< Irmiya 50 >

1 Ga maganar Ubangiji da ya yi ta wurin Irmiya annabi game da Babilon da kuma ƙasar Babiloniyawa.
Parole que prononça l’Eternel au sujet de Babel, du pays des Chaldéens par l’organe de Jérémie le prophète:
2 “Ka yi shela ka kuma furta a cikin al’ummai, ka tā da tuta ka kuma furta; kada ku ɓoye kome, amma ku ce, ‘Za a ci Babilon da yaƙi; za a kunyata Bel, Marduk ya cika da tsoro. Siffofinta za su sha kunya gumakanta za su cika da tsoro.’
"Annoncez-le parmi les nations, proclamez-le, dressez un signal, publiez-le sans rien dissimuler! dites: Babel est prise, Bel est confondu, Merodac est abattu; ses divinités sont couvertes de honte, ses idoles sont en pièces.
3 Al’umma daga arewa za tă fāɗa mata su mai da ƙasar kango. Ba wanda zai zauna a cikinta; mutane da dabbobi za su gudu.
Car du Nord un peuple s’avance contre elle, qui fait de son territoire une solitude où nul n’habite plus: hommes et bêtes, tous émigrent, s’en vont.
4 “A kwanakin nan, a wannan lokaci,” in ji Ubangiji, “mutanen Isra’ila da mutanen Yahuda gaba ɗaya za su tafi cikin hawaye su nemi Ubangiji Allahnsu.
En ces jours et en ce temps-là, dit le Seigneur, les fils d’Israël unis aux fils de Juda reviendront; ils chemineront, tout en pleurant, à la recherche de l’Eternel, leur Dieu.
5 Za su tambayi hanyar zuwa Sihiyona su kuma juya fuskokinsu wajenta. Za su zo su haɗa kansu ga Ubangiji a madawwamin alkawari da ba za a manta da shi ba.
C’Est de Sion qu’ils s’enquerront, le visage tourné dans sa direction; ils viendront et s’attacheront au Seigneur par un pacte éternel, qui ne sera pas oublié.
6 “Mutanena sun zama ɓatattun tumaki; makiyayansu sun bauɗar da su suka sa suna ta yawo a cikin duwatsu. Sun yi ta yawo a bisa dutse da tudu suka manta wurin hutunsu.
Mon peuple se composait de brebis égarées; leurs pasteurs les avaient fourvoyées, les laissant errer par les montagnes; elles vaguaient de hauteur en hauteur; oublieuses de leur gîte.
7 Duk wanda ya same su ya cinye su; abokan gābansu suka ce, ‘Ba mu da laifi, gama sun yi zunubi wa Ubangiji, wurin kiwonsu na gaske, Ubangiji, abin sa zuciyar kakanninsu.’
Tous ceux qui les rencontraient en faisaient leur pâture, et leurs ennemis disaient: "Nous ne faisons pas de mal, puisqu’ils ont péché contre l’Eternel, leur abri véridique, contre l’Eternel, espoir de leurs ancêtres."
8 “Ku gudu daga Babilon; ku bar ƙasar Babiloniyawa, ku zama kamar awakin da suke bi da garke.
Fuyez de l’enceinte de Babel, sortez du pays des Chaldéens, et soyez comme des béliers à la tête du troupeau!
9 Gama zan kuta in kuma kawo a kan Babilon haɗinkan manyan al’ummai na arewa. Za su ja dāgār gāba da ita, kuma daga arewa za a ci ta da yaƙi. Kibiyoyinsu za su zama kamar na gwanayen jarumawa waɗanda ba sa dawowa hannu wofi.
Car voici, du pays du Nord je fais surgir et marcher sur Babel une ligue de grandes nations, qui feront campagne contre elle, et c’est ainsi qu’elle sera prise. Leurs flèches ressemblent à un guerrier triomphant qui ne subit pas d’échec.
10 Saboda haka za a washe Babiloniyawa; dukan waɗanda suka washe ta za su ƙoshi,” in ji Ubangiji.
La Chaldée sera mise à sac; tous ceux qui la pilleront seront comblés, dit le Seigneur.
11 “Saboda kuna farin ciki kuna kuma murna, ku da kuka washe gādona, domin kuna tsalle kamar karsana mai sussuka hatsi kuna kuma haniniya kamar ingarmu.
Ah! réjouissez-vous, triomphez donc, vous les spoliateurs de mon héritage! Oui, ébattez-vous comme une génisse qui foule le blé et hennissez comme de fiers coursiers!
12 Mahaifiyarku za tă sha babbar kunya; ita da ta haife ku za tă sha kunya. Za tă zama mafi ƙanƙanta na al’ummai, jeji, busasshiyar ƙasa, hamada.
Elle va être entièrement confondue, votre mère; celle qui vous a donné le jour va connaître la rougeur de la honte. Tel sera le sort de ces nations: l’abandon, la ruine, la solitude.
13 Saboda fushin Ubangiji ba za tă zauna a cikinta ba amma za tă zama kufai gaba ɗaya. Duk waɗanda suka wuce Babilon za su ji tsoro su kuma yi tsaki saboda dukan mikinta.
Par suite de la colère du Seigneur, elle deviendra inhabitable, complètement désolée. Quiconque passera près de Babel Sera stupéfait et ricanera à la vue de toutes ses plaies.
14 “Ku ja dāgā kewaye da Babilon, dukanku waɗanda kuke jan baka. Ku harbe ta! Kada ku rage kibiyoyi, gama ta yi zunubi ga Ubangiji.
A vos rangs de bataille contre Babel, tout autour, vous tous qui bandez l’arc! tirez sur elle, ne ménagez pas les flèches, car elle s’est rendue coupable envers l’Eternel.
15 Ku yi kuwwa a kanta a kowane gefe! Ta miƙa wuya, hasumiyarta ta fāɗi, katangarta sun rushe. Da yake wannan sakayya ce ta Ubangiji, ku ɗauki fansa a kanta; yi mata yadda ta yi wa waɗansu.
Poussez le cri de guerre contre elle de toutes parts: elle tend les mains, ses créneaux tombent, ses murs s’écroulent, car ce sont les représailles de l’Eternel. Vengez-vous sur elle, faites-lui ce qu’elle a fait elle-même.
16 Ku datse wa Babilon mai shuka, da mai girbi lauje a lokacin girbi. Saboda takobin mai zalunci bari kowa ya koma ga mutanensa, bari kowa ya gudu zuwa ga ƙasarsa.
Exterminez dans Babel quiconque sème et quiconque manie la faucille au temps de la moisson. Devant le glaive meurtrier, que chacun se dirige vers son peuple, que chacun se réfugie dans son pays!
17 “Isra’ila garke ne da ya watse da zakoki suka kora. Na farkon da ya cinye shi sarkin Assuriya ne; na ƙarshen da ya ragargaza ƙasusuwansa Nebukadnezzar sarkin Babilon ne.”
Israël était une brebis pourchassée, que des lions avaient mise en fuite; le roi d’Assyrie fut le premier à le dévorer et voilà que ce dernier lui a broyé les os, Nabuchodonosor, roi de Babylone.
18 Saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Zan hukunta sarkin Babilon da ƙasarsa yadda na hukunta sarkin Assuriya.
Aussi l’Eternel-Cebaot, Dieu d’Israël, s’exprime-t-il en ces termes: Je vais demander des comptes au roi de Babylone et à son pays comme j’ai demandé des comptes au roi d’Assyrie.
19 Amma zan komo da Isra’ila zuwa wurin kiwonsa zai kuwa yi kiwo a Karmel da Bashan; zai ƙosar da marmarinsa a tuddan Efraim da Gileyad.
Et je ramènerai Israël à son pâturage, il pâturera sur le Carmel et le Basan, et sur le mont d’Ephraim et le Ghilead il se nourrira à satiété.
20 A kwanakin nan, da kuma a lokacin nan,” in ji Ubangiji, “za a yi bincike don laifin Isra’ila, amma ba za a samu ba, kuma don zunubin Yahuda, amma ba za a sami wani abu ba, gama zan gafarta wa raguwar da na rage.
En ces jours et en ce temps-là, dit le Seigneur, on recherchera le péché d’Israël, et il aura disparu, les prévarications de Juda, et on ne les retrouvera point; car mon pardon est assuré à ceux que j’aurai conservés.
21 “Ku fāɗa wa ƙasar Meratayim da waɗanda suke zama a Fekod. Ku fafara, ku kashe kuma hallaka su sarai,” in ji Ubangiji. “Ku aikata dukan abin da na umarce ku.
Sus au pays de "la double rébellion" et aux habitants de la ville du "châtiment!" Frappe par l’épée, extermine-les jusqu’au bout, dit le Seigneur, et exécute tout ce que je t’ai ordonné.
22 Hargowar yaƙi tana a ƙasar, hargowar babbar hallaka!
Un bruit de guerre retentit dans le pays, c’est une chute terrible.
23 Dubi yadda aka karya aka kuma ragargaza gudumar dukan duniya! Dubi yadda Babilon ta zama kufai a cikin al’ummai!
Comme il est abattu et brisé, le marteau qui broyait toute la terre! Comme elle est devenue, cette Babel, une ruine parmi toutes les nations!
24 Na sa miki tarko, Babilon, kika kuwa kamu kafin ki sani; aka same ki aka kuma kama ki domin kin tayar wa Ubangiji.
Je t’ai dressé un piège, ô Babel, et tu y as été prise, sans t’en apercevoir; te voilà atteinte et appréhendée, parce que tu t’étais insurgée contre le Seigneur!
25 Ubangiji ya buɗe taskar makamansa ya fitar da makaman fushinsa, gama Maɗaukaki Ubangiji Mai Iko Duka yana da aikin da zai yi a ƙasar Babiloniyawa.
L’Eternel a ouvert son arsenal, et en a sorti les instruments de sa colère, car il y a une oeuvre à accomplir pour l’Eternel-Cebaot sur la terre des Chaldéens.
26 Ku zo ku yi gāba da ita daga nesa. Ku buɗe rumbunanta; ku jibga ta kamar tsibin hatsi. Ku hallaka ta sarai kada ku bar mata raguwa.
Marchez contre elle de toutes les extrémités, ouvrez ses greniers, piétinez-la comme des javelles, détruisez-la: que rien d’elle ne subsiste!
27 Ku kashe dukan’yan bijimanta bari su gangara zuwa mayanka! Kaitonsu! Gama ranansu ta zo, lokaci ya yi da za a hukunta su.
Frappez du glaive tous ses taureaux! Qu’ils s’en aillent à la boucherie! Malheur à eux, car leur jour est arrivé, le temps de leur châtiment!
28 Ku saurari masu gudun hijira da masu neman mafaka daga Babilon suna furtawa a Sihiyona yadda Ubangiji Allahnmu ya ɗauki fansa, fansa domin haikalinsa.
Entendez les cris des fuyards, de ceux qui se sauvent du pays de Babei, annonçant dans Sion les représailles de l’Eternel, notre Dieu, la revanche de son sanctuaire.
29 “Ku kira’yan baka a kan Babilon, dukan waɗanda suke jan baka. Ku yi sansani kewaye da ita duka; kada ku bar wani ya tsira. Ku sāka mata don ayyukanta; ku yi mata yadda ta yi. Gama ta tayar wa Ubangiji, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Convoquez contre Babel des archers, tous les tireurs d’arbalète; cernez-la de toutes parts. Point de merci pour elle! Payez-la selon ses oeuvres, faites-lui comme elle a fait elle-même; car elle a défié le Seigneur, le Saint d’Israël.
30 Saboda haka, samarinta za su fāɗi a tituna; za a kawar da dukan sojojinta a wannan rana,” in ji Ubangiji.
Aussi ses jeunes gens tomberont-ils sur ses places publiques, et tous ses combattants seront anéantis en ce jour, dit le Seigneur.
31 “Ga shi, ina gāba da ke, ya ke mai girman kai,” in ji Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, “gama ranarki ta zo, lokacin da za a hukunta ki.
Voici, je vais m’en prendre à toi, modèle d’arrogance, dit le Seigneur, Eternel-Cebaot; car ton jour est venu, l’époque pour te châtier.
32 Mai ɗaga kai za tă yi tuntuɓe ta kuma fāɗi kuma ba wanda zai taimake ta tă tashi; zan hura wuta a garuruwanta da za tă cinye duk waɗanda suke kewaye da ita.”
Ce modèle d’arrogance trébuchera et tombera, sans personne pour le relever; je mettrai le feu à ses villes. et il dévorera tous ses alentours.
33 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “An danne mutanen Isra’ila, haka ma mutanen Yahuda. Dukan waɗanda suka kama su suna riƙe su kankan, suna kin barinsu su tafi.
Ainsi parle l’Eternel-Cebaot: Opprimés sont les enfants d’Israël, et les enfants de Juda tous ensemble; tous ceux qui les ont réduits en captivité les retiennent de force, refusent de les relâcher.
34 Duk da haka Mai Fansarsu yana da ƙarfi; Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa. Zai kāre muradunsu gabagadi don yă kawo hutu ga ƙasarsu, amma rashin hutu ga waɗanda suke zaune a Babilon.
Mais leur sauveur est puissantEternel-Cebaot est son nom, il prendra en mains leur cause, de façon à rendre la paix à la terre et à faire trembler les habitants de Babel.
35 “Akwai takobi a kan Babiloniyawa!” In ji Ubangiji “a kan waɗanda suke zama a Babilon da kuma a kan fadawanta da masu hikimarta!
Guerre aux Chaldéens, dit le Seigneur, aux habitants de Babel, à ses princes et à ses sages!
36 Akwai takobi a kan annabawan ƙaryanta! Za su zama wawaye. Akwai takobi a kan jarumawanta! Za su cika da tsoro.
Guerre aux trafiquants de mensonge! ils perdront la tête. Guerre à ses braves! ils seront brisés.
37 Akwai takobi a kan dawakanta da kekunan yaƙinta da kuma dukan baƙin da suke cikin mayaƙanta! Za su zama mata. Akwai takobi a kan dukiyarta! Za a washe su.
Guerre à ses coursiers, à ses chars et à tout ce ramassis de gens qu’elle abrite et qui deviendront comme des femmes! Guerre à ses trésors! Qu’ils soient pillés!
38 Fări a kan ruwanta! Za su bushe ƙaf. Gama ƙasa ce ta gumaka, gumakan da za su haukace da tsoro.
Sécheresse sur ses eaux, pour qu’elles tarissent! car c’est un pays d’idoles, et on s’y targue follement de ces épouvantails.
39 “Saboda haka halittun hamada da kuraye za su zauna a can, a can kuma mujiya za tă zauna. Ba za a ƙara zauna ko a yi zama a cikinta ba daga tsara zuwa tsara.
C’Est pourquoi chiens sauvages et chats sauvages s’y rencontreront, et des autruches en feront leur séjour: elle ne sera plus jamais habitée, jusqu’aux dernières générations personne ne s’y établira
40 Yadda Allah ya tumɓuke Sodom da Gomorra tare da maƙwabtan garuruwansu,” in ji Ubangiji “haka ma ba wanda zai zauna a can; ba wani da zai zauna a cikinta.
Tel le bouleversement de Sodome, de Gomorrhe et de leurs environs, dit le Seigneur; aucun homme n’y habitera, nul mortel n’y séjournera.
41 “Duba! Ga sojoji suna zuwa daga arewa; babbar al’umma da sarakuna masu yawa suna tahowa daga iyakokin duniya.
Voici, une nation arrive du Nord, un grand peuple et des rois puissants surgissent des extrémités de la terre.
42 Suna riƙe da baka da māshi; mugaye ne marasa tausayi. Amonsu ya yi kamar rurin teku yayinda suke hawan dawakansu; suna zuwa kamar mutane a dāgār yaƙi don su fāɗa miki, ya Diyar Babilon.
Ils sont armés d’arcs et de lances; ils sont inexorables et ne connaissent point la pitié. Leur voix est mugissante comme la mer; ils sont montés sur des chevaux, rangés en bataille comme des braves, contre toi, b fille de Babel.
43 Sarkin Babilon ya ji rahotanni game da su, hannunsa kuma ya yi laƙwas. Wahala ta kama shi, zafi kamar na mace mai naƙuda.
Leur renommée est parvenue au roi de Babel, et ses mains sont devenues défaillantes; l’effroi s’est emparé de lui, une angoisse comme celle d’une femme qui enfante.
44 Kamar zaki mai haurawa daga kurmin Urdun zuwa wurin kiwo mai dausayi, zan fafare Babilon daga ƙasan nan da nan. Wane ne zaɓaɓɓen da zan naɗa domin wannan? Wane ne kamar ni da zai kalubalance ni? Kuma wanda makiyayi zai iya tsaya gāba da ni?”
Voici, tel un lion monte des rives escarpées du Jourdain contre les solides bergeries, en un clin d’oeil je délogerai les habitants de Babel de là, et j’y établirai comme maître celui que j’aurai choisi; car qui est mon égal? Qui m’appellera en justice? Quel est le pasteur qui tiendra ferme contre moi?
45 Saboda haka, ku ji abin da Ubangiji ya shirya a kan Babilon, abin da ya nufa gāba da ƙasar Babiloniyawa. Za a kwashe ƙananan garkensu a tafi; zai hallaka wurin kiwonsu sarai saboda su.
Ecoutez donc les desseins de l’Eternel, qu’il a formés contre Babel et les projets qu’il a médités contre la terre des Chaldéens: certes, les plus humbles gardiens des troupeaux les traîneront dans la poussière, certes on fera s’écrouler sur eux leurs bergeries.
46 Da jin an ci Babilon da yaƙi sai duniya ta girgiza; za a ji kukanta cikin al’ummai.
Au bruit de la prise de Babel, la terre a frémi et une clameur se fait entendre parmi les nations.

< Irmiya 50 >