< Irmiya 50 >

1 Ga maganar Ubangiji da ya yi ta wurin Irmiya annabi game da Babilon da kuma ƙasar Babiloniyawa.
La parole que l’Éternel dit sur Babylone, sur le pays des Chaldéens, par Jérémie le prophète:
2 “Ka yi shela ka kuma furta a cikin al’ummai, ka tā da tuta ka kuma furta; kada ku ɓoye kome, amma ku ce, ‘Za a ci Babilon da yaƙi; za a kunyata Bel, Marduk ya cika da tsoro. Siffofinta za su sha kunya gumakanta za su cika da tsoro.’
Annoncez parmi les nations, et faites-le entendre, et élevez l’étendard; faites-le entendre, ne le cachez pas; dites: Babylone est prise, Bel est honteux; Merodac est brisé; ses idoles sont honteuses, ses images sont brisées.
3 Al’umma daga arewa za tă fāɗa mata su mai da ƙasar kango. Ba wanda zai zauna a cikinta; mutane da dabbobi za su gudu.
Car une nation est montée du nord contre elle; elle a mis en désolation son pays, et il n’y aura plus là d’habitant: tant les hommes que les bêtes se sont enfuis, ils s’en sont allés.
4 “A kwanakin nan, a wannan lokaci,” in ji Ubangiji, “mutanen Isra’ila da mutanen Yahuda gaba ɗaya za su tafi cikin hawaye su nemi Ubangiji Allahnsu.
En ces jours-là et en ce temps-là, dit l’Éternel, les fils d’Israël viendront, eux et les fils de Juda ensemble; ils iront, marchant et pleurant, et ils chercheront l’Éternel leur Dieu.
5 Za su tambayi hanyar zuwa Sihiyona su kuma juya fuskokinsu wajenta. Za su zo su haɗa kansu ga Ubangiji a madawwamin alkawari da ba za a manta da shi ba.
Ils s’enquerront de Sion; vers elle leur face [sera tournée]: Venez, attachons-nous à l’Éternel par une alliance éternelle qui ne sera pas oubliée.
6 “Mutanena sun zama ɓatattun tumaki; makiyayansu sun bauɗar da su suka sa suna ta yawo a cikin duwatsu. Sun yi ta yawo a bisa dutse da tudu suka manta wurin hutunsu.
Mon peuple est un troupeau perdu; leurs pasteurs les ont fait errer, les égarant sur les montagnes; ils sont allés de montagne en colline, ils ont oublié leur gîte.
7 Duk wanda ya same su ya cinye su; abokan gābansu suka ce, ‘Ba mu da laifi, gama sun yi zunubi wa Ubangiji, wurin kiwonsu na gaske, Ubangiji, abin sa zuciyar kakanninsu.’
Tous ceux qui les ont trouvés les ont dévorés; et leurs ennemis disent: Nous ne sommes pas coupables, parce qu’ils ont péché contre l’Éternel, contre la demeure de la justice, contre l’Éternel, l’attente de leurs pères.
8 “Ku gudu daga Babilon; ku bar ƙasar Babiloniyawa, ku zama kamar awakin da suke bi da garke.
Fuyez du milieu de Babylone, et sortez du pays des Chaldéens, et soyez comme les boucs [qui vont] devant le troupeau.
9 Gama zan kuta in kuma kawo a kan Babilon haɗinkan manyan al’ummai na arewa. Za su ja dāgār gāba da ita, kuma daga arewa za a ci ta da yaƙi. Kibiyoyinsu za su zama kamar na gwanayen jarumawa waɗanda ba sa dawowa hannu wofi.
Car voici, du pays du nord je réveillerai et je ferai monter contre Babylone un rassemblement de grandes nations qui se rangeront contre elle: de là elle sera prise. Leurs flèches sont comme celles d’un habile homme fort; pas une ne reviendra à vide.
10 Saboda haka za a washe Babiloniyawa; dukan waɗanda suka washe ta za su ƙoshi,” in ji Ubangiji.
Et la Chaldée sera un butin; tous ceux qui la pilleront seront rassasiés, dit l’Éternel;
11 “Saboda kuna farin ciki kuna kuma murna, ku da kuka washe gādona, domin kuna tsalle kamar karsana mai sussuka hatsi kuna kuma haniniya kamar ingarmu.
parce que vous vous êtes réjouis, parce que vous vous êtes égayés, vous qui avez pillé mon héritage, parce que vous avez bondi comme une génisse qui foule le blé, et que vous avez henni comme de puissants chevaux.
12 Mahaifiyarku za tă sha babbar kunya; ita da ta haife ku za tă sha kunya. Za tă zama mafi ƙanƙanta na al’ummai, jeji, busasshiyar ƙasa, hamada.
Votre mère est fort honteuse, celle qui vous enfanta est couverte d’opprobre: voici, [elle est] la dernière des nations, un désert, un pays stérile et une solitude!
13 Saboda fushin Ubangiji ba za tă zauna a cikinta ba amma za tă zama kufai gaba ɗaya. Duk waɗanda suka wuce Babilon za su ji tsoro su kuma yi tsaki saboda dukan mikinta.
À cause du courroux de l’Éternel elle ne sera pas habitée, elle sera tout entière une désolation; quiconque passera près de Babylone sera étonné et sifflera à cause de toutes ses plaies.
14 “Ku ja dāgā kewaye da Babilon, dukanku waɗanda kuke jan baka. Ku harbe ta! Kada ku rage kibiyoyi, gama ta yi zunubi ga Ubangiji.
Rangez-vous en bataille contre Babylone, tout alentour, vous tous qui bandez l’arc; tirez contre elle, n’épargnez pas les flèches, car elle a péché contre l’Éternel.
15 Ku yi kuwwa a kanta a kowane gefe! Ta miƙa wuya, hasumiyarta ta fāɗi, katangarta sun rushe. Da yake wannan sakayya ce ta Ubangiji, ku ɗauki fansa a kanta; yi mata yadda ta yi wa waɗansu.
Poussez des cris contre elle tout alentour! Elle s’est rendue, ses remparts sont tombés, ses murailles sont renversées, car c’est ici la vengeance de l’Éternel. Vengez-vous sur elle, faites-lui comme elle a fait!
16 Ku datse wa Babilon mai shuka, da mai girbi lauje a lokacin girbi. Saboda takobin mai zalunci bari kowa ya koma ga mutanensa, bari kowa ya gudu zuwa ga ƙasarsa.
Retranchez de Babylone celui qui sème, et celui qui tient la faucille au temps de la moisson. À cause de l’épée qui ravage, qu’ils s’en retournent chacun vers son peuple, et qu’ils fuient chacun vers son pays.
17 “Isra’ila garke ne da ya watse da zakoki suka kora. Na farkon da ya cinye shi sarkin Assuriya ne; na ƙarshen da ya ragargaza ƙasusuwansa Nebukadnezzar sarkin Babilon ne.”
Israël est une brebis chassée çà et là; les lions l’ont pourchassée. Le roi d’Assyrie, le premier, l’a dévorée; et celui-ci, le dernier, Nebucadretsar, roi de Babylone, lui a brisé les os.
18 Saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Zan hukunta sarkin Babilon da ƙasarsa yadda na hukunta sarkin Assuriya.
C’est pourquoi, ainsi dit l’Éternel des armées, le Dieu d’Israël: Voici, je visite le roi de Babylone et son pays, comme j’ai visité le roi d’Assyrie;
19 Amma zan komo da Isra’ila zuwa wurin kiwonsa zai kuwa yi kiwo a Karmel da Bashan; zai ƙosar da marmarinsa a tuddan Efraim da Gileyad.
et je ferai revenir Israël à ses pâturages; et il paîtra sur le Carmel et en Basan, et son âme sera rassasiée dans la montagne d’Éphraïm et en Galaad.
20 A kwanakin nan, da kuma a lokacin nan,” in ji Ubangiji, “za a yi bincike don laifin Isra’ila, amma ba za a samu ba, kuma don zunubin Yahuda, amma ba za a sami wani abu ba, gama zan gafarta wa raguwar da na rage.
En ces jours-là et en ce temps-là, dit l’Éternel, on cherchera l’iniquité d’Israël, et il n’y en aura point, et les péchés de Juda, et ils ne seront pas trouvés; car je pardonnerai à ceux que j’aurai fait demeurer de reste.
21 “Ku fāɗa wa ƙasar Meratayim da waɗanda suke zama a Fekod. Ku fafara, ku kashe kuma hallaka su sarai,” in ji Ubangiji. “Ku aikata dukan abin da na umarce ku.
Monte contre le pays doublement rebelle, contre lui et contre les habitants destinés à la visitation; dévaste et détruis entièrement derrière eux, dit l’Éternel, et fais selon tout ce que je t’ai commandé.
22 Hargowar yaƙi tana a ƙasar, hargowar babbar hallaka!
Le cri de guerre est dans le pays, et une grande ruine.
23 Dubi yadda aka karya aka kuma ragargaza gudumar dukan duniya! Dubi yadda Babilon ta zama kufai a cikin al’ummai!
Comment est mis en pièces et brisé le marteau de toute la terre! Comment Babylone est-elle réduite en désolation parmi les nations!
24 Na sa miki tarko, Babilon, kika kuwa kamu kafin ki sani; aka same ki aka kuma kama ki domin kin tayar wa Ubangiji.
Je t’ai tendu un piège, et aussi tu es prise, Babylone! et tu ne le savais pas; tu as été trouvée, et tu as aussi été saisie, parce que tu as combattu contre l’Éternel.
25 Ubangiji ya buɗe taskar makamansa ya fitar da makaman fushinsa, gama Maɗaukaki Ubangiji Mai Iko Duka yana da aikin da zai yi a ƙasar Babiloniyawa.
L’Éternel a ouvert son trésor, et il en a fait sortir les armes de son indignation; car c’est ici l’œuvre du Seigneur, l’Éternel des armées, dans le pays des Chaldéens.
26 Ku zo ku yi gāba da ita daga nesa. Ku buɗe rumbunanta; ku jibga ta kamar tsibin hatsi. Ku hallaka ta sarai kada ku bar mata raguwa.
Venez contre elle de toute part; ouvrez ses granges, entassez-la comme des gerbes et détruisez-la entièrement; qu’elle n’ait rien de reste!
27 Ku kashe dukan’yan bijimanta bari su gangara zuwa mayanka! Kaitonsu! Gama ranansu ta zo, lokaci ya yi da za a hukunta su.
Tuez tous ses taureaux; qu’ils descendent à la tuerie. Malheur à eux! car leur jour est venu, le temps de leur visitation.
28 Ku saurari masu gudun hijira da masu neman mafaka daga Babilon suna furtawa a Sihiyona yadda Ubangiji Allahnmu ya ɗauki fansa, fansa domin haikalinsa.
La voix de ceux qui fuient, qui sont réchappés du pays de Babylone, pour annoncer dans Sion la vengeance de l’Éternel, notre Dieu, la vengeance de son temple!
29 “Ku kira’yan baka a kan Babilon, dukan waɗanda suke jan baka. Ku yi sansani kewaye da ita duka; kada ku bar wani ya tsira. Ku sāka mata don ayyukanta; ku yi mata yadda ta yi. Gama ta tayar wa Ubangiji, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Convoquez des archers contre Babylone, tous ceux qui bandent l’arc! Campez contre elle tout alentour, qu’elle n’ait pas de réchappés; rendez-lui selon son œuvre, faites-lui selon tout ce qu’elle a fait; car elle a été fière contre l’Éternel, contre le Saint d’Israël.
30 Saboda haka, samarinta za su fāɗi a tituna; za a kawar da dukan sojojinta a wannan rana,” in ji Ubangiji.
C’est pourquoi ses jeunes gens tomberont dans ses places et tous ses hommes de guerre seront détruits en ce jour-là, dit l’Éternel.
31 “Ga shi, ina gāba da ke, ya ke mai girman kai,” in ji Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, “gama ranarki ta zo, lokacin da za a hukunta ki.
Voici, [j’en veux] à toi, orgueilleuse, dit le Seigneur, l’Éternel des armées; car ton jour est venu, le temps où je te visite.
32 Mai ɗaga kai za tă yi tuntuɓe ta kuma fāɗi kuma ba wanda zai taimake ta tă tashi; zan hura wuta a garuruwanta da za tă cinye duk waɗanda suke kewaye da ita.”
Et l’orgueilleuse a bronché et est tombée, et il n’y a personne qui la relève; et j’allumerai dans ses villes un feu qui dévorera tous ses alentours.
33 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “An danne mutanen Isra’ila, haka ma mutanen Yahuda. Dukan waɗanda suka kama su suna riƙe su kankan, suna kin barinsu su tafi.
Ainsi dit l’Éternel des armées: Les fils d’Israël et les fils de Juda ont été ensemble opprimés; et tous ceux qui les emmenèrent captifs les ont retenus, ils ont refusé de les laisser aller.
34 Duk da haka Mai Fansarsu yana da ƙarfi; Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa. Zai kāre muradunsu gabagadi don yă kawo hutu ga ƙasarsu, amma rashin hutu ga waɗanda suke zaune a Babilon.
Leur rédempteur est fort. Son nom est l’Éternel des armées; il prendra certainement en main leur cause, afin de donner du repos au pays et de troubler les habitants de Babylone.
35 “Akwai takobi a kan Babiloniyawa!” In ji Ubangiji “a kan waɗanda suke zama a Babilon da kuma a kan fadawanta da masu hikimarta!
L’épée est sur les Chaldéens, dit l’Éternel, et sur les habitants de Babylone, et sur ses princes, et sur ses sages;
36 Akwai takobi a kan annabawan ƙaryanta! Za su zama wawaye. Akwai takobi a kan jarumawanta! Za su cika da tsoro.
l’épée est sur les menteurs, et ils deviendront insensés; l’épée est sur ses hommes forts, et ils seront terrifiés;
37 Akwai takobi a kan dawakanta da kekunan yaƙinta da kuma dukan baƙin da suke cikin mayaƙanta! Za su zama mata. Akwai takobi a kan dukiyarta! Za a washe su.
l’épée est sur ses chevaux, et sur ses chars, et sur tout le peuple mélangé qui est au milieu d’elle, et ils seront comme des femmes; l’épée est sur ses trésors, et ils seront pillés;
38 Fări a kan ruwanta! Za su bushe ƙaf. Gama ƙasa ce ta gumaka, gumakan da za su haukace da tsoro.
la sécheresse est sur ses eaux, et elles tarissent; car c’est un pays d’images taillées, et ils sont fous de leurs affreuses idoles.
39 “Saboda haka halittun hamada da kuraye za su zauna a can, a can kuma mujiya za tă zauna. Ba za a ƙara zauna ko a yi zama a cikinta ba daga tsara zuwa tsara.
C’est pourquoi les bêtes du désert, avec des chacals, y habiteront, et il y habitera des autruches; et elle ne sera plus jamais habitée, et on n’y demeurera plus, de génération en génération.
40 Yadda Allah ya tumɓuke Sodom da Gomorra tare da maƙwabtan garuruwansu,” in ji Ubangiji “haka ma ba wanda zai zauna a can; ba wani da zai zauna a cikinta.
Comme dans la subversion que Dieu a faite de Sodome et de Gomorrhe et des villes voisines, dit l’Éternel, personne n’y habitera et aucun fils d’homme n’y séjournera.
41 “Duba! Ga sojoji suna zuwa daga arewa; babbar al’umma da sarakuna masu yawa suna tahowa daga iyakokin duniya.
Voici, un peuple vient du nord, et une grande nation et beaucoup de rois se réveillent des extrémités de la terre.
42 Suna riƙe da baka da māshi; mugaye ne marasa tausayi. Amonsu ya yi kamar rurin teku yayinda suke hawan dawakansu; suna zuwa kamar mutane a dāgār yaƙi don su fāɗa miki, ya Diyar Babilon.
Ils saisissent l’arc et le javelot; ils sont cruels, et ils n’ont pas de compassion; leur voix bruit comme la mer, et ils sont montés sur des chevaux, préparés comme un homme pour la guerre, contre toi, fille de Babylone.
43 Sarkin Babilon ya ji rahotanni game da su, hannunsa kuma ya yi laƙwas. Wahala ta kama shi, zafi kamar na mace mai naƙuda.
Le roi de Babylone en a entendu la rumeur, et ses mains sont devenues lâches; la détresse l’a saisi, l’angoisse comme celle d’une femme qui enfante.
44 Kamar zaki mai haurawa daga kurmin Urdun zuwa wurin kiwo mai dausayi, zan fafare Babilon daga ƙasan nan da nan. Wane ne zaɓaɓɓen da zan naɗa domin wannan? Wane ne kamar ni da zai kalubalance ni? Kuma wanda makiyayi zai iya tsaya gāba da ni?”
Voici, comme un lion il monte de la crue du Jourdain contre la demeure forte; car je les en chasserai précipitamment. Et qui est l’homme choisi, que je préposerai sur elle? Car qui est comme moi, et qui m’assignera le temps, et qui sera le pasteur qui se tiendra devant moi?
45 Saboda haka, ku ji abin da Ubangiji ya shirya a kan Babilon, abin da ya nufa gāba da ƙasar Babiloniyawa. Za a kwashe ƙananan garkensu a tafi; zai hallaka wurin kiwonsu sarai saboda su.
C’est pourquoi, écoutez le conseil de l’Éternel, qu’il a formé contre Babylone, et les pensées qu’il a pensées contre le pays des Chaldéens: Si les petits du troupeau ne les entraînent! S’il ne rend désolée pour eux [leur] habitation!…
46 Da jin an ci Babilon da yaƙi sai duniya ta girgiza; za a ji kukanta cikin al’ummai.
Au bruit de la prise de Babylone la terre est ébranlée, et il y a un cri, entendu parmi les nations.

< Irmiya 50 >