< Irmiya 51 >

1 Ubangiji ya ce, “Ga shi, zan zuga ruhun mai hallakarwa a kan Babilon da mutanen Leb Kamai.
BOEIPA loh he ni a. thui. Kutcaihnah mueihla te Babylon taeng neh, Lebkamai khosa rhoek taengah ka haeng coeng ne.
2 Zan aika da baƙi zuwa Babilon su casa ta su kuma yi kaca-kaca da ƙasarta; za su yi hamayya da ita a kowane gefe a ranar masifarta.
Babylon taengah kholong rhoek neh anih aka vam te ka tueih ni. A yoethae hnin ah tah a khohmuen te a kaepvai ah a om thil vetih a hlaih ni.
3 Kada ku bar maharbi yă ja bakansa, kada kuma ku bari yă sa kayan yaƙinsa. Kada ku rage samarinta, ku hallaka sojojinta ƙaf.
A lii aka nuen loh nuen khaw nuen mai saeh lamtah a caempho te khuen saeh. Te vaengah a tongpang rhoek te hnaih kolla a caempuei khaw boeih thup uh saeh.
4 Za su fāɗi matattu a ƙasar Babilon, da munanan raunuka a titunanta.
Khalden khohmuen kah rhok neh a kawtpoeng kah a thun rhoek khaw cungku uh ni.
5 Gama Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila da Yahuda bai yashe su ba, ko da yake ƙasarsu cike da take da laifi a gaban Mai Tsarki na Isra’ila.
Amih kah Pathen caempuei BOEIPA loh Israel neh Judah te a hnong van pawt bangla Israel kah aka cim taeng lamkah moeithennah tah amih khohmuen ah cung coeng.
6 “Ku gudu daga cikin Babilon! Bari kowa yă ceci ransa! Kada a hallaka saboda zunubanta. Gama lokaci ne don ramuwar Ubangiji, zai sāka mata bisa ga alhakinta.
Babylon khui lamloh rhaelrham saeh lamtah hlang loh a hinglu te hlawt saeh. Amih kathaesainah dongah ngam boeh. BOEIPA kah tawnlohnah tue ah tah amah neh a tiing la a taengah a thuung.
7 Babilon ta zama ƙoƙon zinariya a hannun Ubangiji, ta sa dukan duniya ta yi maye. Ƙasashe sun sha ruwan inabinta, saboda haka yanzu sun haukace.
BOEIPA kut kah Babylon sui boengloeng loh diklai pum a rhuihmil sak. A misurtui te namtom loh a ok tih namtom khaw yan uh.
8 Farat ɗaya Babilon za tă fāɗi ta farfashe. Ku yi kuka dominta! Ku samo mata magani saboda azabarta; wataƙila za a iya warkar da ita.
Babylon te buengrhuet cungku vetih bawt ni. Anih ham rhung uh lamtah thingpi loh pa uh lah, a nganboh te a hoeih pah khaming.
9 “‘Da mun warkar da Babilon, amma ba za tă warke ba; mu ƙyale ta kowane yă koma garinsu, gama hukuncinta ya kai sammai, ya yi tsawo kamar gizagizai.’
Babylon te n'toi khaw n'toi dae a hoeih moenih. Anih te hnoo uh lamtah hlang loh amah khohmuen la cet uh saeh. A laitloeknah loh vaan duela a pha tih khomong duela a toh.
10 “‘Ubangiji ya baratar da mu; zo mu tafi mu yi shelarsa a Sihiyona mu faɗa abin da Ubangiji Allahnmu ya yi.’
BOEIPA loh kaimih kah duengnah hang khuen te khuen uh sih lamtah kaimih Pathen BOEIPA kah khoboe te Zion ah doek uh sih.
11 “Ku wasa kibiyoyi, ku ɗauko garkuwoyi! Ubangiji ya zuga sarakunan Medes, domin niyyarsa ce yă hallaka Babilon. Ubangiji zai yi ramuwa, zai yi ramuwa saboda haikalinsa.
Thaltang te meet lamtah photling te cung sakuh. BOEIPA loh Madai manghai kah mueihla te a haeng coeng. A thuepnah lamloh BOEIPA kah tawnlohnah neh a bawkim kah tawnlohnah dongah Babylon te phae kuekluek ham om.
12 Ku tā da tuta gāba da katangan Babilon! Ku ƙara matsara, ku kafa masu tsaro, ku shirya kwanto! Ga shi, Ubangiji zai aikata abin da ya faɗa umarninsa a kan mutanen Babilon.
Babylon vongtung te rholik ling thiluh. Thongim te bingbo lamtah rhaltawt hlah uh. Rhongngol te soepsoei uh. Babylon khosa rhoek a voek tih BOEIPA loh a mangtaeng te khaw a saii bal ni.
13 Ke da kike zama kusa da ruwaye da kike kuma wadatar dukiya, ƙarshenki ya zo, lokaci ya yi da za a kau da ke.
A tui aka buem taengah kho aka sa, kho aka sa kah thakvoh he len dae na mueluemnah dong khat te na bawtnah la pawk coeng.
14 Ubangiji Maɗaukaki ya rantse da zatinsa, ya ce Tabbatacce zan cika ka da mutane kamar fāra, za su kuwa yi sowa don nasara a kanka.
Caempuei BOEIPA loh a hinglu neh a toemngam coeng. Hlang te lungang bangla nang kan cung sak kuekluek vetih nang te tamlung neh n'doo uh ni.
15 “Ya halicci ƙasa ta wurin ikonsa; ya kafa duniya ta wurin hikimarsa, ya kuma shimfiɗa sammai ta wurin fahiminsa.
A thadueng lamloh diklai a saii tih a cueihnah loh lunglai a picai. A lungcuei neh vaan a cueh.
16 Sa’ad da ya yi tsawa ruwan da suke sammai sukan yi ruri; yakan sa gizagizai su tashi daga ƙarshen duniya. Yakan tura walƙiya tare da ruwan sama yakan kuma saki iska daga cikin taskokinsa.
Vaan kah tui len khaw ol a paek tih diklai khobawt lamkah khomong a luei sak. Khotlan ham rhaek a saii tih a thakvoh lamloh khohli hang khuen.
17 “Kowane mutum marar azanci ne kuma ba shi da sani; kowane maƙerin zinariya yakan sha kunya daga wurin gumakansa. Siffofinsa na ƙarya ne; babu numfashi a cikinsu.
A mingnah lamloh hlang boeih a dom tih mueithuk aka picai boeih khaw yak. A tuisi hong neh amih khuiah mueihla a om moenih.
18 Su marasa amfani ne, abubuwan ba’a ne kawai; sa’ad da lokacin hukuncinsu ya kai, za su hallaka.
Akaimih kah a honghi neh a hohap bibi te a cawhnah tue ah paltham bitni.
19 Wanda yake na wajen Yaƙub ba kamar waɗannan ba ne, gama shi ne Mahalicci dukan abu, har da kabilar abin gādonsa, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
Jakob kah khoyo tah te bang moenih. A ming khaw caempuei Yahweh tih a cungkuem amah kah rho koca la a hlinsai.
20 “Kai ne kulkin yaƙina, kayan yaƙina, da kai ne na ragargaza ƙasashe, da kai ne na hallaka mulkoki,
Nang tah ka caemboh neh caemtloek tubael ni. Nang te namtom kan daeh nah vetih nang te ram kam phae nah ni.
21 da kai ne na ragargaza doki da mahayi, da kai ne na ragargaza keken yaƙin da matuƙi,
Nang te marhang neh a sokah aka ngol te kan daeh nah vetih nang te leng neh a sokah aka ngol te kan daeh nah ni.
22 da kai ne na ragargaza miji da mata, da kai ne na ragargaza tsoho da saurayi, da kai ne na ragargaza saurayi da budurwa,
Nang te huta tongpa kan daeh nah vetih nang te patong camoe kan daeh nah bal ni. Nang te tongpang, oila kan daeh nah ni.
23 da kai ne na ragargaza makiyayi da garke, da kai ne na ragargaza manoma da dawakan noma, da kai ne na ragargaza masu mulki da shugabanni.
Nang te boiva aka dawn neh a tuping khaw kan daeh nah vetih nang te lopho neh a tarhoi kan daeh nah ni. Nang te rhalboei neh ukkung te kan daeh nah ni.
24 “Zan sāka wa Babilon da dukan mazaunan Babilon a idanunku saboda dukan muguntar da suka aikata a Sihiyona,” in ji Ubangiji.
Zion kah namah mikhmuh ah a boethae cungkuem a saii uh te Babylon taeng neh Khalden khosa boeih taengah ka thuung ni. He tah BOEIPA kah olphong ni.
25 “Ga shi, ina gāba da kai, ya ke dutse mai hallakarwa, wadda ta hallaka duniya duka,” in ji Ubangiji. “Zan miƙa hannuna gāba da ke, zan mirgina ƙasa daga ƙwanƙolin dutse, zan maishe ki ƙonannen dutse.
Kutcaihnah tlang nang taengah ka pai coeng ne. He tah BOEIPA kah olphong ni. Diklai boeih aka phae khaw nang taengla ka kut ka thueng ni. Te vaengah thaelpang lamloh nang kam paluet vetih ungkhang tlang la nang kang khueh ni.
26 Ba za a ɗauki dutsen yin kusurwa daga gare ki ba ko na kafa harsashen gini, gama za ki zama marar amfani har abada,” in ji Ubangiji.
Nang lamkah te bangkil lung neh tungkho lung khaw lo uh mahpawh. BOEIPA kah olphong bangla kumhal due khopong la na om ni.
27 “Ku tā da tuta a ƙasa! Ku busa ƙahoni a cikin ƙasashe! Ku shirya ƙasashe don yaƙi da ita, ku kira waɗannan mulkokin gāba da ita. Ararat, Minni, da Ashkenaz. A naɗa shugaba gāba da ita; ku shirya dawakai kamar fāra.
Diklai ah rholik thoh uh lamtah namtom taengah tuki ueng uh. Namtom taengah ciim uh lamtah a ram soah khaw yaak sakuh. Minni Ararat neh Ashkenaz te rhalboei khueh thil lamtah marhang te lungang hathawp bangla yuel sakuh.
28 Ku shirya ƙasashe don yaƙi da ita, sarakunan Medes, gwamnoninsu da dukan masu shugabancinsu da kowace ƙasar da take ƙarƙashin mulkinsu.
Namtom Madai manghai rhoek neh a rhalboei rhoek, a ukkung boeih neh a khohung khohmuen boeih anih taengah ciim uh laeh.
29 Ƙasa ta girgiza tana makyarkyata saboda nufin Ubangiji na gāba da Babilon ya tabbata, nufinsa na mai da ƙasar Babilon kufai don kada kowa yă zauna a can.
Khosak pawt hil Babylon khohmuen te imsuep la khueh ham Babylon sokah BOEIPA kopoek te a thoh dongah khohmuen hinghuen tih kilkul ni.
30 Sojojin Babilon sun daina yaƙi, suna zaune a cikin kagaransu. Ƙarfinsu ya ƙare, sun zama mata. An sa wa wuraren zamanta wuta, an karya ƙyamaren ƙofofin garinta.
Babylon hlangrhalh loh vathoh ham khaw paa uh tih rhalmahim ah ngol uh. Amih kah thayung thamal te tla coeng tih huta bangla om uh. A tolhmuen a hlup uh tih a thohkalh ngen coeng.
31 Maguji yana biye da maguji a guje, jakada yana biye da jakada, don su faɗa wa sarkin Babilon, cewa an ci birninsa a kowane gefe.
A khopuei a bawt duela a loh pah te Babylon manghai taengah puen ham, aka yong loh aka yong te doe ham neh, aka puen loh aka puen te doe ham yong uh.
32 An ƙwace mashigai aka ƙone fadamu da wuta, sojoji kuma suka giggice.”
Lamkai te a tlaeng uh tih tuibap te hmai neh a hoeh uh. Te dongah caemtloek hlang rhoek khaw let uh.
33 Ni Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila na ce, “’Yar Babilon kamar daɓen masussuka a lokacin da ake sussuka, ba da daɗewa ba lokacin girbe ta zai zo.”
Israel Pathen caempuei BOEIPA loh he ni a. thui. A til tue ah tah Babylon nu te cangtilhmuen bangla om pawn vetih a taengah cangah tue pai pawn ni.
34 “Nebukadnezzar sarkin Babilon ya cinye mu, ya sa muka rikice, ya maishe mu kamar tulun da babu kome a cikinsa. Ya cinye mu kamar yadda dodon ruwa yakan yi ya kuma cika cikinsa da kayan marmarinmu, sa’an nan kuma ya yi amanmu.
Babylon manghai Nebukhanezar loh kaimih n'yoop tih kamah khaw n'yoop coeng, kaimih n'khawkkhek tih kamah n'khawkkhek coeng. Kaimih he am hong la n'khueh tih kamah khaw n'khueh. Tuihnam bangla kaimih he n'dolh tih kai khaw n'dolh. Ka omthennah neh a bungpuei a hah phoeiah tah kaimih te n'hoek tih kai khaw n'hoek.
35 Bari abin da aka yi wa jikinmu yă kasance a bisa Babilon,” in ji mazaunan Sihiyona. “Bari jininmu yă kasance a kan waɗanda suke zama a Babilon,” in ji Urushalima.
Zion khosa rhoek loh, “ka kuthlahnah neh ka pumsa he Babylon soah tla saeh,” ti saeh. Jerusalem loh, “Ka thii Khalden khosa rhoek soah tla saeh,” ti uh saeh.
36 Saboda haka ga abin da Ubangiji ya ce, “Duba, zan tsaya muku, zan ɗaukar muku fansa, zan sa tekunta kafe in kuma sa maɓulɓulanta su ƙafe.
Te dongah BOEIPA loh he ni a. thui. Na tuituknah te kai loh kang rhoe tih nang kah tawnlohnah khaw phu ka loh ni. Te vaengah a tuipuei te ka kak sak vetih a thunsih te ka haang sak ni.
37 Babilon za tă zama tarin juji, wurin zaman diloli, abin ƙyama da abar ba’a, inda ba kowa.
Babylon te pongui kah khuirhung lungkuk la om vetih imsuep neh a thuithetnah la khosa om mahpawh.
38 Mutanenta duk suna ruri kamar zakoki, suna gurnani kamar’ya’yan zaki.
Sathuengca bangla huek kawk uh tih sathueng casen bangla cai uh.
39 Amma sa’ad da aka farkar da su, zan yi musu biki in sa su sha su bugu, domin yi sowa da dariya, sa’an nan su shiga barcin da ba za su farka ba,” in ji Ubangiji.
A bae vaengah a buhkoknah ka khueh pah saeh lamtah amih ka rhuihmil sak eh. Te daengah ni sundaep uh vetih aka ip loh kumhal due a ih vaengah a haenghang uh pawt eh. He tah BOEIPA kah olphong ni.
40 “Zan sauko da su kamar tumaki zuwa mayanka, kamar raguna da bunsurai.
Amih te tuca bangla ngawn ham tutal neh kikong bangla ka suntlak sak ni.
41 “Yadda za a ci Sheshak, taƙamar duniya duka za tă daina! Babilon za tă zama abar ƙyama a cikin al’ummai!
Balae tih Sheshak te a loh veith diklai pum kah koehnah te a loh eh? Balae tih Babylon he namtom taengah imsuep la a om eh?
42 Teku zai malalo a kan Babilon, raƙumansa masu hauka za su rufe ta.
Babylon soah tuitunli loh a khuk tih a tuiphu tuilipo loh a et.
43 Garuruwanta sun zama abin kufai, za tă zama hamada inda ba ruwa, ƙasar da ba mazauna, ba kuma mutumin da zai ratsa ta cikinta.
A khopuei te rhamrhae khohmuen neh khohmuen kolken kah imsuep la poeh. A khuihah hlang boeih khosa pawt tih hlang capa tah te longah ah pongpa pawh.
44 Zan hukunta Bel a Babilon, in sa ya yi aman abin da ya haɗiye. Ƙasashe ba za su ƙara bumbuntowa wurinsa ba. Katangan Babilon kuwa za tă rushe!
Babylon kah Bel te ka cawh coeng tih a dolhhnap te a ka lamloh ka yawt pah. Te dongah namtom khaw a taengah hlampan voel pawt tih Babylon vongtung khaw cungku van.
45 “Ku fito daga cikinta, jama’ata! Ku tsere da ranku! Ku tsere daga zafin fushin Ubangiji.
Ka pilnam te a khui lamloh coe laeh saeh lamtah hlang loh a hinglu te BOEIPA kah thintoek thinsa lamloh loeih sak laeh.
46 Kada zuciyarku tă yi suwu ko ku ji tsoro sa’ad da aka ji labarin a ƙasar, labari guda a wannan shekara, wani kuma a ta biye, labarin hargitsi a ƙasar mai mulki ya tasar wa mai mulki.
Nangmih thinko te phoena vetih khohmuen kah olthang na yaak vaengah na rhih uh ve. Kum khat dongkah olthang phoeiah kum khat dongah olthang he ha pawk. Diklai ah kuthlahnah he aka taemrhai loh aka taemrhai taengah a khueh.
47 Gama kwanaki tabbatacce suna zuwa, sa’ad da zan hukunta gumakan Babilon, zan kunyatar da dukan ƙasar kuma matattunta duk za su kwanta a cikinta.
Te dongah khohnin ha pawk coeng he. Babylon mueidaep te ka cawh coeng dongah a khohmuen boeih yak pawn ni. A rhok boeih te a khui ah yalh ni.
48 Sa’an nan sama da ƙasa da dukan abin da yake cikinsu, za su yi sowa ta murna a kan Babilon, gama daga arewa masu hallakarwa su auko mata,” in ji Ubangiji.
Te vaengah vaan neh diklai loh Babylon a tamhoe thil vetih anih aka rhoelrhak te tlangpuei lamloh amih taengah boeih ha pawk ni. He tah BOEIPA kah olphong ni.
49 “Babilon za tă fāɗi saboda kisassun mutanen Isra’ila, kamar dai yadda kisassu dukan duniya suka fāɗi saboda Babilon.
Israel rhok aka yalh sak khaw Babylon tangkhuet, diklai pum rhok la aka yalh sak khaw Babylon tangkhuet ni.
50 Ku waɗanda kuka tsere wa takobi, ku gudu kada ku tsaya! Ku tuna da Ubangiji a ƙasa mai nesa, ku kuma yi ta tunani a kan Urushalima.”
cunghang lamkah hlangyong rhoek loh pai kolla cet uh. Khohla lamloh BOEIPA te poek uh lamtah Jerusalem te na thinko ah dueh.
51 “Mun sha kunya saboda zargin da ake yi mana kunya ta rufe mu, domin baƙi sun shiga tsarkakan wurare na gidan Ubangiji.”
BOEIPA im kah rhokso ah kholong rhoek kun uh tih kaimih maelhmai mingthae han hluk te kokhahnah la n'yaak uh dongah n'yak uh.
52 “Amma kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan hukunta gumakanta, da kuma a dukan ƙasarta waɗanda aka yi wa rauni, za su yi nishi.
Te dongah BOEIPA kah olphong khohnin ha pawk coeng he. A mueidaep te ka cawh thil vetih a khohmuen pum ah a rhok neh kii ni.
53 Ko da Babilon za tă kai sararin sama ne, ta gina kagaranta mai ƙarfi, duk da haka zan aiki masu hallakarwa a kanta,” in ji Ubangiji.
Babylon te vaan la luei mai tih a sarhi hmuensang te bit cakhaw anih aka rhoelrhak te kamah taeng lamloh thoeng uh ni. He tah BOEIPA kah olphong ni.
54 “Ku ji muryar kuka daga Babilon, Da hargowar babbar hallakarwa daga ƙasar Babiloniyawa!
Babylon lamkah a pang ol neh Khalden khohmuen lamkah pocinah tanglue aih te.
55 Gama Ubangiji zai rushe Babilon, zai sa ta ƙame bakinta na alfarma. Sojoji za su yi ta kutsawa kamar raƙuman ruwa; suna tā da muryoyinsu.
BOEIPA loh Babylon te a rhoelrhak coeng tih, anih lamkah ol tanglue khaw a paltham sak. Tui len bangla a tuiphu loh kawk tih, a ol te longlonah la a huel.
56 Gama mai hallakarwa ya auka wa Babilon, a kama sojojinta, a kuma kakkarya bakkunansu. Gama Ubangiji shi Allah ne mai sakayya; zai yi sakayya sosai.
Babylon aka rhoelrhak te anih taengla pawk ni. Te vaengah a hlangrhalh rhoek a tuuk vetih, a lii khaw yawk ni. BOEIPA Pathen loh a khoboe te a thuung rhoe a thuung ni.
57 Zan sa mahukuntanta da masu hikimarta, gwamnoninta, shugabanninta da sojojinta su sha su bugu; za su dinga yin barcin da ba za su farka ba,” in ji Sarkin, mai suna Ubangiji Maɗaukaki.
A mangpa rhoek neh a hlangcueih, a rhalboei neh anih kah ukkung rhoek khaw, a hlangrhalh khaw ka rhuihmil sak ni. Te vaengah kumhal due ip rhoe ip vetih haenghang uh mahpawh. A ming ah caempuei manghai, Yahweh kah olphong ni.
58 Ni Ubangiji Maɗaukaki, na ce, “Za a baje katangan nan na Babilon mai kauri za a kuma ƙone dogayen ƙyamarenta da wuta; mutane sun wahalar da kansu a banza, al’umma sun yi wahala kawai domin wutar lalata.”
Caempuei BOEIPA loh he ni a. thui. Babylon vongtung a thah te a phae rhoe a phae ni. A vongka a sang te hmai dongah a hlup uh ni. Pilnam kah a kohnue carhil khaw a poeyoek la om tih namtu khaw hmai carhil dongah tawnba uh bal.
59 Jawabin da annabi Irmiya ya ba Serahiya, ɗan Neriya, wato, jikan Ma’asehiya, lokacin da ya tafi tare da Zedekiya, Sarkin Yahuda, zuwa Babilon a shekara ta huɗu ta mulkinsa. Serahiya shi ne shugaba mai lura da gidajen saukar baƙi.
Judah manghai Zedekiah a manghai kah a kum li dongah amah neh Babylon la a caeh vaengah tonghma Jeremiah loh Maaseiah koca Neriah capa Seraiah te ol a uen. Te vaengah Seraiah kah a mangpa tah duemnah la om.
60 Irmiya ya rubuta a littafi dukan masifun da za su auko wa Babilon, wato, dukan wannan magana da aka rubuta a kan Babilon.
Te dongah Babylon ah aka pawk ham boethae cungkuem neh Babylon ham a daek ol cungkuem te khaw cabu pakhat dongah Jeremiah loh a daek.
61 Irmiya kuwa ya ce wa Serahiya, “Lokacin da ka kai Babilon, sai ka karanta dukan maganan nan.
Te vaengah Jeremiah loh Seraiah taengah, “Babylon na pha neh na hmuh taengah he ol cungkuem he doek pah.
62 Ka kuma ce, ‘Ya Ubangiji, kai ne ka yi magana a kan wannan wuri, cewa za ka lalatar da shi, har ba abin da zai zauna a ciki, mutum ko dabba. Wurin zai zama kufai har abada.’
Te vaengah, 'BOEIPA loh he hmuen he a saii vetih a khuiah hlang neh rhamsa khaw khosa om pawt vetih kumhal ah khopong la om ni, 'ti nah lamtah namah loh thui pah.
63 Sa’ad da ka gama karanta wannan littafi, sai ka ɗaura wa littafin dutse, sa’an nan ka jefar da shi tsakiyar Kogin Yuferites.
Cabu na tae te na khah vaengah lungto te khit thil lamtah Perath laklung la voei ne.
64 Sa’an nan ka ce, ‘Haka Babilon za tă nutse, ba za tă ƙara tashi ba saboda masifar da zan kawo mata. Mutanenta kuwa za su fāɗi.’” Wannan shi ne ƙarshen kalmomin Irmiya.
Te vaengah, 'Babylon khaw buek van vetih yoethae hmai lamloh thoo thai mahpawh. Te tah kai loh anih soah ka thoeng sak dongah tawnba uh ni,’ ti nah,” a ti nah. He hil he Jeremiah kah ol ni.

< Irmiya 51 >