< Irmiya 50 >

1 Ga maganar Ubangiji da ya yi ta wurin Irmiya annabi game da Babilon da kuma ƙasar Babiloniyawa.
کلامی که خداوند درباره بابل و زمین کلدانیان به واسطه ارمیا نبی گفت:۱
2 “Ka yi shela ka kuma furta a cikin al’ummai, ka tā da tuta ka kuma furta; kada ku ɓoye kome, amma ku ce, ‘Za a ci Babilon da yaƙi; za a kunyata Bel, Marduk ya cika da tsoro. Siffofinta za su sha kunya gumakanta za su cika da tsoro.’
«درمیان امت‌ها اخبار و اعلام نمایید، علمی برافراشته، اعلام نمایید و مخفی مدارید. بگوییدکه بابل گرفتار شده، و بیل خجل گردیده است. مرودک خرد شده و اصنام او رسوا و بتهایش شکسته گردیده است۲
3 Al’umma daga arewa za tă fāɗa mata su mai da ƙasar kango. Ba wanda zai zauna a cikinta; mutane da dabbobi za su gudu.
زیرا که امتی از طرف شمال بر او می‌آید و زمینش را ویران خواهدساخت به حدی که کسی در آن ساکن نخواهد شدو هم انسان و هم بهایم فرار کرده، خواهند رفت.۳
4 “A kwanakin nan, a wannan lokaci,” in ji Ubangiji, “mutanen Isra’ila da mutanen Yahuda gaba ɗaya za su tafi cikin hawaye su nemi Ubangiji Allahnsu.
خداوند می‌گوید که در آن ایام و در آن زمان بنی‌اسرائیل و بنی یهودا با هم خواهند آمد. ایشان گریه‌کنان خواهند آمد و یهوه خدای خود راخواهند طلبید.۴
5 Za su tambayi hanyar zuwa Sihiyona su kuma juya fuskokinsu wajenta. Za su zo su haɗa kansu ga Ubangiji a madawwamin alkawari da ba za a manta da shi ba.
و رویهای خود را بسوی صهیون نهاده، راه آن را خواهند پرسید و خواهندگفت بیایید و به عهد ابدی که فراموش نشود به خداوند ملصق شویم.۵
6 “Mutanena sun zama ɓatattun tumaki; makiyayansu sun bauɗar da su suka sa suna ta yawo a cikin duwatsu. Sun yi ta yawo a bisa dutse da tudu suka manta wurin hutunsu.
«قوم من گوسفندان گم شده بودند و شبانان ایشان ایشان را گمراه کرده، بر کوهها آواره ساختند. از کوه به تل رفته، آرامگاه خود رافراموش کردند.۶
7 Duk wanda ya same su ya cinye su; abokan gābansu suka ce, ‘Ba mu da laifi, gama sun yi zunubi wa Ubangiji, wurin kiwonsu na gaske, Ubangiji, abin sa zuciyar kakanninsu.’
هر‌که ایشان را می‌یافت ایشان را می‌خورد و دشمنان ایشان می‌گفتند که گناه نداریم زیرا که به یهوه که مسکن عدالت است و به یهوه که امید پدران ایشان بود، گناه ورزیدند.۷
8 “Ku gudu daga Babilon; ku bar ƙasar Babiloniyawa, ku zama kamar awakin da suke bi da garke.
ازمیان بابل فرار کنید و از زمین کلدانیان بیرون آیید. و مانند بزهای نر پیش روی گله راه روید.۸
9 Gama zan kuta in kuma kawo a kan Babilon haɗinkan manyan al’ummai na arewa. Za su ja dāgār gāba da ita, kuma daga arewa za a ci ta da yaƙi. Kibiyoyinsu za su zama kamar na gwanayen jarumawa waɗanda ba sa dawowa hannu wofi.
زیرااینک من جمعیت امت های عظیم را از زمین شمال برمی انگیزانم و ایشان را بر بابل می‌آورم وایشان در برابر آن صف آرایی خواهند نمود و درآنوقت گرفتار خواهد شد. تیرهای ایشان مثل تیرهای جبار هلاک کننده که یکی از آنها خالی برنگردد خواهد بود.۹
10 Saboda haka za a washe Babiloniyawa; dukan waɗanda suka washe ta za su ƙoshi,” in ji Ubangiji.
خداوند می‌گوید که کلدانیان تاراج خواهند شد و هر‌که ایشان را غارت نماید سیر خواهد گشت.۱۰
11 “Saboda kuna farin ciki kuna kuma murna, ku da kuka washe gādona, domin kuna tsalle kamar karsana mai sussuka hatsi kuna kuma haniniya kamar ingarmu.
زیرا شما‌ای غارت کنندگان میراث من شادی و وجد کردید ومانند گوساله‌ای که خرمن را پایمال کند، جست وخیز نمودید و مانند اسبان زورآور شیهه زدید.۱۱
12 Mahaifiyarku za tă sha babbar kunya; ita da ta haife ku za tă sha kunya. Za tă zama mafi ƙanƙanta na al’ummai, jeji, busasshiyar ƙasa, hamada.
مادر شما بسیار خجل خواهد شد و والده شمارسوا خواهد گردید. هان او موخر امت‌ها و بیابان و زمین خشک و عربه خواهد شد.۱۲
13 Saboda fushin Ubangiji ba za tă zauna a cikinta ba amma za tă zama kufai gaba ɗaya. Duk waɗanda suka wuce Babilon za su ji tsoro su kuma yi tsaki saboda dukan mikinta.
به‌سبب خشم خداوند مسکون نخواهد شد بلکه بالکل ویران خواهد گشت. و هر‌که از بابل عبور نمایدمتحیر شده، به جهت تمام بلایایش صفیر خواهدزد.۱۳
14 “Ku ja dāgā kewaye da Babilon, dukanku waɗanda kuke jan baka. Ku harbe ta! Kada ku rage kibiyoyi, gama ta yi zunubi ga Ubangiji.
‌ای جمیع کمان داران در برابر بابل از هرطرف صف آرایی نمایید. تیرها بر او بیندازید ودریغ منمایید زیرا به خداوند گناه ورزیده است.۱۴
15 Ku yi kuwwa a kanta a kowane gefe! Ta miƙa wuya, hasumiyarta ta fāɗi, katangarta sun rushe. Da yake wannan sakayya ce ta Ubangiji, ku ɗauki fansa a kanta; yi mata yadda ta yi wa waɗansu.
از هر طرف بر او نعره زنید چونکه خویشتن راتسلیم نموده است. حصارهایش افتاده ودیوارهایش منهدم شده است زیرا که این انتقام خداوند است. پس از او انتقام بگیرید و بطوری که او عمل نموده است همچنان با او عمل نمایید.۱۵
16 Ku datse wa Babilon mai shuka, da mai girbi lauje a lokacin girbi. Saboda takobin mai zalunci bari kowa ya koma ga mutanensa, bari kowa ya gudu zuwa ga ƙasarsa.
و از بابل، برزگران و آنانی را که داس را در زمان درو بکار می‌برند منقطع سازید. و از ترس شمشیر برنده هرکس بسوی قوم خود توجه نماید و هر کس به زمین خویش بگریزد.۱۶
17 “Isra’ila garke ne da ya watse da zakoki suka kora. Na farkon da ya cinye shi sarkin Assuriya ne; na ƙarshen da ya ragargaza ƙasusuwansa Nebukadnezzar sarkin Babilon ne.”
«اسرائیل مثل گوسفند، پراکنده گردید. شیران او را تعاقب کردند. اول پادشاه آشور او راخورد و آخر این نبوکدرصر پادشاه بابل استخوانهای او را خرد کرد.»۱۷
18 Saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Zan hukunta sarkin Babilon da ƙasarsa yadda na hukunta sarkin Assuriya.
بنابراین یهوه صبایوت خدای اسرائیل چنین می‌گوید: «اینک من بر پادشاه بابل و بر زمین او عقوبت خواهم رسانید چنانکه بر پادشاه آشور عقوبت رسانیدم.۱۸
19 Amma zan komo da Isra’ila zuwa wurin kiwonsa zai kuwa yi kiwo a Karmel da Bashan; zai ƙosar da marmarinsa a tuddan Efraim da Gileyad.
و اسرائیل را به مرتع خودش باز خواهم آورد و در کرمل و باشان خواهد چرید و بر کوهستان افرایم و جلعاد جان او سیر خواهد شد.۱۹
20 A kwanakin nan, da kuma a lokacin nan,” in ji Ubangiji, “za a yi bincike don laifin Isra’ila, amma ba za a samu ba, kuma don zunubin Yahuda, amma ba za a sami wani abu ba, gama zan gafarta wa raguwar da na rage.
خداوند می‌گوید که در آن ایام و در آن زمان عصیان اسرائیل را خواهند جست و نخواهد بودو گناه یهودا را اما پیدا نخواهد شد، زیرا آنانی راکه باقی می‌گذارم خواهم آمرزید.۲۰
21 “Ku fāɗa wa ƙasar Meratayim da waɗanda suke zama a Fekod. Ku fafara, ku kashe kuma hallaka su sarai,” in ji Ubangiji. “Ku aikata dukan abin da na umarce ku.
«بر زمین مراتایم برآی یعنی بر آن و برساکنان فقود. خداوند می‌گوید: بکش و ایشان راتعاقب نموده، بالکل هلاک کن و موافق هر‌آنچه من تو را امر فرمایم عمل نما.۲۱
22 Hargowar yaƙi tana a ƙasar, hargowar babbar hallaka!
آواز جنگ وشکست عظیم در زمین است.۲۲
23 Dubi yadda aka karya aka kuma ragargaza gudumar dukan duniya! Dubi yadda Babilon ta zama kufai a cikin al’ummai!
کوپال تمام جهان چگونه بریده و شکسته شده و بابل در میان امت‌ها چگونه ویران گردیده است.۲۳
24 Na sa miki tarko, Babilon, kika kuwa kamu kafin ki sani; aka same ki aka kuma kama ki domin kin tayar wa Ubangiji.
‌ای بابل ازبرای تو دام گستردم و تو نیز گرفتار شده، اطلاع نداری. یافت شده، تسخیر گشته‌ای چونکه باخداوند مخاصمه نمودی.۲۴
25 Ubangiji ya buɗe taskar makamansa ya fitar da makaman fushinsa, gama Maɗaukaki Ubangiji Mai Iko Duka yana da aikin da zai yi a ƙasar Babiloniyawa.
خداونداسلحه خانه خود را گشوده، اسلحه خشم خویش را بیرون آورده است. زیرا خداوند یهوه صبایوت با زمین کلدانیان کاری دارد.۲۵
26 Ku zo ku yi gāba da ita daga nesa. Ku buɗe rumbunanta; ku jibga ta kamar tsibin hatsi. Ku hallaka ta sarai kada ku bar mata raguwa.
بر او از همه اطراف بیایید و انبارهای او را بگشایید، او را مثل توده های انباشته بالکل هلاک سازید و چیزی ازاو باقی نماند.۲۶
27 Ku kashe dukan’yan bijimanta bari su gangara zuwa mayanka! Kaitonsu! Gama ranansu ta zo, lokaci ya yi da za a hukunta su.
همه گاوانش را به سلاخ خانه فرود آورده، بکشید. وای بر ایشان! زیرا که یوم ایشان و زمان عقوبت ایشان رسیده است.۲۷
28 Ku saurari masu gudun hijira da masu neman mafaka daga Babilon suna furtawa a Sihiyona yadda Ubangiji Allahnmu ya ɗauki fansa, fansa domin haikalinsa.
آوازفراریان و نجات‌یافتگان از زمین بابل مسموع می‌شود که از انتقام یهوه خدای ما و انتقام هیکل او در صهیون اخبار می‌نمایند.۲۸
29 “Ku kira’yan baka a kan Babilon, dukan waɗanda suke jan baka. Ku yi sansani kewaye da ita duka; kada ku bar wani ya tsira. Ku sāka mata don ayyukanta; ku yi mata yadda ta yi. Gama ta tayar wa Ubangiji, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
تیراندازان را به ضد بابل جمع کنید. ای همگانی که کمان را زه می‌کنید، در برابر او از هر طرف اردو زنید تااحدی رهایی نیابد و بر وفق اعمالش او را جزا دهید و مطابق هر‌آنچه کرده است به او عمل نمایید. زیرا که به ضد خداوند و به ضد قدوس اسرائیل تکبر نموده است.۲۹
30 Saboda haka, samarinta za su fāɗi a tituna; za a kawar da dukan sojojinta a wannan rana,” in ji Ubangiji.
لهذا خداوندمی گوید که جوانانش در کوچه هایش خواهندافتاد و جمیع مردان جنگیش در آن روز هلاک خواهند شد.۳۰
31 “Ga shi, ina gāba da ke, ya ke mai girman kai,” in ji Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, “gama ranarki ta zo, lokacin da za a hukunta ki.
«اینک خداوند یهوه صبایوت می‌گوید: ای متکبر من بر‌ضد تو هستم. زیرا که یوم تو و زمانی که به تو عقوبت برسانم رسیده است.۳۱
32 Mai ɗaga kai za tă yi tuntuɓe ta kuma fāɗi kuma ba wanda zai taimake ta tă tashi; zan hura wuta a garuruwanta da za tă cinye duk waɗanda suke kewaye da ita.”
و آن متکبر لغزش خورده، خواهد افتاد و کسی او رانخواهد برخیزانید و آتش در شهرهایش خواهم افروخت که تمامی حوالی آنها را خواهدسوزانید.۳۲
33 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “An danne mutanen Isra’ila, haka ma mutanen Yahuda. Dukan waɗanda suka kama su suna riƙe su kankan, suna kin barinsu su tafi.
یهوه صبایوت چنین می‌گوید: بنی‌اسرائیل و بنی یهودا با هم مظلوم شدند و همه آنانی که ایشان را اسیر کردند ایشان را محکم نگاه می‌دارند و از رها کردن ایشان ابا می‌نمایند.۳۳
34 Duk da haka Mai Fansarsu yana da ƙarfi; Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa. Zai kāre muradunsu gabagadi don yă kawo hutu ga ƙasarsu, amma rashin hutu ga waɗanda suke zaune a Babilon.
اماولی ایشان که اسم او یهوه صبایوت می‌باشدزورآور است و دعوی ایشان را البته انجام خواهدداد و زمین را آرامی خواهد بخشید و ساکنان بابل را بی‌آرام خواهد ساخت.۳۴
35 “Akwai takobi a kan Babiloniyawa!” In ji Ubangiji “a kan waɗanda suke zama a Babilon da kuma a kan fadawanta da masu hikimarta!
خداوند می‌گوید: شمشیری بر کلدانیان است و بر ساکنان بابل وسرورانش و حکیمانش.۳۵
36 Akwai takobi a kan annabawan ƙaryanta! Za su zama wawaye. Akwai takobi a kan jarumawanta! Za su cika da tsoro.
شمشیری بر کاذبان است و احمق خواهند گردید. شمشیری برجباران است و مشوش خواهند شد.۳۶
37 Akwai takobi a kan dawakanta da kekunan yaƙinta da kuma dukan baƙin da suke cikin mayaƙanta! Za su zama mata. Akwai takobi a kan dukiyarta! Za a washe su.
شمشیری بر اسبانش و بر ارابه هایش می‌باشدو بر تمامی مخلوق مختلف که در میانش هستند ومثل زنان خواهند شد. شمشیری بر خزانه هایش است و غارت خواهد شد.۳۷
38 Fări a kan ruwanta! Za su bushe ƙaf. Gama ƙasa ce ta gumaka, gumakan da za su haukace da tsoro.
خشکسالی برآبهایش می‌باشد و خشک خواهد شد زیرا که آن زمین بتها است و بر اصنام دیوانه شده‌اند.۳۸
39 “Saboda haka halittun hamada da kuraye za su zauna a can, a can kuma mujiya za tă zauna. Ba za a ƙara zauna ko a yi zama a cikinta ba daga tsara zuwa tsara.
بنابراین وحوش صحرا با گرگان ساکن خواهندشد و شترمرغ در آن سکونت خواهد داشت و بعداز آن تا به ابد مسکون نخواهد شد و نسلا بعدنسل معمور نخواهد گردید.»۳۹
40 Yadda Allah ya tumɓuke Sodom da Gomorra tare da maƙwabtan garuruwansu,” in ji Ubangiji “haka ma ba wanda zai zauna a can; ba wani da zai zauna a cikinta.
خداوندمی گوید: «چنانکه خدا سدوم و عموره وشهرهای مجاور آنها را واژگون ساخت، همچنان کسی آنجا ساکن نخواهد شد و احدی از بنی آدم در آن ماوا نخواهد گزید.۴۰
41 “Duba! Ga sojoji suna zuwa daga arewa; babbar al’umma da sarakuna masu yawa suna tahowa daga iyakokin duniya.
اینک قومی از طرف شمال می‌آیند و امتی عظیم و پادشاهان بسیار ازکرانه های جهان برانگیخته خواهند شد.۴۱
42 Suna riƙe da baka da māshi; mugaye ne marasa tausayi. Amonsu ya yi kamar rurin teku yayinda suke hawan dawakansu; suna zuwa kamar mutane a dāgār yaƙi don su fāɗa miki, ya Diyar Babilon.
ایشان کمان و نیزه خواهند گرفت. ایشان ستم پیشه هستند و ترحم نخواهند نمود. آواز ایشان مثل شورش دریا است و بر اسبان سوار شده، در برابرتو‌ای دختر بابل مثل مردان جنگی صف آرایی خواهند نمود.۴۲
43 Sarkin Babilon ya ji rahotanni game da su, hannunsa kuma ya yi laƙwas. Wahala ta kama shi, zafi kamar na mace mai naƙuda.
پادشاه بابل آوازه ایشان راشنید و دستهایش سست گردید. و الم و درد او رامثل زنی که می‌زاید در‌گرفته است.۴۳
44 Kamar zaki mai haurawa daga kurmin Urdun zuwa wurin kiwo mai dausayi, zan fafare Babilon daga ƙasan nan da nan. Wane ne zaɓaɓɓen da zan naɗa domin wannan? Wane ne kamar ni da zai kalubalance ni? Kuma wanda makiyayi zai iya tsaya gāba da ni?”
اینک اومثل شیر از طغیان اردن به آن مسکن منیع برخواهد آمد زیرا که من ایشان را در لحظه‌ای ازآنجا خواهم راند. و کیست آن برگزیده‌ای که او رابر آن بگمارم؟ زیرا کیست که مثل من باشد وکیست که مرا به محاکمه بیاورد و کیست آن شبانی که به حضور من تواند ایستاد؟»۴۴
45 Saboda haka, ku ji abin da Ubangiji ya shirya a kan Babilon, abin da ya nufa gāba da ƙasar Babiloniyawa. Za a kwashe ƙananan garkensu a tafi; zai hallaka wurin kiwonsu sarai saboda su.
بنابراین مشورت خداوند را که درباره بابل نموده است وتقدیرهای او را که درباره زمین کلدانیان فرموده است بشنوید. البته ایشان صغیران گله را خواهندربود و هر آینه مسکن ایشان را برای ایشان خراب خواهد ساخت.۴۵
46 Da jin an ci Babilon da yaƙi sai duniya ta girgiza; za a ji kukanta cikin al’ummai.
از صدای تسخیر بابل زمین متزلزل شد و آواز آن در میان امت‌ها مسموع گردید.۴۶

< Irmiya 50 >