< Irmiya 5 >
1 “Ku yi ta kai da kawowa a titunan Urushalima, ku dudduba ko’ina ku kuma lura, ku bincika cikin dandalinta. Ko za ku sami mutum guda wanda yake aikata adalci wanda yake kuma son bin gaskiya, sai in gafarta wa wannan birni.
Помандруйте по вулицях Єрусалиму, і розгля́ньтеся та розпізна́йте, і на майда́нах його пошукайте: чи не зна́йдете там люди́ни, чи нема там такого, що чинить за правом, що правди шукає, — то Я їм проба́чу!
2 Ko da yake suna cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye,’ duk da haka suna rantsuwar ƙarya.”
Коли ж вони кажуть: „ Як живий Господь“, то справді клянуться неправдою.
3 Ya Ubangiji, idanunka ba sa ganin gaskiya? Ka buge su, amma ba su ji zafi ba; ka ragargaza su, amma suka ƙi su gyara. Fuskarsu ta ƙeƙashe fiye da dutse suka ƙi su tuba.
Хіба ж о́чі Твої не для правди, о Господи? Ура́зив Ти їх, але їм не боли́ть, понищив Ти їх, та відмовились узяти поу́ку вони, обличчя свої поробили від скелі тверді́шими, відмо́вилися наверну́тись!
4 Na yi tunani, “Waɗannan ne kawai matalauta; su wawaye ne, gama ba su san hanyar Ubangiji ba, ko abubuwan da Allahnsu yake bukata ba.
А Я думав: Це про́сті лиш люди, безглу́зді, — вони бо не знають дороги Господньої, права Бога свого́.
5 Saboda haka zan tafi wurin shugabanni in yi musu magana; tabbatacce sun san hanyar Ubangiji, da abubuwan da Allahnsu yake bukata.” Amma da nufi guda su ma suka karye karkiyar suka tsintsinke sarƙoƙin.
Піду́ но собі до вельмо́жних і з ними помо́влю, — бо знають доро́гу Господню вони, право Бога свого, — та й вони усі ра́зом зламали ярмо́, а шле́ї пірва́ли!
6 Saboda haka zaki daga kurmi zai fāɗa musu, kyarkeci kuma daga hamada zai cinye su, damisa za tă yi musu ƙawanya kusa da garuruwansu yă yayyage duk wanda ya kuskura ya fita, gama tawayensu da girma yake jan bayansu kuma yana da yawa.
Тому лев лісови́й їх поб'є, погубить їх вовк степови́й, панте́ра чига́є на їхні міста́: кожен, хто вийде із них, пошмато́ваний буде, бо помно́жились їхні гріхи́, їхні відсту́пства числе́нними стали!
7 “Me zai sa in gafarta muku?’Ya’yanku sun yashe ni sun yi rantsuwa da allolin da ba alloli ba ne. Na biya musu dukan bukatunsu, duk da haka suka yi zina suka tattaru a gidajen karuwai.
Хіба через це Я проба́чу тобі: твої діти Мене полишили, і присяга́ються тим, хто не Бог. Я їх нагодува́в, а вони чужоло́жать і на́товпом ходять до дому блудниці,
8 An ciyar da su sosai, kamar ƙosassun ingarmu, masu jaraba, kowanne yana haniniya, yana neman matar maƙwabcinsa.
воло́чаться, мов жеребці́ відгодо́вані: кожен ірже́ до жони свого бли́жнього.
9 Ba zan hukunta su saboda wannan ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata in yi ramuwa a kan irin al’ummar nan ba?
Чи ж оцього Я не покараю? говорить Господь. І хіба над наро́дом, як цей, не помсти́ться душа Моя?
10 “Ku ratsa cikin gonakin inabinta ku cinye su, amma kada ku hallaka su gaba ɗaya. Ku kakkaɓe rassanta, gama waɗannan mutane ba na Ubangiji ba ne.
Зберіться на мури його та й пони́щте, але́ не вчиня́йте кінця́ їм! Усуньте підпо́ри його, бо вони не для Господа,
11 Gidan Isra’ila da gidan Yahuda sun zama marasa aminci gaba ɗaya gare ni” in ji Ubangiji.
бо зра́джуючи, Мене зра́див Ізраїлів дім та дім Юдин, говорить Госпо́дь.
12 Sun yi ƙarya a kan Ubangiji; sun ce, “Ba zai yi kome ba! Ba wata masifar da za tă same mu; ba za mu taɓa ganin takobi ko yunwa ba.
Вони відцура́лися Господа та говорили: „Немає Його, й зло не при́йде на нас, — ні меча, ані го́лоду ми не побачимо!“
13 Annabawa holoƙo ne kawai maganar kuwa ba ta cikinsu; saboda haka bari abin da suke faɗi ya koma kansu.”
А пророки поро́бляться вітром, і немає в них слова Господнього, — отак їм поро́блено буде!
14 Saboda haka ga abin Ubangiji Allah Maɗaukaki yana cewa, “Domin mutanen sun yi waɗannan maganganu, zan mai da maganata a bakinku wuta waɗannan mutane kuwa su zama itacen da za tă ci.
Тому́ вирікає отак Господь Бог Савао́т: За те, що гово́рите слово таке́, ось Я в у́ста твої вкладу слово Своє за огонь, а наро́д цей — то дро́ва, — і він пожере́ їх!
15 Ya gidan Isra’ila,” in ji Ubangiji, “Ina kawo al’umma daga nesa a kanku al’umma ce ta tun dā mai ƙarfin hali, mutane ne da ba ku san harshensu ba, waɗanda ba za ku fahimci abin da suke faɗa ba.
Ось Я приведу́ іздале́ка наро́да на вас, о доме Ізраїлів, каже Госпо́дь, — це сильний наро́д, старода́вній це люд, люд, що мови його ти не знаєш, і не зрозумієш, що він говори́тиме.
16 Kwarinsu kamar buɗaɗɗen kabari ne; dukansu jarumawa ne.
Його сагайда́к, як відчи́нений гріб, усі хоро́брі вони.
17 Za su cinye amfanin gonakinku da abincinku, za su cinye’ya’yanku maza da mata; za su cinye garkunan tumakinku da na awakinku, za su cinye’ya’yan inabinku da na ɓaurenku. Da takobi za su hallaka biranenku masu katanga.
І він пожере́ твоє жни́во та хліб твій, поїсть він синів твоїх та дочок твоїх, худобу дрібну́ та худобу велику твою пожере́, з'їсть твого́ виноградника й фіґу твою́, понищить мече́м тверди́нні міста твої, на які ти наді́єшся.
18 “Amma ko a cikin waɗancan kwanaki,” in ji Ubangiji, “ba zan hallaka ku gaba ɗaya ba.
Та й за тих днів, — говорить Госпо́дь, — не зроблю́ Я із вами кінця́!
19 Sa’ad da kuma mutanen suka yi tambaya, ‘Me ya sa Ubangiji Allahnmu ya yi dukan wannan gare mu?’ Sai ka amsa musu, ‘Yadda kuka yashe ni kuka kuma bauta wa baƙin alloli a ƙasarku, haka yanzu za ku bauta wa baƙi a ƙasar da ba taku ba.’
І буде, як скажуть: За́ що Господь, Бог наш зробив нам усе це? то ти скажеш до них: Як Мене ви покинули, і служите в вашому кра́ї бога́м чужозе́мним, так чужи́нцям служити ви будете в кра́ї не вашому!
20 “Ka sanar da wannan ga gidan Yaƙub ka yi shelarsa a Yahuda.
Сповістіть в домі Якова це, та оголосіть це в Юдеї, говорить Господь.
21 Ku ji wannan, ku wawaye marasa azanci, waɗanda suke da idanu amma ba sa gani, waɗanda suke da kunnuwa amma ba sa ji.
Почуй же оце, ти наро́де безумний й безсердий, який має очі — й не бачить, має вуха — й не чує!
22 Bai kamata ku ji tsorona ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata ku yi rawar jiki a gabana ba? Na sa yashi ya zama iyakar teku, madawwamiyar iyakar da ba zai tsallake ba. Raƙuman ruwa za su iya yin hauka, amma ba za su iya haye ta ba; za su iya yin ruri, amma ba za su iya ƙetare ta ba.
Чи Мене ви боятись не бу́дете, — каже Господь, чи тремтіти не будете перед лицем Моїм? Мене, що пісок покла́в за границю для моря, за вічну межу́, якої воно не пере́йде: хоч повста́нуть, та не перемо́жуть, і шумі́тимуть хвилі його, але не пересту́плять її!
23 Amma mutanen nan suna da tauraren zukata, kuma’yan tawaye ne; sun kauce suka kuma rabu da ni.
А серце в наро́да цього неслухня́не та непокі́рне, відпа́ли вони та й пішли.
24 Ba sa faɗa wa kansu, ‘Bari mu ji tsoron Ubangiji Allahnmu, wanda yake ba mu ruwan sama a kan kari na kaka da na bazara, wanda kullum yake tabbatar mana da girbi.’
І не сказали вони в своїм серці: Біймося ж Господа, нашого Бога, який дає дощ, дощ ранній та пізній ча́су його, стереже́ нам уста́влені тижні для жнив.
25 Laifofinku sun raba ku da waɗannan abubuwa; zunubanku sun hana ku samun alheri.
Ваші провини оце відхилили, а ваші гріхи́ від вас стри́мали цеє добро́.
26 “A cikin mutanena an sami mugaye waɗanda suke kwanton ɓauna kamar masu sa tarko wa tsuntsaye kamar waɗanda suke kafa tarko don su kama mutane.
Бо в наро́ді Моєму безбожники є, — чига́ють вони, немов той птахоло́в, вони сі́тки розста́вили, хапа́ють людей.
27 Kamar keji cike da tsuntsaye, gidajensu sun cika da ruɗu; sun yi arziki suka kuma zama masu iko
Як клі́тка, напо́внена пта́хами, так доми́ їхні повні ома́ни, — тому́ повиро́стали та збагати́лись вони!
28 suka kuma yi ƙiba, suka yi bul-bul. Mugayen ayyukansu ba su da iyaka; ba sa wa marayu shari’ar adalci, ba sa kāre’yancin matalauta.
Потовсті́ли вони та погла́дшали, переступа́ють також міру злого, справедливо вони не судили сирі́тського су́ду, — і мають пово́дження! — і не помагають убогим у їхній справі.
29 Bai kamata in hukunta su saboda wannan ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata in yi ramuwa a kan irin al’umma kamar wannan ba?
Чи ж оцьо́го Я не покараю? говорить Господь. І хіба над наро́дом, як цей, не помсти́ться душа Моя?
30 “Abin banmamaki da bantsoro ya faru a ƙasar.
Чудне́ та страшне́ стало в кра́ї:
31 Annabawa suna annabcin ƙarya, firistoci suna mulki da ikon kansu, mutanena kuma suna son haka. Amma me za ku yi a ƙarshe?
пророки віщу́ють неправду, при помочі їхній панують священики, і наро́д Мій оце так кохає! І що зробите ви, як кінець тому при́йде?