< Irmiya 50 >

1 Ga maganar Ubangiji da ya yi ta wurin Irmiya annabi game da Babilon da kuma ƙasar Babiloniyawa.
Dette er det ord Herren talte om Babel, om kaldeernes land, ved profeten Jeremias.
2 “Ka yi shela ka kuma furta a cikin al’ummai, ka tā da tuta ka kuma furta; kada ku ɓoye kome, amma ku ce, ‘Za a ci Babilon da yaƙi; za a kunyata Bel, Marduk ya cika da tsoro. Siffofinta za su sha kunya gumakanta za su cika da tsoro.’
Forkynn det iblandt folkene og kunngjør det og løft op banner, kunngjør det, dølg det ikke, si: Babel er inntatt, Bel er blitt til skamme, Merodak er blitt forferdet, dets gudebilleder er blitt til skamme, dets vederstyggelige avguder er forferdet!
3 Al’umma daga arewa za tă fāɗa mata su mai da ƙasar kango. Ba wanda zai zauna a cikinta; mutane da dabbobi za su gudu.
For et folk drar op imot det fra nord, det gjør dets land til en ørken, og det er ingen som bor i det; både mennesker og dyr er flyktet bort.
4 “A kwanakin nan, a wannan lokaci,” in ji Ubangiji, “mutanen Isra’ila da mutanen Yahuda gaba ɗaya za su tafi cikin hawaye su nemi Ubangiji Allahnsu.
I de dager og på den tid, sier Herren, skal Israels barn komme, de og Judas barn sammen; de skal gå og gråte, og Herren sin Gud skal de søke.
5 Za su tambayi hanyar zuwa Sihiyona su kuma juya fuskokinsu wajenta. Za su zo su haɗa kansu ga Ubangiji a madawwamin alkawari da ba za a manta da shi ba.
Efter Sion skal de spørre, hit er deres åsyn vendt: Kom og gi eder til Herren ved en evig pakt, som ikke glemmes!
6 “Mutanena sun zama ɓatattun tumaki; makiyayansu sun bauɗar da su suka sa suna ta yawo a cikin duwatsu. Sun yi ta yawo a bisa dutse da tudu suka manta wurin hutunsu.
Fortapte får var mitt folk, deres hyrder hadde ført dem vill, til fjellene hadde de drevet dem bort; fra fjell til haug gikk de, de glemte sitt hvilested.
7 Duk wanda ya same su ya cinye su; abokan gābansu suka ce, ‘Ba mu da laifi, gama sun yi zunubi wa Ubangiji, wurin kiwonsu na gaske, Ubangiji, abin sa zuciyar kakanninsu.’
Alle som traff dem, åt dem, og deres fiender sa: Vi skal ikke bøte for det - fordi de hadde syndet mot Herren, rettferdighetens bolig, og mot sine fedres håp, Herren.
8 “Ku gudu daga Babilon; ku bar ƙasar Babiloniyawa, ku zama kamar awakin da suke bi da garke.
Fly ut av Babel og dra bort fra kaldeernes land, og gå som bukker foran hjorden!
9 Gama zan kuta in kuma kawo a kan Babilon haɗinkan manyan al’ummai na arewa. Za su ja dāgār gāba da ita, kuma daga arewa za a ci ta da yaƙi. Kibiyoyinsu za su zama kamar na gwanayen jarumawa waɗanda ba sa dawowa hannu wofi.
For se, jeg vekker og fører op imot Babel en skare av store folkeslag fra landet i nord, og de skal stille sig op imot det; av dem skal det bli inntatt; deres piler er som en prøvet kjempes, ingen vender tilbake med uforrettet sak.
10 Saboda haka za a washe Babiloniyawa; dukan waɗanda suka washe ta za su ƙoshi,” in ji Ubangiji.
Og Kaldea skal bli til rov; alle som røver det, skal mettes, sier Herren.
11 “Saboda kuna farin ciki kuna kuma murna, ku da kuka washe gādona, domin kuna tsalle kamar karsana mai sussuka hatsi kuna kuma haniniya kamar ingarmu.
Ja, gled eder bare, ja, juble bare, I som plyndrer min arv! Ja, hopp bare som en treskende kvige og vrinsk som de sterke hester!
12 Mahaifiyarku za tă sha babbar kunya; ita da ta haife ku za tă sha kunya. Za tă zama mafi ƙanƙanta na al’ummai, jeji, busasshiyar ƙasa, hamada.
Eders mor blir storlig til skamme, hun som fødte eder, blues; se, hun blir det siste blandt folkene, en ørken, et tørt land og en øde mark.
13 Saboda fushin Ubangiji ba za tă zauna a cikinta ba amma za tă zama kufai gaba ɗaya. Duk waɗanda suka wuce Babilon za su ji tsoro su kuma yi tsaki saboda dukan mikinta.
For Herrens vredes skyld skal det aldri bo folk der igjen, det hele skal bli til en ørken; hver den som går forbi Babel, skal forferdes og spotte over alle dets plager.
14 “Ku ja dāgā kewaye da Babilon, dukanku waɗanda kuke jan baka. Ku harbe ta! Kada ku rage kibiyoyi, gama ta yi zunubi ga Ubangiji.
Still eder op mot Babel rundt omkring, alle I som spenner bue! Skyt på det, spar ikke på pilene! For mot Herren har det syndet.
15 Ku yi kuwwa a kanta a kowane gefe! Ta miƙa wuya, hasumiyarta ta fāɗi, katangarta sun rushe. Da yake wannan sakayya ce ta Ubangiji, ku ɗauki fansa a kanta; yi mata yadda ta yi wa waɗansu.
Opløft hærskrik mot det rundt omkring! Det har overgitt sig, dets grunnvoller er falt, dets murer er brutt ned; for det er Herrens hevn. Hevn eder på det! Gjør mot det således som det har gjort!
16 Ku datse wa Babilon mai shuka, da mai girbi lauje a lokacin girbi. Saboda takobin mai zalunci bari kowa ya koma ga mutanensa, bari kowa ya gudu zuwa ga ƙasarsa.
Utrydd av Babel både såmann og den som fører sigden i høstens tid! For det herjende sverd skal de vende sig hver til sitt folk og fly hver til sitt land.
17 “Isra’ila garke ne da ya watse da zakoki suka kora. Na farkon da ya cinye shi sarkin Assuriya ne; na ƙarshen da ya ragargaza ƙasusuwansa Nebukadnezzar sarkin Babilon ne.”
Et bortdrevet lam er Israel, løver har jaget det bort; først åt Assurs konge det, og nu sist har Babels konge Nebukadnesar knust dets ben.
18 Saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Zan hukunta sarkin Babilon da ƙasarsa yadda na hukunta sarkin Assuriya.
Derfor sier Herren, hærskarenes Gud, Israels Gud, så: Se, jeg hjemsøker Babels konge og hans land, likesom jeg har hjemsøkt Assurs konge.
19 Amma zan komo da Isra’ila zuwa wurin kiwonsa zai kuwa yi kiwo a Karmel da Bashan; zai ƙosar da marmarinsa a tuddan Efraim da Gileyad.
Og jeg vil føre Israel tilbake til dets beitemarker, og det skal beite på Karmel og i Basan, og på Efra'ims fjell og i Gilead skal det ete sig mett.
20 A kwanakin nan, da kuma a lokacin nan,” in ji Ubangiji, “za a yi bincike don laifin Isra’ila, amma ba za a samu ba, kuma don zunubin Yahuda, amma ba za a sami wani abu ba, gama zan gafarta wa raguwar da na rage.
I de dager og på den tid, sier Herren, skal de søke efter Israels misgjerning, men den skal ikke være til, og efter Judas synder, men de skal ikke finnes; for jeg vil tilgi dem som jeg lar bli igjen.
21 “Ku fāɗa wa ƙasar Meratayim da waɗanda suke zama a Fekod. Ku fafara, ku kashe kuma hallaka su sarai,” in ji Ubangiji. “Ku aikata dukan abin da na umarce ku.
Dra op mot Merata'ims land og mot Pekods innbyggere! Forfølg dem, ødelegg dem og slå dem med bann, sier Herren, og gjør i alle deler som jeg har befalt dig!
22 Hargowar yaƙi tana a ƙasar, hargowar babbar hallaka!
Det er larm av krig i landet og stor ødeleggelse.
23 Dubi yadda aka karya aka kuma ragargaza gudumar dukan duniya! Dubi yadda Babilon ta zama kufai a cikin al’ummai!
Hvor den er blitt knekket og knust den hammer som slo hele jorden! Hvor Babel er blitt til en forferdelse blandt folkene!
24 Na sa miki tarko, Babilon, kika kuwa kamu kafin ki sani; aka same ki aka kuma kama ki domin kin tayar wa Ubangiji.
Jeg stilte snare for dig, og du blev fanget, Babel, uten at du visste av det; du blev funnet og grepet; for mot Herren hadde du gitt dig i strid.
25 Ubangiji ya buɗe taskar makamansa ya fitar da makaman fushinsa, gama Maɗaukaki Ubangiji Mai Iko Duka yana da aikin da zai yi a ƙasar Babiloniyawa.
Herren har åpnet sitt rustkammer og tatt frem sin vredes våben; for Herren, Israels Gud, hærskarenes Gud, har et arbeid fore i kaldeernes land.
26 Ku zo ku yi gāba da ita daga nesa. Ku buɗe rumbunanta; ku jibga ta kamar tsibin hatsi. Ku hallaka ta sarai kada ku bar mata raguwa.
Kom imot det fra alle kanter! Åpne dets forrådshus, dyng op som korndynger det som finnes der, og slå det med bann! La det ikke ha noget igjen!
27 Ku kashe dukan’yan bijimanta bari su gangara zuwa mayanka! Kaitonsu! Gama ranansu ta zo, lokaci ya yi da za a hukunta su.
Drep alle dets okser, la dem stige ned for å slaktes! Ve over dem! For deres dag er kommet, deres hjemsøkelses tid.
28 Ku saurari masu gudun hijira da masu neman mafaka daga Babilon suna furtawa a Sihiyona yadda Ubangiji Allahnmu ya ɗauki fansa, fansa domin haikalinsa.
Hør! De er flyktet og undkommet fra Babels land for å kunngjøre i Sion Herrens, vår Guds hevn, hevnen for hans tempel!
29 “Ku kira’yan baka a kan Babilon, dukan waɗanda suke jan baka. Ku yi sansani kewaye da ita duka; kada ku bar wani ya tsira. Ku sāka mata don ayyukanta; ku yi mata yadda ta yi. Gama ta tayar wa Ubangiji, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Kall skytterne sammen mot Babel, alle dem som spenner bue! Slå leir mot det rundt omkring, la ingen slippe unda! Betal det efter dets gjerninger, gjør mot det i alle deler som det har gjort! For mot Herren har det ophøiet sig, mot Israels Hellige.
30 Saboda haka, samarinta za su fāɗi a tituna; za a kawar da dukan sojojinta a wannan rana,” in ji Ubangiji.
Derfor skal dets unge menn falle på dets gater, og alle dets krigsmenn skal tilintetgjøres på den dag, sier Herren.
31 “Ga shi, ina gāba da ke, ya ke mai girman kai,” in ji Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, “gama ranarki ta zo, lokacin da za a hukunta ki.
Se, jeg kommer over dig, Sadon, sier Herren, Israels Gud, hærskarenes Gud; for din dag er kommet, den tid da jeg hjemsøker dig.
32 Mai ɗaga kai za tă yi tuntuɓe ta kuma fāɗi kuma ba wanda zai taimake ta tă tashi; zan hura wuta a garuruwanta da za tă cinye duk waɗanda suke kewaye da ita.”
Og Sadon skal snuble og falle uten å ha nogen som reiser det op, og jeg vil sette ild på dets byer, og den skal fortære alt rundt omkring det.
33 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “An danne mutanen Isra’ila, haka ma mutanen Yahuda. Dukan waɗanda suka kama su suna riƙe su kankan, suna kin barinsu su tafi.
Så sier Herren, hærskarenes Gud: Undertrykt er både Israels barn og Judas barn, og alle de som har ført dem i fangenskap, holder dem fast; de nekter å la dem fare.
34 Duk da haka Mai Fansarsu yana da ƙarfi; Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa. Zai kāre muradunsu gabagadi don yă kawo hutu ga ƙasarsu, amma rashin hutu ga waɗanda suke zaune a Babilon.
Deres gjenløser er sterk, Herren, hærskarenes Gud, er hans navn; han skal visselig føre deres sak og la jorden få ro, men volde Babels innbyggere uro.
35 “Akwai takobi a kan Babiloniyawa!” In ji Ubangiji “a kan waɗanda suke zama a Babilon da kuma a kan fadawanta da masu hikimarta!
Sverd over kaldeerne, sier Herren, over Babels innbyggere, over dets høvdinger og over dets vismenn!
36 Akwai takobi a kan annabawan ƙaryanta! Za su zama wawaye. Akwai takobi a kan jarumawanta! Za su cika da tsoro.
Sverd over snakkerne! De skal stå der som dårer. Sverd over dets kjemper! De skal bli forferdet.
37 Akwai takobi a kan dawakanta da kekunan yaƙinta da kuma dukan baƙin da suke cikin mayaƙanta! Za su zama mata. Akwai takobi a kan dukiyarta! Za a washe su.
Sverd over dets hester og over dets vogner og over alle de fremmede krigsfolk blandt dem! De skal bli til kvinner. Sverd over dets skatter! De skal bli røvet.
38 Fări a kan ruwanta! Za su bushe ƙaf. Gama ƙasa ce ta gumaka, gumakan da za su haukace da tsoro.
Tørke over dets vann! De skal tørkes ut. For det er et land med avgudsbilleder, og med sine gruelige avguder ter de sig som rasende.
39 “Saboda haka halittun hamada da kuraye za su zauna a can, a can kuma mujiya za tă zauna. Ba za a ƙara zauna ko a yi zama a cikinta ba daga tsara zuwa tsara.
Derfor skal ørkenens dyr bo der sammen med ville hunder, og strutser skal bo i det; og det skal aldri mere reise sig igjen, og slekt efter slekt skal ingen bo der.
40 Yadda Allah ya tumɓuke Sodom da Gomorra tare da maƙwabtan garuruwansu,” in ji Ubangiji “haka ma ba wanda zai zauna a can; ba wani da zai zauna a cikinta.
Som da Gud la Sodoma og Gomorra og dets nabobyer i grus, sier Herren, skal ingen mann bo der, og intet menneskebarn opholde sig der.
41 “Duba! Ga sojoji suna zuwa daga arewa; babbar al’umma da sarakuna masu yawa suna tahowa daga iyakokin duniya.
Se, et folk kommer fra nord, et stort folk, og mange konger skal stå frem fra jordens ytterste ende.
42 Suna riƙe da baka da māshi; mugaye ne marasa tausayi. Amonsu ya yi kamar rurin teku yayinda suke hawan dawakansu; suna zuwa kamar mutane a dāgār yaƙi don su fāɗa miki, ya Diyar Babilon.
Bue og spyd holder de i hånden, de er grusomme og skåner ingen; deres røst bruser som havet, og på hester kommer de ridende, rustet som en krigsmann, mot dig, Babels datter!
43 Sarkin Babilon ya ji rahotanni game da su, hannunsa kuma ya yi laƙwas. Wahala ta kama shi, zafi kamar na mace mai naƙuda.
Babels konge har hørt ryktet om dem, og hans hender er blitt kraftløse; angst har grepet ham, smerter som den fødende kvinnes.
44 Kamar zaki mai haurawa daga kurmin Urdun zuwa wurin kiwo mai dausayi, zan fafare Babilon daga ƙasan nan da nan. Wane ne zaɓaɓɓen da zan naɗa domin wannan? Wane ne kamar ni da zai kalubalance ni? Kuma wanda makiyayi zai iya tsaya gāba da ni?”
Se, han stiger op som en løve fra Jordans prakt til de alltid grønne enger; for i et øieblikk vil jeg jage dem bort derfra, og den som er utvalgt, ham vil jeg sette over det; for hvem er som jeg, og hvem vil stevne mig, og hvem er den hyrde som kan bli stående for mitt åsyn?
45 Saboda haka, ku ji abin da Ubangiji ya shirya a kan Babilon, abin da ya nufa gāba da ƙasar Babiloniyawa. Za a kwashe ƙananan garkensu a tafi; zai hallaka wurin kiwonsu sarai saboda su.
Hør derfor det råd som Herren har lagt mot Babel, og de tanker som han har tenkt mot kaldeernes land: Visselig, de skal bli slept bort de små lam; visselig, deres beitemark skal forferdes over dem.
46 Da jin an ci Babilon da yaƙi sai duniya ta girgiza; za a ji kukanta cikin al’ummai.
Ved det rop: Babel er inntatt, bever jorden, og det høres skrik blandt folkene.

< Irmiya 50 >