< Irmiya 50 >

1 Ga maganar Ubangiji da ya yi ta wurin Irmiya annabi game da Babilon da kuma ƙasar Babiloniyawa.
Parole que le Seigneur dit sur Babylone et sur les Chaldéens par l’entremise de Jérémie, le prophète.
2 “Ka yi shela ka kuma furta a cikin al’ummai, ka tā da tuta ka kuma furta; kada ku ɓoye kome, amma ku ce, ‘Za a ci Babilon da yaƙi; za a kunyata Bel, Marduk ya cika da tsoro. Siffofinta za su sha kunya gumakanta za su cika da tsoro.’
Annoncez parmi les nations, et faites-le entendre; levez l’étendard, publiez, ne cachez point, dites: Babylone est prise. Bel est couvert de confusion, Mérodach est vaincu; ses images taillées au ciseau sont couvertes de confusion, leurs idoles sont vaincues.
3 Al’umma daga arewa za tă fāɗa mata su mai da ƙasar kango. Ba wanda zai zauna a cikinta; mutane da dabbobi za su gudu.
Parce qu’une nation est montée contre elle venant de l’aquilon, laquelle réduira sa terre en solitude; et il n’y aura personne qui habitera en elle depuis l’homme jusqu’à la bête; et ils ont été troublés, et ils s’en sont allés.
4 “A kwanakin nan, a wannan lokaci,” in ji Ubangiji, “mutanen Isra’ila da mutanen Yahuda gaba ɗaya za su tafi cikin hawaye su nemi Ubangiji Allahnsu.
En ces jours-là, et en ce temps-là, dit le Seigneur, viendront les fils d’Israël et les fils de Juda, et marchant ensemble, et pleurant, ils se hâteront et ils chercheront le Seigneur leur Dieu.
5 Za su tambayi hanyar zuwa Sihiyona su kuma juya fuskokinsu wajenta. Za su zo su haɗa kansu ga Ubangiji a madawwamin alkawari da ba za a manta da shi ba.
Ils demanderont le chemin de Sion; vers elle se tourneront leurs faces. Ils viendront et s’uniront au Seigneur par une alliance éternelle qui ne sera nullement effacée par l’oubli.
6 “Mutanena sun zama ɓatattun tumaki; makiyayansu sun bauɗar da su suka sa suna ta yawo a cikin duwatsu. Sun yi ta yawo a bisa dutse da tudu suka manta wurin hutunsu.
Mon peuple est devenu un troupeau perdu; leurs pasteurs les ont séduits et les ont fait errer dans les montagnes; ils sont passés d’une montagne en une colline; ils ont oublié le lieu de leur repos.
7 Duk wanda ya same su ya cinye su; abokan gābansu suka ce, ‘Ba mu da laifi, gama sun yi zunubi wa Ubangiji, wurin kiwonsu na gaske, Ubangiji, abin sa zuciyar kakanninsu.’
Tous ceux qui les ont trouvés les ont dévorés; et leurs ennemis ont dit: Nous n’avons pas péché; parce qu’ils ont péché contre le Seigneur, la splendeur de la justice, contre le Seigneur, l’attente de leurs pères.
8 “Ku gudu daga Babilon; ku bar ƙasar Babiloniyawa, ku zama kamar awakin da suke bi da garke.
Retirez-vous du milieu de Babylone, et sortez de la terre des Chaldéens; soyez comme des béliers devant un troupeau.
9 Gama zan kuta in kuma kawo a kan Babilon haɗinkan manyan al’ummai na arewa. Za su ja dāgār gāba da ita, kuma daga arewa za a ci ta da yaƙi. Kibiyoyinsu za su zama kamar na gwanayen jarumawa waɗanda ba sa dawowa hannu wofi.
Parce que voilà que moi je suscite et que j’amènerai contre Babylone une assemblée de grandes nations de la terre de l’Aquilon; et elles se prépareront contre elle; et de là elle sera prise; sa flèche, comme celle d’un homme fort qui tue, ne retournera pas vide.
10 Saboda haka za a washe Babiloniyawa; dukan waɗanda suka washe ta za su ƙoshi,” in ji Ubangiji.
Et la Chaldée sera en proie: tous ses dévasteurs seront remplis de dépouilles, dit le Seigneur.
11 “Saboda kuna farin ciki kuna kuma murna, ku da kuka washe gādona, domin kuna tsalle kamar karsana mai sussuka hatsi kuna kuma haniniya kamar ingarmu.
Parce que vous exultez et dites de grandes choses en pillant mon héritage; parce que vous vous êtes répandus comme des veaux sur l’herbe et que vous avez mugi comme des taureaux.
12 Mahaifiyarku za tă sha babbar kunya; ita da ta haife ku za tă sha kunya. Za tă zama mafi ƙanƙanta na al’ummai, jeji, busasshiyar ƙasa, hamada.
Votre mère a été couverte de confusion extrêmement, et elle a été égalée à la poussière, celle qui vous a engendrés; voilà qu’elle sera la dernière parmi les nations, déserte, sans chemin frayé, et aride.
13 Saboda fushin Ubangiji ba za tă zauna a cikinta ba amma za tă zama kufai gaba ɗaya. Duk waɗanda suka wuce Babilon za su ji tsoro su kuma yi tsaki saboda dukan mikinta.
À cause de la colère du Seigneur, elle ne sera pas habitée, mais elle sera tout entière réduite en une solitude; quiconque passera par Babylone, sera frappé de stupeur et sifflera sur toutes ses plaies.
14 “Ku ja dāgā kewaye da Babilon, dukanku waɗanda kuke jan baka. Ku harbe ta! Kada ku rage kibiyoyi, gama ta yi zunubi ga Ubangiji.
Préparez-vous contre Babylone de tous côtes, vous tous qui tendez l’arc; combattez-la, n’épargnez point les flèches, parce que c’est contre le Seigneur qu’elle a péché.
15 Ku yi kuwwa a kanta a kowane gefe! Ta miƙa wuya, hasumiyarta ta fāɗi, katangarta sun rushe. Da yake wannan sakayya ce ta Ubangiji, ku ɗauki fansa a kanta; yi mata yadda ta yi wa waɗansu.
Criez contre elle; partout elle a donné la main; ses fondements sont tombés, ses murs sont détruits, parce que c’est la vengeance du Seigneur, prenez vengeance d’elle; comme elle a fait, faites-lui.
16 Ku datse wa Babilon mai shuka, da mai girbi lauje a lokacin girbi. Saboda takobin mai zalunci bari kowa ya koma ga mutanensa, bari kowa ya gudu zuwa ga ƙasarsa.
Exterminez de Babylone le semeur, et celui qui tient la faucille au temps de la moisson; à la force du glaive de la colombe chacun vers son peuple retournera, et les uns après les autres dans leur terre s’enfuiront.
17 “Isra’ila garke ne da ya watse da zakoki suka kora. Na farkon da ya cinye shi sarkin Assuriya ne; na ƙarshen da ya ragargaza ƙasusuwansa Nebukadnezzar sarkin Babilon ne.”
C’est un troupeau dispersé qu’Israël; des lions l’ont chassé; le premier qui l’a mangé est le roi d’Assur; celui-ci, le dernier, lui a brisé les os, Nabuchodonosor, roi de Babylone.
18 Saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Zan hukunta sarkin Babilon da ƙasarsa yadda na hukunta sarkin Assuriya.
À cause de cela, voici ce que dit le Seigneur des armées, le Dieu d’Israël: Voilà que moi je visiterai le roi de Babylone, et sa terre, comme j’ai visité le roi d’Assur;
19 Amma zan komo da Isra’ila zuwa wurin kiwonsa zai kuwa yi kiwo a Karmel da Bashan; zai ƙosar da marmarinsa a tuddan Efraim da Gileyad.
Et je ramènerai Israël dans sa demeure, il paîtra sur le Carmel et en Basan, et sur la montagne d’Ephraïm et de Galaad son âme se rassasiera.
20 A kwanakin nan, da kuma a lokacin nan,” in ji Ubangiji, “za a yi bincike don laifin Isra’ila, amma ba za a samu ba, kuma don zunubin Yahuda, amma ba za a sami wani abu ba, gama zan gafarta wa raguwar da na rage.
En ces jours-là, et en ce temps-là, dit le Seigneur, on cherchera l’iniquité d’Israël et elle ne sera pas; le péché de Juda et il ne sera pas trouvé; parce que je serai propice à ceux que j’aurai laissés.
21 “Ku fāɗa wa ƙasar Meratayim da waɗanda suke zama a Fekod. Ku fafara, ku kashe kuma hallaka su sarai,” in ji Ubangiji. “Ku aikata dukan abin da na umarce ku.
Monte sur la terre des dominateurs, et visite ses habitants; dissipe et tue ce qui est derrière eux, dit le Seigneur; et fais tout selon que je t’ai ordonné.
22 Hargowar yaƙi tana a ƙasar, hargowar babbar hallaka!
Voix de guerre sur la terre et grande destruction.
23 Dubi yadda aka karya aka kuma ragargaza gudumar dukan duniya! Dubi yadda Babilon ta zama kufai a cikin al’ummai!
Comment a-t-il été rompu et brisé, le marteau de toute la terre? Comment Babylone a-t-elle été changée en un désert parmi les nations?
24 Na sa miki tarko, Babilon, kika kuwa kamu kafin ki sani; aka same ki aka kuma kama ki domin kin tayar wa Ubangiji.
Je t’ai enlacée, et tu as été prise, Babylone, et tu ne le savais pas; tu as été trouvée et saisie, parce que c’est le Seigneur que tu as provoqué.
25 Ubangiji ya buɗe taskar makamansa ya fitar da makaman fushinsa, gama Maɗaukaki Ubangiji Mai Iko Duka yana da aikin da zai yi a ƙasar Babiloniyawa.
Le Seigneur a ouvert son trésor et il en a tiré les instruments de sa colère, parce que le Seigneur, Dieu des armées, en a besoin dans la terre des Chaldéens.
26 Ku zo ku yi gāba da ita daga nesa. Ku buɗe rumbunanta; ku jibga ta kamar tsibin hatsi. Ku hallaka ta sarai kada ku bar mata raguwa.
Venez vers elle des confins les plus éloignés; ouvrez, afin que sortent ceux qui doivent la fouler aux pieds; ôtez de la voie les pierres, et mettez-les en monceaux, et tuez-la et qu’il n’y ait rien de reste.
27 Ku kashe dukan’yan bijimanta bari su gangara zuwa mayanka! Kaitonsu! Gama ranansu ta zo, lokaci ya yi da za a hukunta su.
Dissipez tous ses braves, qu’ils descendent à la tuerie; malheur à eux, parce qu’est venu leur jour, le temps de leur visite.
28 Ku saurari masu gudun hijira da masu neman mafaka daga Babilon suna furtawa a Sihiyona yadda Ubangiji Allahnmu ya ɗauki fansa, fansa domin haikalinsa.
Voix de ceux qui fuient, de ceux qui sont échappés de la terre de Babylone, afin qu’ils annoncent à Sion la vengeance du Seigneur, notre Dieu, la vengeance de son temple.
29 “Ku kira’yan baka a kan Babilon, dukan waɗanda suke jan baka. Ku yi sansani kewaye da ita duka; kada ku bar wani ya tsira. Ku sāka mata don ayyukanta; ku yi mata yadda ta yi. Gama ta tayar wa Ubangiji, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Annoncez à tous ceux qui tendent l’arc en si grand nombre de marcher contre Babylone; tenez-vous contre elle tout au autour, et que personne n’échappe; rendez-lui selon son œuvre; selon tout ce qu’elle a fait, faites-lui, parce que c’est contre le Seigneur qu’elle s’est élevée, contre le saint d’Israël.
30 Saboda haka, samarinta za su fāɗi a tituna; za a kawar da dukan sojojinta a wannan rana,” in ji Ubangiji.
C’est pour cela que ses jeunes hommes tomberont sur ses places et que tous ses hommes de guerre se tairont en ce jour-là, dit le Seigneur.
31 “Ga shi, ina gāba da ke, ya ke mai girman kai,” in ji Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, “gama ranarki ta zo, lokacin da za a hukunta ki.
Voilà que moi-même je viens à toi, superbe, dit le Seigneur, Dieu des armées, parce qu’est venu ton jour, le jour de ta visite.
32 Mai ɗaga kai za tă yi tuntuɓe ta kuma fāɗi kuma ba wanda zai taimake ta tă tashi; zan hura wuta a garuruwanta da za tă cinye duk waɗanda suke kewaye da ita.”
Et il tombera, le superbe, et il sera renversé, et il n’y aura personne qui le relèvera; et j’allumerai un feu dans ses villes; et il dévorera tout ce qui est autour de lui.
33 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “An danne mutanen Isra’ila, haka ma mutanen Yahuda. Dukan waɗanda suka kama su suna riƙe su kankan, suna kin barinsu su tafi.
Voici ce que dit le Seigneur des armées: Les fils d’Israël et les fils de Juda souffrent ensemble l’oppression: tous ceux qui les ont pris les retiennent, et ne veulent pas les laisser aller.
34 Duk da haka Mai Fansarsu yana da ƙarfi; Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa. Zai kāre muradunsu gabagadi don yă kawo hutu ga ƙasarsu, amma rashin hutu ga waɗanda suke zaune a Babilon.
Leur rédempteur est fort; son nom est le Seigneur des armées; en jugement il défendra leur cause, afin d’épouvanter la terre et d’agiter les habitants de Babylone.
35 “Akwai takobi a kan Babiloniyawa!” In ji Ubangiji “a kan waɗanda suke zama a Babilon da kuma a kan fadawanta da masu hikimarta!
Glaive sur les Chaldéens, dit le Seigneur, sur les habitants de Babylone, sur ses princes et ses sages.
36 Akwai takobi a kan annabawan ƙaryanta! Za su zama wawaye. Akwai takobi a kan jarumawanta! Za su cika da tsoro.
Glaive sur ses devins qui seront insensés; glaive sur ses braves qui seront dans l’effroi.
37 Akwai takobi a kan dawakanta da kekunan yaƙinta da kuma dukan baƙin da suke cikin mayaƙanta! Za su zama mata. Akwai takobi a kan dukiyarta! Za a washe su.
Glaive sur ses chevaux et sur ses chars, et sur tout le peuple qui est au milieu d’elle; et ils seront comme des femmes; glaive sur ses trésors qui seront pillés.
38 Fări a kan ruwanta! Za su bushe ƙaf. Gama ƙasa ce ta gumaka, gumakan da za su haukace da tsoro.
La sécheresse sera sur ses eaux, et elles tariront; parce que c’est la terre des images taillées au ciseau, et ils se glorifient dans des monstres.
39 “Saboda haka halittun hamada da kuraye za su zauna a can, a can kuma mujiya za tă zauna. Ba za a ƙara zauna ko a yi zama a cikinta ba daga tsara zuwa tsara.
À cause de cela, les dragons y habiteront avec les faunes qui recherchent les figues; et les autruches habiteront en elle; et elle ne sera plus habitée à jamais, elle ne sera pas reconstruite dans la suite des générations.
40 Yadda Allah ya tumɓuke Sodom da Gomorra tare da maƙwabtan garuruwansu,” in ji Ubangiji “haka ma ba wanda zai zauna a can; ba wani da zai zauna a cikinta.
Ainsi que le Seigneur a renversé Sodome et Gomorrhe, et ses voisines, dit le Seigneur; un homme n’y habitera pas, et le fils d’un homme n’y séjournera pas.
41 “Duba! Ga sojoji suna zuwa daga arewa; babbar al’umma da sarakuna masu yawa suna tahowa daga iyakokin duniya.
Voilà qu’un peuple vient de l’Aquilon, et une grande nation, et un grand nombre de rois s’élèveront des confins de la terre.
42 Suna riƙe da baka da māshi; mugaye ne marasa tausayi. Amonsu ya yi kamar rurin teku yayinda suke hawan dawakansu; suna zuwa kamar mutane a dāgār yaƙi don su fāɗa miki, ya Diyar Babilon.
Ils saisiront l’arc et le bouclier; ils sont cruels et impitoyables; leur voix comme la mer retentira; et sur leurs chevaux ils monteront comme un homme prêt au combat contre toi, fille de Babylone.
43 Sarkin Babilon ya ji rahotanni game da su, hannunsa kuma ya yi laƙwas. Wahala ta kama shi, zafi kamar na mace mai naƙuda.
Le roi de Babylone a appris la nouvelle de leur dessein, et ses mains ont défailli; l’angoisse l’a saisi, et la douleur, comme une femme en travail.
44 Kamar zaki mai haurawa daga kurmin Urdun zuwa wurin kiwo mai dausayi, zan fafare Babilon daga ƙasan nan da nan. Wane ne zaɓaɓɓen da zan naɗa domin wannan? Wane ne kamar ni da zai kalubalance ni? Kuma wanda makiyayi zai iya tsaya gāba da ni?”
Voilà que comme un lion il montera de l’orgueil du Jourdain vers une beauté puissante; parce que soudain je le ferai courir vers elle; et quel est l’élu que je préposerai sur elle? car qui est semblable à moi? qui tiendra contre moi? et quel est le pasteur qui résistera à mon visage?
45 Saboda haka, ku ji abin da Ubangiji ya shirya a kan Babilon, abin da ya nufa gāba da ƙasar Babiloniyawa. Za a kwashe ƙananan garkensu a tafi; zai hallaka wurin kiwonsu sarai saboda su.
À cause de cela, écoutez le dessein que le Seigneur a conçu en son esprit contre Babylone, et les pensées qu’il a méditées contre la terre des Chaldéens; il a dit: Je jure si les petits troupeaux, ne les enlèveront pas; et si leur habitation ne sera pas détruite avec eux.
46 Da jin an ci Babilon da yaƙi sai duniya ta girgiza; za a ji kukanta cikin al’ummai.
À la voix de la captivité de Babylone, la terre a été agitée, et une clameur parmi les nations a été entendue.

< Irmiya 50 >