato, dukan wannan magana da aka rubuta a kan Babilon.
Et Jérémie écrivit tout le mal qui devait venir sur Babylone dans son livre, toutes ces paroles qui ont été écrites contre Babylone.
61 Irmiya kuwa ya ce wa Serahiya, “Lokacin da ka kai Babilon, sai ka karanta dukan maganan nan.
Et Jérémie dit à Saraïas: Lorsque tu seras venu à Babylone, et que tu auras vu, et que tu auras lu toutes ces paroles,
62 Ka kuma ce, ‘Ya Ubangiji, kai ne ka yi magana a kan wannan wuri, cewa za ka lalatar da shi, har ba abin da zai zauna a ciki, mutum ko dabba. Wurin zai zama kufai har abada.’
Tu diras: Seigneur, c’est vous qui avez parlé contre ce lieu-ci, afin de le perdre entièrement, pour qu’il n’y ait personne qui l’habite depuis l’homme jusqu’à la bête, et afin qu’il soit une éternelle solitude.
63 Sa’ad da ka gama karanta wannan littafi, sai ka ɗaura wa littafin dutse, sa’an nan ka jefar da shi tsakiyar Kogin Yuferites.
Et lorsque tu auras achevé de lire ce livre, tu y attacheras une pierre et tu le jetteras au milieu de l’Euphrate;
64 Sa’an nan ka ce, ‘Haka Babilon za tă nutse, ba za tă ƙara tashi ba saboda masifar da zan kawo mata. Mutanenta kuwa za su fāɗi.’” Wannan shi ne ƙarshen kalmomin Irmiya.
Et tu diras: Ainsi sera submergée Babylone, et elle ne se relèvera pas, à cause de l’affliction que moi j’amène sur elle; et elle sera détruite. Jusqu’ici ce sont les paroles de Jérémie.