< Irmiya 51 >

1 Ubangiji ya ce, “Ga shi, zan zuga ruhun mai hallakarwa a kan Babilon da mutanen Leb Kamai.
Thus saith Jehovah: Behold, I will raise up against Babylon, And against them that dwell in the midst of mine adversaries, A destroying wind;
2 Zan aika da baƙi zuwa Babilon su casa ta su kuma yi kaca-kaca da ƙasarta; za su yi hamayya da ita a kowane gefe a ranar masifarta.
And I will send against Babylon winnowers, And they shall winnow her, and empty her land; For they shall come against her on every side.
3 Kada ku bar maharbi yă ja bakansa, kada kuma ku bari yă sa kayan yaƙinsa. Kada ku rage samarinta, ku hallaka sojojinta ƙaf.
Against him that bendeth, let the archer bend his bow, And against him that lifteth himself up in his brigandine! And spare ye not her young men; Destroy ye utterly her whole host!
4 Za su fāɗi matattu a ƙasar Babilon, da munanan raunuka a titunanta.
Thus shall they fall down slain in the land of the Chaldaeans, And thrust through in her streets.
5 Gama Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila da Yahuda bai yashe su ba, ko da yake ƙasarsu cike da take da laifi a gaban Mai Tsarki na Isra’ila.
For Israel is not forsaken, nor Judah abandoned of his God, of Jehovah of hosts; For their land is full of guilt against the Holy One of Israel.
6 “Ku gudu daga cikin Babilon! Bari kowa yă ceci ransa! Kada a hallaka saboda zunubanta. Gama lokaci ne don ramuwar Ubangiji, zai sāka mata bisa ga alhakinta.
Flee ye out of Babylon, And save ye every man his life, That ye be not cut off in her punishment! For this is the time of Jehovah's vengeance; He will render to her a recompense.
7 Babilon ta zama ƙoƙon zinariya a hannun Ubangiji, ta sa dukan duniya ta yi maye. Ƙasashe sun sha ruwan inabinta, saboda haka yanzu sun haukace.
Babylon has been a golden cup in the hand of Jehovah, That made all the earth drunken; The nations have drunken of her wine, Therefore the nations are mad.
8 Farat ɗaya Babilon za tă fāɗi ta farfashe. Ku yi kuka dominta! Ku samo mata magani saboda azabarta; wataƙila za a iya warkar da ita.
Babylon is suddenly fallen, and broken; Howl ye over her; Bring ye balm for her wounds, If so be she may be healed.
9 “‘Da mun warkar da Babilon, amma ba za tă warke ba; mu ƙyale ta kowane yă koma garinsu, gama hukuncinta ya kai sammai, ya yi tsawo kamar gizagizai.’
“We would have healed Babylon, But she cannot be healed. Forsake her, and let us go every one to his own country! For her punishment reacheth to the heavens, And ascendeth even to the skies.”
10 “‘Ubangiji ya baratar da mu; zo mu tafi mu yi shelarsa a Sihiyona mu faɗa abin da Ubangiji Allahnmu ya yi.’
Jehovah hath brought forth our deliverance; Come ye, and let us declare in Zion The work of Jehovah our God.
11 “Ku wasa kibiyoyi, ku ɗauko garkuwoyi! Ubangiji ya zuga sarakunan Medes, domin niyyarsa ce yă hallaka Babilon. Ubangiji zai yi ramuwa, zai yi ramuwa saboda haikalinsa.
Make sharp the arrows; put on the shields! Jehovah hath roused up the spirit of the kings of the Medes; For his purpose is against Babylon, to destroy it; For this is the vengeance of Jehovah, The vengeance for his temple.
12 Ku tā da tuta gāba da katangan Babilon! Ku ƙara matsara, ku kafa masu tsaro, ku shirya kwanto! Ga shi, Ubangiji zai aikata abin da ya faɗa umarninsa a kan mutanen Babilon.
Against the walls of Babylon set up a standard, Make strong the guard, appoint the watchmen, prepare the ambush! For Jehovah deviseth and doeth that which he spake Against the inhabitants of Babylon.
13 Ke da kike zama kusa da ruwaye da kike kuma wadatar dukiya, ƙarshenki ya zo, lokaci ya yi da za a kau da ke.
O thou that dwellest by great waters, That aboundest in treasures, Thine end is come; The measure of thy rapaciousness is full!
14 Ubangiji Maɗaukaki ya rantse da zatinsa, ya ce Tabbatacce zan cika ka da mutane kamar fāra, za su kuwa yi sowa don nasara a kanka.
Jehovah of hosts hath sworn by himself, [[saying, ]] Surely I will fill thee with men, as with caterpillars, Who shall raise the war-shout against thee.
15 “Ya halicci ƙasa ta wurin ikonsa; ya kafa duniya ta wurin hikimarsa, ya kuma shimfiɗa sammai ta wurin fahiminsa.
He made the earth by his power, He established the world by his wisdom, And by his understanding he spread out the heavens.
16 Sa’ad da ya yi tsawa ruwan da suke sammai sukan yi ruri; yakan sa gizagizai su tashi daga ƙarshen duniya. Yakan tura walƙiya tare da ruwan sama yakan kuma saki iska daga cikin taskokinsa.
When he uttereth his voice there is an abundance of water in the heavens; He causeth clouds to ascend from the ends of the earth; He bringeth the wind from his storehouses.
17 “Kowane mutum marar azanci ne kuma ba shi da sani; kowane maƙerin zinariya yakan sha kunya daga wurin gumakansa. Siffofinsa na ƙarya ne; babu numfashi a cikinsu.
Brutish is every man who hath not this knowledge; By his images is every founder put to shame; For his molten work is deceit; There is no breath in it.
18 Su marasa amfani ne, abubuwan ba’a ne kawai; sa’ad da lokacin hukuncinsu ya kai, za su hallaka.
They are vanity, deceptive work; In the time of their punishment shall they perish.
19 Wanda yake na wajen Yaƙub ba kamar waɗannan ba ne, gama shi ne Mahalicci dukan abu, har da kabilar abin gādonsa, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
Not like them is he who is the portion of Jacob; He is the former of all things, And Israel is his allotted inheritance. Jehovah of hosts is his name.
20 “Kai ne kulkin yaƙina, kayan yaƙina, da kai ne na ragargaza ƙasashe, da kai ne na hallaka mulkoki,
Thou hast been to me my battle-hammer, My weapon of war. And with thee I broke in pieces the nations, And with thee I destroyed the kingdoms.
21 da kai ne na ragargaza doki da mahayi, da kai ne na ragargaza keken yaƙin da matuƙi,
And with thee I broke in pieces the horse and his rider, And with thee I broke in pieces the chariot and its driver.
22 da kai ne na ragargaza miji da mata, da kai ne na ragargaza tsoho da saurayi, da kai ne na ragargaza saurayi da budurwa,
With thee I broke in pieces man and woman, And with thee I broke in pieces the old and the young, And with thee I broke in pieces the young man and the maiden.
23 da kai ne na ragargaza makiyayi da garke, da kai ne na ragargaza manoma da dawakan noma, da kai ne na ragargaza masu mulki da shugabanni.
With thee I broke in pieces the shepherd and his flock, And with thee I broke in pieces the husbandman and his team; And with thee I broke in pieces prefects and governors.
24 “Zan sāka wa Babilon da dukan mazaunan Babilon a idanunku saboda dukan muguntar da suka aikata a Sihiyona,” in ji Ubangiji.
But now before your eyes will I repay to Babylon, And to all the inhabitants of Chaldaea, All the evil which they have done in Zion, saith Jehovah.
25 “Ga shi, ina gāba da kai, ya ke dutse mai hallakarwa, wadda ta hallaka duniya duka,” in ji Ubangiji. “Zan miƙa hannuna gāba da ke, zan mirgina ƙasa daga ƙwanƙolin dutse, zan maishe ki ƙonannen dutse.
O thou destroying mountain, that destroyest the whole earth, Behold, I am against thee, saith Jehovah! And I will stretch out my hand against thee, And roll thee down from the rocks, And make thee a burnt mountain,
26 Ba za a ɗauki dutsen yin kusurwa daga gare ki ba ko na kafa harsashen gini, gama za ki zama marar amfani har abada,” in ji Ubangiji.
So that none shall take from thee a corner-stone, or a foundation-stone; But thou shalt be a perpetual desolation, saith Jehovah.
27 “Ku tā da tuta a ƙasa! Ku busa ƙahoni a cikin ƙasashe! Ku shirya ƙasashe don yaƙi da ita, ku kira waɗannan mulkokin gāba da ita. Ararat, Minni, da Ashkenaz. A naɗa shugaba gāba da ita; ku shirya dawakai kamar fāra.
Set ye up a standard in the land, Sound a trumpet among the nations; Enlist the nations against Babylon, Call together against her the kingdoms of Ararat, Minni, and Ashchenaz; Appoint captains against her, Cause the horses to come up like the bristled locusts!
28 Ku shirya ƙasashe don yaƙi da ita, sarakunan Medes, gwamnoninsu da dukan masu shugabancinsu da kowace ƙasar da take ƙarƙashin mulkinsu.
Enlist ye against her the nations, The kings of the Medes, and their prefects, And all their governors, And all the lands under their dominion,
29 Ƙasa ta girgiza tana makyarkyata saboda nufin Ubangiji na gāba da Babilon ya tabbata, nufinsa na mai da ƙasar Babilon kufai don kada kowa yă zauna a can.
So that the earth shall tremble and quake! For the purpose of Jehovah against Babylon is to be fulfilled, To make the land of Babylon a desolation, without an inhabitant.
30 Sojojin Babilon sun daina yaƙi, suna zaune a cikin kagaransu. Ƙarfinsu ya ƙare, sun zama mata. An sa wa wuraren zamanta wuta, an karya ƙyamaren ƙofofin garinta.
The mighty men of Babylon refuse to fight; They remain in their stronghold; Their strength hath failed; They have become women; Her habitations are burned; Her bars are broken.
31 Maguji yana biye da maguji a guje, jakada yana biye da jakada, don su faɗa wa sarkin Babilon, cewa an ci birninsa a kowane gefe.
Courier runs to meet courier, And messenger to meet messenger, To make known to the king of Babylon, That his city is taken from end to end;
32 An ƙwace mashigai aka ƙone fadamu da wuta, sojoji kuma suka giggice.”
That the passages are taken, That the reeds are burned with fire, And that the men of war are struck with terror.
33 Ni Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila na ce, “’Yar Babilon kamar daɓen masussuka a lokacin da ake sussuka, ba da daɗewa ba lokacin girbe ta zai zo.”
For thus saith Jehovah of hosts, the God of Israel: The daughter of Babylon shall be like a thrashing-floor when it is thrashed; Yet a little while, and the time of harvest for her shall come.
34 “Nebukadnezzar sarkin Babilon ya cinye mu, ya sa muka rikice, ya maishe mu kamar tulun da babu kome a cikinsa. Ya cinye mu kamar yadda dodon ruwa yakan yi ya kuma cika cikinsa da kayan marmarinmu, sa’an nan kuma ya yi amanmu.
Nebuchadnezzar, the king of Babylon, hath devoured us; He hath made an end of us; He hath made us empty vessels; He hath swallowed us up like a dragon; He hath filled his maw with our delicacies; He hath cast us out.
35 Bari abin da aka yi wa jikinmu yă kasance a bisa Babilon,” in ji mazaunan Sihiyona. “Bari jininmu yă kasance a kan waɗanda suke zama a Babilon,” in ji Urushalima.
“The violence done to me and to my flesh be upon Babylon!” Shall the inhabitant of Zion say; And, “My blood be upon the inhabitants of Chaldaeans!” shall Jerusalem say.
36 Saboda haka ga abin da Ubangiji ya ce, “Duba, zan tsaya muku, zan ɗaukar muku fansa, zan sa tekunta kafe in kuma sa maɓulɓulanta su ƙafe.
Therefore, thus saith Jehovah: Behold, I will maintain thy cause, And take vengeance for thee; And I will dry up her sea, And make her springs dry.
37 Babilon za tă zama tarin juji, wurin zaman diloli, abin ƙyama da abar ba’a, inda ba kowa.
And Babylon shall become heaps, The dwelling-place of jackals, An astonishment and a hissing, Without an inhabitant.
38 Mutanenta duk suna ruri kamar zakoki, suna gurnani kamar’ya’yan zaki.
Together shall they roar like lions; They shall yell like lions' whelps.
39 Amma sa’ad da aka farkar da su, zan yi musu biki in sa su sha su bugu, domin yi sowa da dariya, sa’an nan su shiga barcin da ba za su farka ba,” in ji Ubangiji.
In their heat I will prepare them a drink, And will make them drunk, so that they shall rejoice, And then sleep an everlasting sleep, And awake no more, saith Jehovah.
40 “Zan sauko da su kamar tumaki zuwa mayanka, kamar raguna da bunsurai.
I will bring them down like lambs to the slaughter, Like rams with he-goats.
41 “Yadda za a ci Sheshak, taƙamar duniya duka za tă daina! Babilon za tă zama abar ƙyama a cikin al’ummai!
How is Sheshach taken! How is the praise of the whole earth fallen! How is Babylon become an astonishment among the nations!
42 Teku zai malalo a kan Babilon, raƙumansa masu hauka za su rufe ta.
The sea is come up over Babylon; With the roaring of its waves is she covered.
43 Garuruwanta sun zama abin kufai, za tă zama hamada inda ba ruwa, ƙasar da ba mazauna, ba kuma mutumin da zai ratsa ta cikinta.
Her cities have become a desolation, A dry land and a desert, A land in which no man dwelleth, And which no son of man passeth through.
44 Zan hukunta Bel a Babilon, in sa ya yi aman abin da ya haɗiye. Ƙasashe ba za su ƙara bumbuntowa wurinsa ba. Katangan Babilon kuwa za tă rushe!
I will punish Bel at Babylon, And bring forth from his mouth that which he hath swallowed, And the nations shall flow to him no more; Even the wall of Babylon shall fall.
45 “Ku fito daga cikinta, jama’ata! Ku tsere da ranku! Ku tsere daga zafin fushin Ubangiji.
Go ye out of her, my people, And save ye every man his life From the fierce anger of Jehovah!
46 Kada zuciyarku tă yi suwu ko ku ji tsoro sa’ad da aka ji labarin a ƙasar, labari guda a wannan shekara, wani kuma a ta biye, labarin hargitsi a ƙasar mai mulki ya tasar wa mai mulki.
And let not your heart faint, And fear ye not on account of the rumors which are heard in the land, When in one year a rumor cometh, And after it in another year another rumor, And violence is in the land, Ruler against ruler.
47 Gama kwanaki tabbatacce suna zuwa, sa’ad da zan hukunta gumakan Babilon, zan kunyatar da dukan ƙasar kuma matattunta duk za su kwanta a cikinta.
Therefore, behold the days come When I will punish the graven images of Babylon, And her whole land shall be confounded; And all her slain shall fall in the midst of her.
48 Sa’an nan sama da ƙasa da dukan abin da yake cikinsu, za su yi sowa ta murna a kan Babilon, gama daga arewa masu hallakarwa su auko mata,” in ji Ubangiji.
Then the heavens shall shout over Babylon, And the earth and all that is therein; For out of the North come spoilers against her, saith Jehovah.
49 “Babilon za tă fāɗi saboda kisassun mutanen Isra’ila, kamar dai yadda kisassu dukan duniya suka fāɗi saboda Babilon.
As Babylon caused the slain of Israel to fall, So at Babylon shall fall the slain of all the land.
50 Ku waɗanda kuka tsere wa takobi, ku gudu kada ku tsaya! Ku tuna da Ubangiji a ƙasa mai nesa, ku kuma yi ta tunani a kan Urushalima.”
Ye that have escaped her sword, go! Tarry not! Remember Jehovah afar off, And let Jerusalem come into your mind!
51 “Mun sha kunya saboda zargin da ake yi mana kunya ta rufe mu, domin baƙi sun shiga tsarkakan wurare na gidan Ubangiji.”
We have been confounded, because we have heard reproach; Shame hath covered our faces, For strangers have come into the sanctuaries of the house of Jehovah.
52 “Amma kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan hukunta gumakanta, da kuma a dukan ƙasarta waɗanda aka yi wa rauni, za su yi nishi.
Therefore, behold, the days come, saith Jehovah, When I will punish her graven images, And through all her land shall the wounded groan.
53 Ko da Babilon za tă kai sararin sama ne, ta gina kagaranta mai ƙarfi, duk da haka zan aiki masu hallakarwa a kanta,” in ji Ubangiji.
Though Babylon should mount up to the heavens, And make inaccessible the height of her strength, Yet from me shall spoilers come upon her, saith Jehovah.
54 “Ku ji muryar kuka daga Babilon, Da hargowar babbar hallakarwa daga ƙasar Babiloniyawa!
Hark! a cry from Babylon, Of great destruction from the land of the Chaldaeans!
55 Gama Ubangiji zai rushe Babilon, zai sa ta ƙame bakinta na alfarma. Sojoji za su yi ta kutsawa kamar raƙuman ruwa; suna tā da muryoyinsu.
For Jehovah destroyeth Babylon, And bringeth to silence her loud tumult; Their waves roar like great waters; Their tumultuous noise resounds.
56 Gama mai hallakarwa ya auka wa Babilon, a kama sojojinta, a kuma kakkarya bakkunansu. Gama Ubangiji shi Allah ne mai sakayya; zai yi sakayya sosai.
For the spoiler is come upon her, upon Babylon; And their mighty men are taken, And all their bows are broken; For Jehovah is a God of retribution; He will surely requite.
57 Zan sa mahukuntanta da masu hikimarta, gwamnoninta, shugabanninta da sojojinta su sha su bugu; za su dinga yin barcin da ba za su farka ba,” in ji Sarkin, mai suna Ubangiji Maɗaukaki.
And I will make drunk her princes, and her wise men, Her prefects, and her governors, and her mighty men; And they shall sleep an everlasting sleep, And shall no more awake, saith the King, Whose name is Jehovah of hosts.
58 Ni Ubangiji Maɗaukaki, na ce, “Za a baje katangan nan na Babilon mai kauri za a kuma ƙone dogayen ƙyamarenta da wuta; mutane sun wahalar da kansu a banza, al’umma sun yi wahala kawai domin wutar lalata.”
Thus saith Jehovah of hosts: The broad walls of Babylon shall be razed to the foundations, And her high gates shall be burned with fire; So that nations shall have labored for naught, And kingdoms have wearied themselves for fire.
59 Jawabin da annabi Irmiya ya ba Serahiya, ɗan Neriya, wato, jikan Ma’asehiya, lokacin da ya tafi tare da Zedekiya, Sarkin Yahuda, zuwa Babilon a shekara ta huɗu ta mulkinsa. Serahiya shi ne shugaba mai lura da gidajen saukar baƙi.
The word which Jeremiah the prophet commanded Seraiah, the son of Neriah, the son of Maaseiah, when he went with Zedekiah, the king of Judah, into Babylon, in the fourth year of his reign. This Seraiah was chief chamberlain.
60 Irmiya ya rubuta a littafi dukan masifun da za su auko wa Babilon, wato, dukan wannan magana da aka rubuta a kan Babilon.
And Jeremiah wrote all the evil that was to come upon Babylon in one book, all these words that are written concerning Babylon.
61 Irmiya kuwa ya ce wa Serahiya, “Lokacin da ka kai Babilon, sai ka karanta dukan maganan nan.
And Jeremiah said to Seraiah, When thou comest to Babylon, see that thou read all these words,
62 Ka kuma ce, ‘Ya Ubangiji, kai ne ka yi magana a kan wannan wuri, cewa za ka lalatar da shi, har ba abin da zai zauna a ciki, mutum ko dabba. Wurin zai zama kufai har abada.’
and say, O Jehovah, thou hast spoken against this place to destroy it, so that none shall remain in it, neither man nor beast, but that it shall remain desolate forever!
63 Sa’ad da ka gama karanta wannan littafi, sai ka ɗaura wa littafin dutse, sa’an nan ka jefar da shi tsakiyar Kogin Yuferites.
And when thou hast made an end of reading this book, bind a stone upon it, and cast it into the midst of the Euphrates,
64 Sa’an nan ka ce, ‘Haka Babilon za tă nutse, ba za tă ƙara tashi ba saboda masifar da zan kawo mata. Mutanenta kuwa za su fāɗi.’” Wannan shi ne ƙarshen kalmomin Irmiya.
and say: So shall Babylon sink, and shall not rise again from the evil which I bring upon her. And they shall utterly fail. Thus far the words of Jeremiah.

< Irmiya 51 >