< Irmiya 50 >
1 Ga maganar Ubangiji da ya yi ta wurin Irmiya annabi game da Babilon da kuma ƙasar Babiloniyawa.
The word which Jehovah spake concerning Babylon, and concerning the land of the Chaldaeans, by Jeremiah the prophet.
2 “Ka yi shela ka kuma furta a cikin al’ummai, ka tā da tuta ka kuma furta; kada ku ɓoye kome, amma ku ce, ‘Za a ci Babilon da yaƙi; za a kunyata Bel, Marduk ya cika da tsoro. Siffofinta za su sha kunya gumakanta za su cika da tsoro.’
Tell ye among the nations, and proclaim, and lift up a standard! Proclaim ye; conceal it not; Say ye, “Babylon is taken, Bel is confounded, Merodach is in consternation, Her idols are confounded, Her images are in consternation.”
3 Al’umma daga arewa za tă fāɗa mata su mai da ƙasar kango. Ba wanda zai zauna a cikinta; mutane da dabbobi za su gudu.
For out of the North cometh up against her a nation Which shall make her land desolate, So that none shall dwell therein; Both man and beast are fled, They are gone.
4 “A kwanakin nan, a wannan lokaci,” in ji Ubangiji, “mutanen Isra’ila da mutanen Yahuda gaba ɗaya za su tafi cikin hawaye su nemi Ubangiji Allahnsu.
In those days, and at that time, saith Jehovah, The children of Israel shall come, They and the children of Judah together; They shall go weeping on their way, And shall seek Jehovah their God.
5 Za su tambayi hanyar zuwa Sihiyona su kuma juya fuskokinsu wajenta. Za su zo su haɗa kansu ga Ubangiji a madawwamin alkawari da ba za a manta da shi ba.
They shall ask the way to Zion, with their faces thitherward; They shall come, and shall join themselves to Jehovah In a perpetual covenant, that shall not be forgotten.
6 “Mutanena sun zama ɓatattun tumaki; makiyayansu sun bauɗar da su suka sa suna ta yawo a cikin duwatsu. Sun yi ta yawo a bisa dutse da tudu suka manta wurin hutunsu.
My people have been lost sheep; Their shepherds have caused them to go astray; They have caused them to wander upon the mountains; They have gone from mountain to hill, They have forgotten their fold.
7 Duk wanda ya same su ya cinye su; abokan gābansu suka ce, ‘Ba mu da laifi, gama sun yi zunubi wa Ubangiji, wurin kiwonsu na gaske, Ubangiji, abin sa zuciyar kakanninsu.’
All that found them devoured them; For their adversaries said, “We shall not be held guilty,” Because they had sinned against Jehovah, The fold of safety, and the hope of their fathers, Jehovah.
8 “Ku gudu daga Babilon; ku bar ƙasar Babiloniyawa, ku zama kamar awakin da suke bi da garke.
Flee ye out of Babylon, And go forth out of the land of the Chaldeans, And be ye like he-goats before the flock!
9 Gama zan kuta in kuma kawo a kan Babilon haɗinkan manyan al’ummai na arewa. Za su ja dāgār gāba da ita, kuma daga arewa za a ci ta da yaƙi. Kibiyoyinsu za su zama kamar na gwanayen jarumawa waɗanda ba sa dawowa hannu wofi.
For, behold, I will raise up and bring against Babylon An assembly of great nations from the land of the North, And they shall set themselves in array against her, And then shall she be taken; Their arrows shall be as those of an expert warrior; None shall return in vain.
10 Saboda haka za a washe Babiloniyawa; dukan waɗanda suka washe ta za su ƙoshi,” in ji Ubangiji.
And Chaldaea shall be a spoil; All that spoil her shall have their fill, saith Jehovah.
11 “Saboda kuna farin ciki kuna kuma murna, ku da kuka washe gādona, domin kuna tsalle kamar karsana mai sussuka hatsi kuna kuma haniniya kamar ingarmu.
Because ye rejoiced and exulted, O ye plunderers of my inheritance, Because ye wantoned like a thrashing heifer, And neighed like a stallion,
12 Mahaifiyarku za tă sha babbar kunya; ita da ta haife ku za tă sha kunya. Za tă zama mafi ƙanƙanta na al’ummai, jeji, busasshiyar ƙasa, hamada.
Your mother is utterly confounded; She that bore you is put to shame. Behold, the end of the nations, A wilderness, a dry land, a desert!
13 Saboda fushin Ubangiji ba za tă zauna a cikinta ba amma za tă zama kufai gaba ɗaya. Duk waɗanda suka wuce Babilon za su ji tsoro su kuma yi tsaki saboda dukan mikinta.
Because of the wrath of Jehovah, she shall not be inhabited, She shall be wholly desolate; Every one that passeth by Babylon shall be amazed, And hiss on account of all her plagues.
14 “Ku ja dāgā kewaye da Babilon, dukanku waɗanda kuke jan baka. Ku harbe ta! Kada ku rage kibiyoyi, gama ta yi zunubi ga Ubangiji.
Put yourselves in array against Babylon round about: All ye that bend the bow, shoot at her; Spare not the arrows! For she hath sinned against Jehovah.
15 Ku yi kuwwa a kanta a kowane gefe! Ta miƙa wuya, hasumiyarta ta fāɗi, katangarta sun rushe. Da yake wannan sakayya ce ta Ubangiji, ku ɗauki fansa a kanta; yi mata yadda ta yi wa waɗansu.
Raise the war-shout! She reacheth forth her hand; Her pillars are fallen; Her walls are thrown down; For it is the vengeance of Jehovah. Take ye vengeance upon her! As she hath done, do ye to her!
16 Ku datse wa Babilon mai shuka, da mai girbi lauje a lokacin girbi. Saboda takobin mai zalunci bari kowa ya koma ga mutanensa, bari kowa ya gudu zuwa ga ƙasarsa.
Cut ye off the sower from Babylon, And him that handleth the sickle in harvest-time! Because of the overpowering sword They shall turn every one to his own people, And they shall flee every one to his own land.
17 “Isra’ila garke ne da ya watse da zakoki suka kora. Na farkon da ya cinye shi sarkin Assuriya ne; na ƙarshen da ya ragargaza ƙasusuwansa Nebukadnezzar sarkin Babilon ne.”
Israel hath been like scattered sheep, Which the lions have driven away; First the king of Assyria devoured him, And last, this Nebuchadnezzar, the king of Babylon, hath broken his bones.
18 Saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Zan hukunta sarkin Babilon da ƙasarsa yadda na hukunta sarkin Assuriya.
Therefore thus saith Jehovah of hosts, the God of Israel: Behold, I will punish the king of Babylon and his land, As I have punished the king of Assyria.
19 Amma zan komo da Isra’ila zuwa wurin kiwonsa zai kuwa yi kiwo a Karmel da Bashan; zai ƙosar da marmarinsa a tuddan Efraim da Gileyad.
And I will bring back Israel to his own pasture, And he shall feed upon Carmel and Bashan, And satiate himself upon mount Ephraim and Gilead.
20 A kwanakin nan, da kuma a lokacin nan,” in ji Ubangiji, “za a yi bincike don laifin Isra’ila, amma ba za a samu ba, kuma don zunubin Yahuda, amma ba za a sami wani abu ba, gama zan gafarta wa raguwar da na rage.
In those days and at that time, saith Jehovah, The iniquity of Israel shall be sought for, and there shall be none; And the sins of Judah, and they shall not be found; For I will pardon those whom I cause to be left.
21 “Ku fāɗa wa ƙasar Meratayim da waɗanda suke zama a Fekod. Ku fafara, ku kashe kuma hallaka su sarai,” in ji Ubangiji. “Ku aikata dukan abin da na umarce ku.
Against the land of Rebellion go ye up, And against the inhabitants of Vengeance! Lay waste and utterly destroy after them, saith Jehovah, And do all which I have commanded thee!
22 Hargowar yaƙi tana a ƙasar, hargowar babbar hallaka!
The din of battle is in the land, And great destruction.
23 Dubi yadda aka karya aka kuma ragargaza gudumar dukan duniya! Dubi yadda Babilon ta zama kufai a cikin al’ummai!
How is the battle-hammer of the whole earth cut asunder and broken! How is Babylon become an astonishment to all the nations!
24 Na sa miki tarko, Babilon, kika kuwa kamu kafin ki sani; aka same ki aka kuma kama ki domin kin tayar wa Ubangiji.
I have laid a snare for thee, And thou hast been caught, O Babylon, When thou wast not aware! Thou hast been found and taken, Because thou hast contended against Jehovah.
25 Ubangiji ya buɗe taskar makamansa ya fitar da makaman fushinsa, gama Maɗaukaki Ubangiji Mai Iko Duka yana da aikin da zai yi a ƙasar Babiloniyawa.
Jehovah hath opened his armory, And hath brought out the weapons of his indignation; For the Lord Jehovah of hosts performeth a work against the land of the Chaldaeans.
26 Ku zo ku yi gāba da ita daga nesa. Ku buɗe rumbunanta; ku jibga ta kamar tsibin hatsi. Ku hallaka ta sarai kada ku bar mata raguwa.
Come against her from the utmost border! Open ye her barns, Cast her up into heaps, And destroy her utterly; Let nothing of her be left!
27 Ku kashe dukan’yan bijimanta bari su gangara zuwa mayanka! Kaitonsu! Gama ranansu ta zo, lokaci ya yi da za a hukunta su.
Slay all her bullocks, Let them go down to the slaughter! Woe unto them, For their day is come, The time of their punishment!
28 Ku saurari masu gudun hijira da masu neman mafaka daga Babilon suna furtawa a Sihiyona yadda Ubangiji Allahnmu ya ɗauki fansa, fansa domin haikalinsa.
The voice of them that flee and escape is heard from the land of Babylon, To make known to Zion the vengeance of Jehovah, our God, The vengeance for his temple.
29 “Ku kira’yan baka a kan Babilon, dukan waɗanda suke jan baka. Ku yi sansani kewaye da ita duka; kada ku bar wani ya tsira. Ku sāka mata don ayyukanta; ku yi mata yadda ta yi. Gama ta tayar wa Ubangiji, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Call together the archers against Babylon, All ye that bend the bow, encamp ye round about her; Let no one escape; Recompense her according to her work; According to all that she hath done, do ye to her! For she hath exalted herself against Jehovah, Against the Holy One of Israel.
30 Saboda haka, samarinta za su fāɗi a tituna; za a kawar da dukan sojojinta a wannan rana,” in ji Ubangiji.
Therefore shall her young men fall in the streets, And all her men of war shall be cut off in that day, saith Jehovah.
31 “Ga shi, ina gāba da ke, ya ke mai girman kai,” in ji Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, “gama ranarki ta zo, lokacin da za a hukunta ki.
Behold I am against thee, thou proud one, saith the Lord Jehovah of hosts; For thy day is come, The time of thy punishment.
32 Mai ɗaga kai za tă yi tuntuɓe ta kuma fāɗi kuma ba wanda zai taimake ta tă tashi; zan hura wuta a garuruwanta da za tă cinye duk waɗanda suke kewaye da ita.”
And the proud one shall stumble and fall, And none shall raise him up; And I will kindle a fire in his cities, And it shall devour all round about him.
33 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “An danne mutanen Isra’ila, haka ma mutanen Yahuda. Dukan waɗanda suka kama su suna riƙe su kankan, suna kin barinsu su tafi.
Thus saith Jehovah of hosts: The children of Israel and the children of Judah are oppressed together, And all that took them captives hold them fast; They refuse to let them go.
34 Duk da haka Mai Fansarsu yana da ƙarfi; Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa. Zai kāre muradunsu gabagadi don yă kawo hutu ga ƙasarsu, amma rashin hutu ga waɗanda suke zaune a Babilon.
But their redeemer is strong; Jehovah of hosts is his name. He will maintain their cause, So as to give rest to the land, And confusion to the inhabitants of Babylon.
35 “Akwai takobi a kan Babiloniyawa!” In ji Ubangiji “a kan waɗanda suke zama a Babilon da kuma a kan fadawanta da masu hikimarta!
The sword shall be upon the Chaldaeans, saith Jehovah, And upon the inhabitants of Babylon; And upon her princes, And upon her wise men;
36 Akwai takobi a kan annabawan ƙaryanta! Za su zama wawaye. Akwai takobi a kan jarumawanta! Za su cika da tsoro.
The sword upon her lying prophets, and they shall be fools; The sword upon her heroes, and they shall be dismayed;
37 Akwai takobi a kan dawakanta da kekunan yaƙinta da kuma dukan baƙin da suke cikin mayaƙanta! Za su zama mata. Akwai takobi a kan dukiyarta! Za a washe su.
The sword upon her horses, and upon her chariots, And against all the allied multitude that is within her, And they shall become women. The sword is upon their treasures, and they shall be plundered;
38 Fări a kan ruwanta! Za su bushe ƙaf. Gama ƙasa ce ta gumaka, gumakan da za su haukace da tsoro.
A drought is upon her waters, and they shall be dried up; For it is a land of graven images, And they put a mad trust in idols.
39 “Saboda haka halittun hamada da kuraye za su zauna a can, a can kuma mujiya za tă zauna. Ba za a ƙara zauna ko a yi zama a cikinta ba daga tsara zuwa tsara.
Therefore the wild beasts of the desert, with the jackals, shall dwell there, And therein shall the ostrich dwell. And it shall be no more inhabited forever, Neither shall it be dwelt in from generation to generation.
40 Yadda Allah ya tumɓuke Sodom da Gomorra tare da maƙwabtan garuruwansu,” in ji Ubangiji “haka ma ba wanda zai zauna a can; ba wani da zai zauna a cikinta.
As it was when God overthrew Sodom and Gomorrah, and the neighboring cities, saith Jehovah, There shall not a man abide there, Nor any son of man dwell therein.
41 “Duba! Ga sojoji suna zuwa daga arewa; babbar al’umma da sarakuna masu yawa suna tahowa daga iyakokin duniya.
Behold, a nation cometh from the North, And a great people and many kings shall rise up from the extremities of the earth.
42 Suna riƙe da baka da māshi; mugaye ne marasa tausayi. Amonsu ya yi kamar rurin teku yayinda suke hawan dawakansu; suna zuwa kamar mutane a dāgār yaƙi don su fāɗa miki, ya Diyar Babilon.
They bear the bow and the javelin; They are cruel, and show no mercy; Their voice roareth like the sea, And they ride upon horses, arrayed like a warrior, Against thee, O daughter of Babylon!
43 Sarkin Babilon ya ji rahotanni game da su, hannunsa kuma ya yi laƙwas. Wahala ta kama shi, zafi kamar na mace mai naƙuda.
The king of Babylon heareth the rumor concerning them, And his hands become feeble; Anguish taketh hold of him, Trembling, as of a woman in travail.
44 Kamar zaki mai haurawa daga kurmin Urdun zuwa wurin kiwo mai dausayi, zan fafare Babilon daga ƙasan nan da nan. Wane ne zaɓaɓɓen da zan naɗa domin wannan? Wane ne kamar ni da zai kalubalance ni? Kuma wanda makiyayi zai iya tsaya gāba da ni?”
Behold, like a lion from the pride of Jordan, he cometh up against the habitation of the rock; Suddenly will I drive them from her; And him who is chosen by me will I appoint over her; For who is like me? And who will summon me to trial? And who is the shepherd that will stand up against me?
45 Saboda haka, ku ji abin da Ubangiji ya shirya a kan Babilon, abin da ya nufa gāba da ƙasar Babiloniyawa. Za a kwashe ƙananan garkensu a tafi; zai hallaka wurin kiwonsu sarai saboda su.
Therefore hear ye the purpose of Jehovah, which he hath formed against Babylon, And the designs which he meditateth against the land of the Chaldaeans; Surely he [[the enemy]] shall drag them forth like feeble sheep, Surely he will come upon them, and make their pastures desolate.
46 Da jin an ci Babilon da yaƙi sai duniya ta girgiza; za a ji kukanta cikin al’ummai.
At the noise of the taking of Babylon, the earth trembleth, And the cry is heard among the nations.