< Irmiya 5 >
1 “Ku yi ta kai da kawowa a titunan Urushalima, ku dudduba ko’ina ku kuma lura, ku bincika cikin dandalinta. Ko za ku sami mutum guda wanda yake aikata adalci wanda yake kuma son bin gaskiya, sai in gafarta wa wannan birni.
Parcourez les rues de Jérusalem; regardez, et considérez, et informez-vous dans les places, si vous trouvez un homme, s'il y en a un qui fasse ce qui est droit, qui cherche la vérité, et je pardonne à la ville.
2 Ko da yake suna cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye,’ duk da haka suna rantsuwar ƙarya.”
Même s'ils disent: L'Éternel est vivant! c'est faussement qu'ils jurent.
3 Ya Ubangiji, idanunka ba sa ganin gaskiya? Ka buge su, amma ba su ji zafi ba; ka ragargaza su, amma suka ƙi su gyara. Fuskarsu ta ƙeƙashe fiye da dutse suka ƙi su tuba.
Éternel! n'est-ce pas à la fidélité que tes yeux regardent? Tu les frappes, et ils n'éprouvent pas de douleur; tu les consumes, et ils ne veulent pas recevoir instruction. Ils ont endurci leurs faces plus qu'un rocher; ils refusent de se convertir.
4 Na yi tunani, “Waɗannan ne kawai matalauta; su wawaye ne, gama ba su san hanyar Ubangiji ba, ko abubuwan da Allahnsu yake bukata ba.
Je disais: mais ce ne sont que les petits; ils se montrent insensés, parce qu'ils ne connaissent pas la voie de l'Éternel, le droit de leur Dieu.
5 Saboda haka zan tafi wurin shugabanni in yi musu magana; tabbatacce sun san hanyar Ubangiji, da abubuwan da Allahnsu yake bukata.” Amma da nufi guda su ma suka karye karkiyar suka tsintsinke sarƙoƙin.
J'irai donc vers les grands et je leur parlerai; car eux, ils connaissent la voie de l'Éternel, le droit de leur Dieu. Mais, eux aussi, ils ont brisé le joug, rompu les liens!
6 Saboda haka zaki daga kurmi zai fāɗa musu, kyarkeci kuma daga hamada zai cinye su, damisa za tă yi musu ƙawanya kusa da garuruwansu yă yayyage duk wanda ya kuskura ya fita, gama tawayensu da girma yake jan bayansu kuma yana da yawa.
C'est pourquoi le lion de la forêt les tue; le loup du désert les ravage; le léopard est au guet contre leurs villes; quiconque en sortira sera dévoré. Car leurs rébellions se sont multipliées, leurs infidélités se sont renforcées.
7 “Me zai sa in gafarta muku?’Ya’yanku sun yashe ni sun yi rantsuwa da allolin da ba alloli ba ne. Na biya musu dukan bukatunsu, duk da haka suka yi zina suka tattaru a gidajen karuwai.
Pourquoi te pardonnerais-je? Tes fils m'ont abandonné, et ils jurent par ce qui n'est pas dieu; je les ai rassasiés, et ils ont commis adultère; ils se pressent en foule dans la maison de la prostituée.
8 An ciyar da su sosai, kamar ƙosassun ingarmu, masu jaraba, kowanne yana haniniya, yana neman matar maƙwabcinsa.
Ils sont comme des chevaux bien nourris, qui courent çà et là; ils hennissent chacun après la femme de son prochain.
9 Ba zan hukunta su saboda wannan ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata in yi ramuwa a kan irin al’ummar nan ba?
Ne punirais-je point ces choses-là, dit l'Éternel, et mon âme ne se vengerait-elle pas d'une telle nation?
10 “Ku ratsa cikin gonakin inabinta ku cinye su, amma kada ku hallaka su gaba ɗaya. Ku kakkaɓe rassanta, gama waɗannan mutane ba na Ubangiji ba ne.
Montez sur ses murailles, et renversez-les! Mais ne détruisez pas entièrement. Otez ses sarments, car ils ne sont pas à l'Éternel!
11 Gidan Isra’ila da gidan Yahuda sun zama marasa aminci gaba ɗaya gare ni” in ji Ubangiji.
Car la maison d'Israël et la maison de Juda ont agi très perfidement envers moi, dit l'Éternel.
12 Sun yi ƙarya a kan Ubangiji; sun ce, “Ba zai yi kome ba! Ba wata masifar da za tă same mu; ba za mu taɓa ganin takobi ko yunwa ba.
Ils ont renié l'Éternel, et ils ont dit: “Ce n'est pas lui! et le mal ne viendra pas sur nous; nous ne verrons ni l'épée ni la famine.
13 Annabawa holoƙo ne kawai maganar kuwa ba ta cikinsu; saboda haka bari abin da suke faɗi ya koma kansu.”
Les prophètes ne sont que du vent; il n'y a point d'oracle en eux; qu'il leur soit fait ainsi! “
14 Saboda haka ga abin Ubangiji Allah Maɗaukaki yana cewa, “Domin mutanen sun yi waɗannan maganganu, zan mai da maganata a bakinku wuta waɗannan mutane kuwa su zama itacen da za tă ci.
C'est pourquoi, ainsi a dit l'Éternel, le Dieu des armées: Parce que vous avez prononcé cette parole, voici, je fais de mes paroles dans ta bouche un feu, et de ce peuple du bois, et ce feu les consumera.
15 Ya gidan Isra’ila,” in ji Ubangiji, “Ina kawo al’umma daga nesa a kanku al’umma ce ta tun dā mai ƙarfin hali, mutane ne da ba ku san harshensu ba, waɗanda ba za ku fahimci abin da suke faɗa ba.
Voici, je fais venir de loin une nation contre vous, maison d'Israël, dit l'Éternel; c'est une nation puissante, une nation ancienne, une nation dont tu ne sauras point la langue, et tu n'entendras point ce qu'elle dira.
16 Kwarinsu kamar buɗaɗɗen kabari ne; dukansu jarumawa ne.
Son carquois est comme un tombeau ouvert; tous, ils sont vaillants.
17 Za su cinye amfanin gonakinku da abincinku, za su cinye’ya’yanku maza da mata; za su cinye garkunan tumakinku da na awakinku, za su cinye’ya’yan inabinku da na ɓaurenku. Da takobi za su hallaka biranenku masu katanga.
Elle dévorera ta moisson et ton pain; elle dévorera tes fils et tes filles; elle dévorera tes brebis et tes bœufs; elle dévorera ta vigne et ton figuier; elle détruira par l'épée tes villes fortes dans lesquelles tu te confies.
18 “Amma ko a cikin waɗancan kwanaki,” in ji Ubangiji, “ba zan hallaka ku gaba ɗaya ba.
Toutefois, même en ces jours-là, dit l'Éternel, je ne vous achèverai pas entièrement.
19 Sa’ad da kuma mutanen suka yi tambaya, ‘Me ya sa Ubangiji Allahnmu ya yi dukan wannan gare mu?’ Sai ka amsa musu, ‘Yadda kuka yashe ni kuka kuma bauta wa baƙin alloli a ƙasarku, haka yanzu za ku bauta wa baƙi a ƙasar da ba taku ba.’
Et il arrivera que vous direz: Pourquoi l'Éternel notre Dieu nous a-t-il fait toutes ces choses? Tu leur diras: Comme vous m'avez abandonné, et que vous avez servi les dieux de l'étranger dans votre pays, ainsi servirez-vous les étrangers dans un pays qui ne sera pas à vous.
20 “Ka sanar da wannan ga gidan Yaƙub ka yi shelarsa a Yahuda.
Faites savoir ceci à la maison de Jacob, publiez-le en Juda, et dites:
21 Ku ji wannan, ku wawaye marasa azanci, waɗanda suke da idanu amma ba sa gani, waɗanda suke da kunnuwa amma ba sa ji.
Écoutez donc ceci, peuple insensé et dépourvu de sens, qui avez des yeux et ne voyez point, des oreilles et n'entendez point.
22 Bai kamata ku ji tsorona ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata ku yi rawar jiki a gabana ba? Na sa yashi ya zama iyakar teku, madawwamiyar iyakar da ba zai tsallake ba. Raƙuman ruwa za su iya yin hauka, amma ba za su iya haye ta ba; za su iya yin ruri, amma ba za su iya ƙetare ta ba.
Ne me craindrez-vous pas, dit l'Éternel, ne tremblerez-vous pas devant moi, qui ai posé le sable pour limite à la mer, borne éternelle qu'elle ne passera point? Ses vagues s'agitent, mais elles sont impuissantes; elles grondent, mais elles ne la passeront point.
23 Amma mutanen nan suna da tauraren zukata, kuma’yan tawaye ne; sun kauce suka kuma rabu da ni.
Mais ce peuple a un cœur rétif et rebelle; ils reculent, ils s'en vont;
24 Ba sa faɗa wa kansu, ‘Bari mu ji tsoron Ubangiji Allahnmu, wanda yake ba mu ruwan sama a kan kari na kaka da na bazara, wanda kullum yake tabbatar mana da girbi.’
Ils ne disent pas dans leur cœur: Craignons donc l'Éternel, notre Dieu, qui donne la pluie de la première et de la dernière saison, et nous garde les semaines ordonnées pour la moisson.
25 Laifofinku sun raba ku da waɗannan abubuwa; zunubanku sun hana ku samun alheri.
Vos iniquités ont détourné tout cela; vos péchés retiennent loin de vous le bien.
26 “A cikin mutanena an sami mugaye waɗanda suke kwanton ɓauna kamar masu sa tarko wa tsuntsaye kamar waɗanda suke kafa tarko don su kama mutane.
Car il s'est trouvé dans mon peuple des méchants, qui épient comme l'oiseleur qui tend des lacets; ils dressent des pièges mortels, et prennent des hommes.
27 Kamar keji cike da tsuntsaye, gidajensu sun cika da ruɗu; sun yi arziki suka kuma zama masu iko
Comme une cage est remplie d'oiseaux, ainsi leurs maisons sont remplies de fraude; aussi sont-ils devenus grands et riches.
28 suka kuma yi ƙiba, suka yi bul-bul. Mugayen ayyukansu ba su da iyaka; ba sa wa marayu shari’ar adalci, ba sa kāre’yancin matalauta.
Ils sont engraissés, ils sont brillants; ils ont surpassé tout mal, ils ne jugent point la cause, la cause de l'orphelin, et ils prospèrent; ils ne font pas droit aux pauvres.
29 Bai kamata in hukunta su saboda wannan ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata in yi ramuwa a kan irin al’umma kamar wannan ba?
Ne punirais-je point ces choses-là, dit l'Éternel? mon âme ne se vengerait-elle pas d'une telle nation?
30 “Abin banmamaki da bantsoro ya faru a ƙasar.
Une chose étonnante, horrible, se fait dans le pays:
31 Annabawa suna annabcin ƙarya, firistoci suna mulki da ikon kansu, mutanena kuma suna son haka. Amma me za ku yi a ƙarshe?
Les prophètes prophétisent le mensonge, et les sacrificateurs dominent par leur moyen, et mon peuple a pris plaisir à cela! Que ferez-vous donc quand viendra la fin?