< Irmiya 51 >

1 Ubangiji ya ce, “Ga shi, zan zuga ruhun mai hallakarwa a kan Babilon da mutanen Leb Kamai.
This is what Yahweh says: “I will inspire/motivate [an army] to destroy Babylon [like a powerful] wind [MET], and [also] to destroy the people of Babylonia.
2 Zan aika da baƙi zuwa Babilon su casa ta su kuma yi kaca-kaca da ƙasarta; za su yi hamayya da ita a kowane gefe a ranar masifarta.
I will send a foreign army to come to get rid of Babylonia [like a strong wind] that blows away chaff. They will attack from every direction on that day of disaster.
3 Kada ku bar maharbi yă ja bakansa, kada kuma ku bari yă sa kayan yaƙinsa. Kada ku rage samarinta, ku hallaka sojojinta ƙaf.
[I will tell them, ] ‘Do not allow the archers [of Babylon] to [have time to] put on their armor or draw their bows. Do not spare the young men of Babylon. Completely destroy their army.’
4 Za su fāɗi matattu a ƙasar Babilon, da munanan raunuka a titunanta.
Their soldiers will fall dead in Babylonia; [they will die after being] wounded in the streets.
5 Gama Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila da Yahuda bai yashe su ba, ko da yake ƙasarsu cike da take da laifi a gaban Mai Tsarki na Isra’ila.
[I, ] the Commander of the armies of angels, the Israelis’ God, have not abandoned Israel and Judah. [Even though] their land was full of people who sinned against [me], the Holy God of Israel, I am still their God.
6 “Ku gudu daga cikin Babilon! Bari kowa yă ceci ransa! Kada a hallaka saboda zunubanta. Gama lokaci ne don ramuwar Ubangiji, zai sāka mata bisa ga alhakinta.
[You people of Israel and Judah, ] flee from Babylon! Run away from there! Do not stay there and be killed when I punish [the people of Babylon]! It will be the time when I will get revenge; I will do to them what they deserve.
7 Babilon ta zama ƙoƙon zinariya a hannun Ubangiji, ta sa dukan duniya ta yi maye. Ƙasashe sun sha ruwan inabinta, saboda haka yanzu sun haukace.
Babylon has been [like] [MET] a gold cup in my hand, [a cup that is full of wine] that caused people all over the earth [who drank some of it to become] drunk. [It is as though] the [rulers of] the nations drank the wine from Babylon, and it caused them to become crazy.
8 Farat ɗaya Babilon za tă fāɗi ta farfashe. Ku yi kuka dominta! Ku samo mata magani saboda azabarta; wataƙila za a iya warkar da ita.
But suddenly Babylon will be conquered. [You foreigners who live in Babylon, ] weep for its people. Give them medicine for their wounds; perhaps they can be healed.”
9 “‘Da mun warkar da Babilon, amma ba za tă warke ba; mu ƙyale ta kowane yă koma garinsu, gama hukuncinta ya kai sammai, ya yi tsawo kamar gizagizai.’
We [foreigners] would have [tried to] heal them, but [now] they cannot be healed. [So we will not try to help them; ] we will abandon them, and return to our own lands, because [it is as though] the punishment they are receiving is so great that it reaches up to the clouds in sky, [so great that no one can measure it].
10 “‘Ubangiji ya baratar da mu; zo mu tafi mu yi shelarsa a Sihiyona mu faɗa abin da Ubangiji Allahnmu ya yi.’
Yahweh has (vindicated us/shown that we were right); [so] let’s proclaim in Jerusalem everything that Yahweh our God has done [for us].
11 “Ku wasa kibiyoyi, ku ɗauko garkuwoyi! Ubangiji ya zuga sarakunan Medes, domin niyyarsa ce yă hallaka Babilon. Ubangiji zai yi ramuwa, zai yi ramuwa saboda haikalinsa.
[You enemy soldiers, ] sharpen your arrows! Lift up your shields, [because] Yahweh has incited your kings of Media [and Persia to march with their armies] to Babylon and to destroy it. That is how Yahweh will get revenge on [those foreigners who entered] his temple [in Jerusalem] and defiled it.
12 Ku tā da tuta gāba da katangan Babilon! Ku ƙara matsara, ku kafa masu tsaro, ku shirya kwanto! Ga shi, Ubangiji zai aikata abin da ya faɗa umarninsa a kan mutanen Babilon.
Lift up a battle flag close to the walls of Babylon! (Reinforce the/Appoint more) guards, and tell the watchmen to stand [in their positions]! Prepare an ambush, because Yahweh is about to accomplish all that he has planned to do to the people of Babylon.
13 Ke da kike zama kusa da ruwaye da kike kuma wadatar dukiya, ƙarshenki ya zo, lokaci ya yi da za a kau da ke.
Babylon is [a city] near the great [Euphrates] River, a city in which there are many rich people, but it is time for Babylon to be finished; the time [for the city] to exist is ended.
14 Ubangiji Maɗaukaki ya rantse da zatinsa, ya ce Tabbatacce zan cika ka da mutane kamar fāra, za su kuwa yi sowa don nasara a kanka.
The Commander of the armies of angels has solemnly promised, using his own name, “Your cities will be filled with your enemies; I will cause them to be like [SIM] a swarm of locusts; and they will shout triumphantly [when they conquer your city].”
15 “Ya halicci ƙasa ta wurin ikonsa; ya kafa duniya ta wurin hikimarsa, ya kuma shimfiɗa sammai ta wurin fahiminsa.
Yahweh created the earth by his power; he established it by his wisdom, and he stretched out the sky by his understanding.
16 Sa’ad da ya yi tsawa ruwan da suke sammai sukan yi ruri; yakan sa gizagizai su tashi daga ƙarshen duniya. Yakan tura walƙiya tare da ruwan sama yakan kuma saki iska daga cikin taskokinsa.
When he speaks loudly, there is thunder in the sky; he causes clouds to form in every part of the earth. He sends lightning with the rain and releases the winds from his storehouses.
17 “Kowane mutum marar azanci ne kuma ba shi da sani; kowane maƙerin zinariya yakan sha kunya daga wurin gumakansa. Siffofinsa na ƙarya ne; babu numfashi a cikinsu.
People are senseless, and they know very little [HYP]; those who make idols are [always] disappointed, because their idols [do nothing for them]. The images/statues that they make are not real [gods]; they are lifeless.
18 Su marasa amfani ne, abubuwan ba’a ne kawai; sa’ad da lokacin hukuncinsu ya kai, za su hallaka.
Idols are worthless; they deserve to be ridiculed; there will be a time when they will [all] be destroyed.
19 Wanda yake na wajen Yaƙub ba kamar waɗannan ba ne, gama shi ne Mahalicci dukan abu, har da kabilar abin gādonsa, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
But the God whom [we] Israelis [worship] is not like those [idols]; he is the one who created everything [that exists]; [we], the people of Israel, belong to him; his name is ‘the Commander of the armies of angels’.
20 “Kai ne kulkin yaƙina, kayan yaƙina, da kai ne na ragargaza ƙasashe, da kai ne na hallaka mulkoki,
Yahweh says [about the army of Babylonia] (OR, [about a nation that will attack Babylonia)], “You have been [like] [MET] my battle-axe and war-club; with your [power] I have shattered nations and destroyed [many] kingdoms.
21 da kai ne na ragargaza doki da mahayi, da kai ne na ragargaza keken yaƙin da matuƙi,
With your [power] I have shattered armies [of other nations]: I destroyed [their] horses and their riders, [their] chariots and [their] chariot-drivers.
22 da kai ne na ragargaza miji da mata, da kai ne na ragargaza tsoho da saurayi, da kai ne na ragargaza saurayi da budurwa,
With your [power] I shattered men and women, old people and children, young men and young women.
23 da kai ne na ragargaza makiyayi da garke, da kai ne na ragargaza manoma da dawakan noma, da kai ne na ragargaza masu mulki da shugabanni.
With your [power] I shattered shepherds and their flocks [of sheep], farmers and their oxen, governors and [their] officials.”
24 “Zan sāka wa Babilon da dukan mazaunan Babilon a idanunku saboda dukan muguntar da suka aikata a Sihiyona,” in ji Ubangiji.
But, Yahweh [also] says, “[Soon] I will repay/punish [you] people in Babylon and in the rest of Babylonia for all the evil things that you have done in Jerusalem.
25 “Ga shi, ina gāba da kai, ya ke dutse mai hallakarwa, wadda ta hallaka duniya duka,” in ji Ubangiji. “Zan miƙa hannuna gāba da ke, zan mirgina ƙasa daga ƙwanƙolin dutse, zan maishe ki ƙonannen dutse.
[Babylonia is] [APO] like [MET] a great mountain [from which bandits descend] to (plunder/steal things from) people all over the earth. But I, Yahweh, am the enemy of you [people of Babylonia]. I will raise my fist to strike you. I will knock you down from the cliffs and cause you to be [only] a huge pile of burned rubble.
26 Ba za a ɗauki dutsen yin kusurwa daga gare ki ba ko na kafa harsashen gini, gama za ki zama marar amfani har abada,” in ji Ubangiji.
Your [city] will be abandoned forever; [even] the stones in your [city] will never [again] be used for buildings. [Your city will be completely destroyed].”
27 “Ku tā da tuta a ƙasa! Ku busa ƙahoni a cikin ƙasashe! Ku shirya ƙasashe don yaƙi da ita, ku kira waɗannan mulkokin gāba da ita. Ararat, Minni, da Ashkenaz. A naɗa shugaba gāba da ita; ku shirya dawakai kamar fāra.
[Tell] the nations to lift up a battle flag! [Tell them to] shout the battle-cry! Gather all their armies to fight against Babylon! Prepare the nations to attack Babylon. Summon [the armies of] the kingdoms [north of Babylonia]—from Ararat, Minni, and Ashkenaz. Appoint a commander for them, and bring [a great number of] horses; [there must be a huge number of horses]; that [huge number] will resemble [SIM] a swarm of locusts.
28 Ku shirya ƙasashe don yaƙi da ita, sarakunan Medes, gwamnoninsu da dukan masu shugabancinsu da kowace ƙasar da take ƙarƙashin mulkinsu.
Prepare the [armies of other nations], armies that will be led by the kings of Media [and Persia], their governors and [their] officials.
29 Ƙasa ta girgiza tana makyarkyata saboda nufin Ubangiji na gāba da Babilon ya tabbata, nufinsa na mai da ƙasar Babilon kufai don kada kowa yă zauna a can.
[When they attack Babylon, it will be as though] the earth will shake and writhe [in pain], because [those armies] will accomplish everything that Yahweh has planned to do to Babylon; they will destroy it completely, [with the result that] no one will live there [again].
30 Sojojin Babilon sun daina yaƙi, suna zaune a cikin kagaransu. Ƙarfinsu ya ƙare, sun zama mata. An sa wa wuraren zamanta wuta, an karya ƙyamaren ƙofofin garinta.
[When their enemies attack], the strongest warriors in Babylon will not fight. They will remain in their barracks, without any strength. They will be as timid/weak as [SIM] women. [The enemy soldiers] will burn the buildings in the city and pull down the bars [of the city gates].
31 Maguji yana biye da maguji a guje, jakada yana biye da jakada, don su faɗa wa sarkin Babilon, cewa an ci birninsa a kowane gefe.
Messengers will go quickly, one after another, to tell the king that his city has been captured.
32 An ƙwace mashigai aka ƙone fadamu da wuta, sojoji kuma suka giggice.”
The places at which people can cross the river [to escape from the city] will be blocked. The dry reeds in the marshes/swamps will be set on fire, and the soldiers of Babylon will be terrified.
33 Ni Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila na ce, “’Yar Babilon kamar daɓen masussuka a lokacin da ake sussuka, ba da daɗewa ba lokacin girbe ta zai zo.”
This is what the Commander of the armies of angels, the God whom [we] Israelis [worship], says; “Babylon is like [SIM] wheat on the ground where it is about to be threshed by [animals] tramping on it. Very soon [their enemies] will trample on [the city of] Babylon [MET].”
34 “Nebukadnezzar sarkin Babilon ya cinye mu, ya sa muka rikice, ya maishe mu kamar tulun da babu kome a cikinsa. Ya cinye mu kamar yadda dodon ruwa yakan yi ya kuma cika cikinsa da kayan marmarinmu, sa’an nan kuma ya yi amanmu.
[The army of] Nebuchadnezzar, the King of Babylon, has attacked and crushed us [Israeli people], and we have no strength [left]. [It is as though] they have swallowed us like a [great] monster that filled its belly with all our tasty parts, and then has spit out [what it did not like].
35 Bari abin da aka yi wa jikinmu yă kasance a bisa Babilon,” in ji mazaunan Sihiyona. “Bari jininmu yă kasance a kan waɗanda suke zama a Babilon,” in ji Urushalima.
[So] the people of [PRS] Jerusalem say [to Yahweh], “Cause the people of Babylon to suffer like they caused us to suffer! Cause the people of Babylonia to be punished for killing [MTY] our people!”
36 Saboda haka ga abin da Ubangiji ya ce, “Duba, zan tsaya muku, zan ɗaukar muku fansa, zan sa tekunta kafe in kuma sa maɓulɓulanta su ƙafe.
And this is what Yahweh replies to the people of Jerusalem: “I will [be like your lawyer to] defend you, and I will avenge you. I will dry up the river in Babylon and [all] the springs of water.
37 Babilon za tă zama tarin juji, wurin zaman diloli, abin ƙyama da abar ba’a, inda ba kowa.
Babylon will become a heap of ruins, a place where jackals/wolves live. It will become a place that people are horrified about and will ridicule; it will be a place where no one lives.
38 Mutanenta duk suna ruri kamar zakoki, suna gurnani kamar’ya’yan zaki.
The people of Babylon will [all] roar like young lions; they will growl like baby lions.
39 Amma sa’ad da aka farkar da su, zan yi musu biki in sa su sha su bugu, domin yi sowa da dariya, sa’an nan su shiga barcin da ba za su farka ba,” in ji Ubangiji.
But while they are extremely hungry, I will prepare a [different kind of] feast for them. [It is as though] I will cause them to drink wine until they are very drunk, [with the result that] they will fall asleep. But they will never wake up from that sleep!
40 “Zan sauko da su kamar tumaki zuwa mayanka, kamar raguna da bunsurai.
I will bring them down to a place where they will be slaughtered, like [SIM] [someone who takes] lambs or rams or goats [to where they will be slaughtered for sacrifices].
41 “Yadda za a ci Sheshak, taƙamar duniya duka za tă daina! Babilon za tă zama abar ƙyama a cikin al’ummai!
People all over the earth [now] (honor/praise) Babylon; they say that it is a great city. But I will cause it to become a [place about which people of all] nations are horrified.
42 Teku zai malalo a kan Babilon, raƙumansa masu hauka za su rufe ta.
The [enemies of Babylon] will cover the city [like] huge waves of the sea [DOU].
43 Garuruwanta sun zama abin kufai, za tă zama hamada inda ba ruwa, ƙasar da ba mazauna, ba kuma mutumin da zai ratsa ta cikinta.
The towns in Babylonia will become ruins, Babylonia will become a dry desert area. It will be a land in which no one lives and which no one walks through.
44 Zan hukunta Bel a Babilon, in sa ya yi aman abin da ya haɗiye. Ƙasashe ba za su ƙara bumbuntowa wurinsa ba. Katangan Babilon kuwa za tă rushe!
And I will punish Bel, [the god that the people] of Babylon [worship], and I will cause the people to give back what they have stolen [MET]. [People of other] nations will no longer come to [worship] Bel. And the walls of Babylon will collapse.”
45 “Ku fito daga cikinta, jama’ata! Ku tsere da ranku! Ku tsere daga zafin fushin Ubangiji.
[Yahweh also says, ] “My people, come out of Babylon! Run away from there! Run, because [I], Yahweh, am extremely angry [MTY] [with the people of Babylon, and I will get rid of them]!
46 Kada zuciyarku tă yi suwu ko ku ji tsoro sa’ad da aka ji labarin a ƙasar, labari guda a wannan shekara, wani kuma a ta biye, labarin hargitsi a ƙasar mai mulki ya tasar wa mai mulki.
Do not be discouraged/worried [IDM] or afraid when you hear reports [about what is happening in Babylon]. People will report rumors like that every year, rumors about violent things being done in the land, and rumors about leaders fighting against each other.
47 Gama kwanaki tabbatacce suna zuwa, sa’ad da zan hukunta gumakan Babilon, zan kunyatar da dukan ƙasar kuma matattunta duk za su kwanta a cikinta.
But it will soon be the time for me to get rid of the idols in Babylon. [People all over] the land will be ashamed [because of being defeated]; and the corpses of their [soldiers] will lie in the streets.
48 Sa’an nan sama da ƙasa da dukan abin da yake cikinsu, za su yi sowa ta murna a kan Babilon, gama daga arewa masu hallakarwa su auko mata,” in ji Ubangiji.
Then all [the angels in] heaven and all the [people on] [PRS] the earth will rejoice, because from the north will come [armies] that will destroy Babylon.
49 “Babilon za tă fāɗi saboda kisassun mutanen Isra’ila, kamar dai yadda kisassu dukan duniya suka fāɗi saboda Babilon.
Like [the soldiers of Babylon] killed the people of Israel and [also] killed others all over the world [HYP], [the people of] Babylon must also be killed.
50 Ku waɗanda kuka tsere wa takobi, ku gudu kada ku tsaya! Ku tuna da Ubangiji a ƙasa mai nesa, ku kuma yi ta tunani a kan Urushalima.”
You [Israeli people] who have not been killed [MTY], get out of Babylon! Do not wait! [Even though you are in a land] far away [from Israel], think about Yahweh, and think about Jerusalem!”
51 “Mun sha kunya saboda zargin da ake yi mana kunya ta rufe mu, domin baƙi sun shiga tsarkakan wurare na gidan Ubangiji.”
[The Israeli people say], “We are ashamed. We are completely disgraced [DOU], because foreigners have entered Yahweh’s temple [and (defiled it/caused it to become unfit for worship)].”
52 “Amma kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan hukunta gumakanta, da kuma a dukan ƙasarta waɗanda aka yi wa rauni, za su yi nishi.
Yahweh replies, “[That is true], but there will soon be a time when I will destroy the idols in Babylon, and throughout Babylonia there will be wounded people who will groan.
53 Ko da Babilon za tă kai sararin sama ne, ta gina kagaranta mai ƙarfi, duk da haka zan aiki masu hallakarwa a kanta,” in ji Ubangiji.
Even if [the walls around] Babylon could extend up to the sky, and if its walls/fortifications were extremely strong, I will send [armies] that will destroy the city. [That will surely happen because I, ] Yahweh, have said it.”
54 “Ku ji muryar kuka daga Babilon, Da hargowar babbar hallakarwa daga ƙasar Babiloniyawa!
Listen to [the people of] Babylon crying [for help]! And listen to the sounds of things being destroyed all over Babylonia!
55 Gama Ubangiji zai rushe Babilon, zai sa ta ƙame bakinta na alfarma. Sojoji za su yi ta kutsawa kamar raƙuman ruwa; suna tā da muryoyinsu.
Yahweh will be destroying Babylon. He will cause the loud noises in the city to cease.
56 Gama mai hallakarwa ya auka wa Babilon, a kama sojojinta, a kuma kakkarya bakkunansu. Gama Ubangiji shi Allah ne mai sakayya; zai yi sakayya sosai.
Enemy troops will surge against the city like [SIM] a great wave. They will capture the city’s mighty soldiers and break their weapons. [That will happen] because Yahweh is a God who punishes [his enemies] justly; he will punish them as they deserve.
57 Zan sa mahukuntanta da masu hikimarta, gwamnoninta, shugabanninta da sojojinta su sha su bugu; za su dinga yin barcin da ba za su farka ba,” in ji Sarkin, mai suna Ubangiji Maɗaukaki.
The king, the Commander of the armies of angels says, “I will cause the city officials and wise men, the army captains and soldiers [in Babylon] to become drunk. They will fall asleep, but they will never wake up [again]!”
58 Ni Ubangiji Maɗaukaki, na ce, “Za a baje katangan nan na Babilon mai kauri za a kuma ƙone dogayen ƙyamarenta da wuta; mutane sun wahalar da kansu a banza, al’umma sun yi wahala kawai domin wutar lalata.”
Yahweh also says, “The thick walls around Babylon will be flattened to the ground. The city gates will be burned. People [from other countries] will work hard [to save the city], but it will be (in vain/useless), because everything [that they have built] will be destroyed by fire.”
59 Jawabin da annabi Irmiya ya ba Serahiya, ɗan Neriya, wato, jikan Ma’asehiya, lokacin da ya tafi tare da Zedekiya, Sarkin Yahuda, zuwa Babilon a shekara ta huɗu ta mulkinsa. Serahiya shi ne shugaba mai lura da gidajen saukar baƙi.
Seraiah was the man who made arrangements for the King of Babylon [whenever he traveled]. He was the son of Neraiah and grandson of Mahseiah. When he was about to go to Babylon with King Zedekiah, after Zedekiah had been ruling Judah for almost four years, the prophet Jeremiah gave him a message.
60 Irmiya ya rubuta a littafi dukan masifun da za su auko wa Babilon, wato, dukan wannan magana da aka rubuta a kan Babilon.
Jeremiah had written on a scroll a list of all the disasters that he had written about, disasters that would soon occur in Babylon.
61 Irmiya kuwa ya ce wa Serahiya, “Lokacin da ka kai Babilon, sai ka karanta dukan maganan nan.
He said to Seraiah, “When you arrive in Babylon, read [aloud] everything that I have written [on this scroll].
62 Ka kuma ce, ‘Ya Ubangiji, kai ne ka yi magana a kan wannan wuri, cewa za ka lalatar da shi, har ba abin da zai zauna a ciki, mutum ko dabba. Wurin zai zama kufai har abada.’
Then pray, ‘Yahweh, you said that you will thoroughly destroy Babylon, with the result that people and animals will no [longer] live there. You said that it will be desolate forever.’
63 Sa’ad da ka gama karanta wannan littafi, sai ka ɗaura wa littafin dutse, sa’an nan ka jefar da shi tsakiyar Kogin Yuferites.
[Then], when you have finished reading [what I have written on] the scroll, tie it to a [heavy] stone and throw it into the Euphrates [River].
64 Sa’an nan ka ce, ‘Haka Babilon za tă nutse, ba za tă ƙara tashi ba saboda masifar da zan kawo mata. Mutanenta kuwa za su fāɗi.’” Wannan shi ne ƙarshen kalmomin Irmiya.
Then say, ‘In the same way, Babylon [and its people] will disappear and never exist again, because of the disasters that Yahweh will cause to occur there’” That is the end of Jeremiah’s messages.

< Irmiya 51 >