< Irmiya 5 >
1 “Ku yi ta kai da kawowa a titunan Urushalima, ku dudduba ko’ina ku kuma lura, ku bincika cikin dandalinta. Ko za ku sami mutum guda wanda yake aikata adalci wanda yake kuma son bin gaskiya, sai in gafarta wa wannan birni.
Go everywhere through the streets of Jerusalem. Look and pay attention! Search all through her city squares to see if you can find even just one person who does what's right, anyone who is faithful, and I'll forgive the city.
2 Ko da yake suna cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye,’ duk da haka suna rantsuwar ƙarya.”
They may make promises in my name, but they're not sincere.
3 Ya Ubangiji, idanunka ba sa ganin gaskiya? Ka buge su, amma ba su ji zafi ba; ka ragargaza su, amma suka ƙi su gyara. Fuskarsu ta ƙeƙashe fiye da dutse suka ƙi su tuba.
Lord, aren't you always looking for faithfulness? You beat them, but they didn't care. You just about destroyed them, but they refused to accept your discipline. They were stubborn, hard as rock, and they wouldn't repent.
4 Na yi tunani, “Waɗannan ne kawai matalauta; su wawaye ne, gama ba su san hanyar Ubangiji ba, ko abubuwan da Allahnsu yake bukata ba.
Then I said to myself, “These people are only the poor—they're just fools who don't know any better. They certainly don't know what the Lord wants, God's right way of living.
5 Saboda haka zan tafi wurin shugabanni in yi musu magana; tabbatacce sun san hanyar Ubangiji, da abubuwan da Allahnsu yake bukata.” Amma da nufi guda su ma suka karye karkiyar suka tsintsinke sarƙoƙin.
Let me go to and talk to the ones in charge. They would surely know what the Lord wants, God's right way of living.” But they had all broken off the yoke as well, and ripped off the chains.
6 Saboda haka zaki daga kurmi zai fāɗa musu, kyarkeci kuma daga hamada zai cinye su, damisa za tă yi musu ƙawanya kusa da garuruwansu yă yayyage duk wanda ya kuskura ya fita, gama tawayensu da girma yake jan bayansu kuma yana da yawa.
As a result a lion from the forest will attack them; a wolf from the desert will rip them apart. A leopard will lie in wait for them near their towns, ready to tear to pieces anyone who goes outside. For they keep on rebelling, and turn away from me so often.
7 “Me zai sa in gafarta muku?’Ya’yanku sun yashe ni sun yi rantsuwa da allolin da ba alloli ba ne. Na biya musu dukan bukatunsu, duk da haka suka yi zina suka tattaru a gidajen karuwai.
Why should I forgive you? Your children have abandoned me and believe in gods that are not gods. I gave them everything they need, yet they went and committed adultery, gathering together at prostitutes' houses.
8 An ciyar da su sosai, kamar ƙosassun ingarmu, masu jaraba, kowanne yana haniniya, yana neman matar maƙwabcinsa.
They're like virile stallions wanting sex, each of them neighing with lust after his neighbor's wife.
9 Ba zan hukunta su saboda wannan ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata in yi ramuwa a kan irin al’ummar nan ba?
Shouldn't I punish them for all this? declares the Lord. Shouldn't I retaliate for what this nation has done?
10 “Ku ratsa cikin gonakin inabinta ku cinye su, amma kada ku hallaka su gaba ɗaya. Ku kakkaɓe rassanta, gama waɗannan mutane ba na Ubangiji ba ne.
Go through her vineyards and damage them, but don't destroy them completely. Rip off her branches, because they don't belong to the Lord.
11 Gidan Isra’ila da gidan Yahuda sun zama marasa aminci gaba ɗaya gare ni” in ji Ubangiji.
The people of Israel and Judah have completely betrayed me, declares the Lord.
12 Sun yi ƙarya a kan Ubangiji; sun ce, “Ba zai yi kome ba! Ba wata masifar da za tă same mu; ba za mu taɓa ganin takobi ko yunwa ba.
They have lied about the Lord, saying, “He won't do anything. Nothing bad will happen to us. We won't have war or famine.
13 Annabawa holoƙo ne kawai maganar kuwa ba ta cikinsu; saboda haka bari abin da suke faɗi ya koma kansu.”
The prophets are just like the wind. The Lord doesn't speak through them. What they predict can happen to them!”
14 Saboda haka ga abin Ubangiji Allah Maɗaukaki yana cewa, “Domin mutanen sun yi waɗannan maganganu, zan mai da maganata a bakinku wuta waɗannan mutane kuwa su zama itacen da za tă ci.
So this is the reply from the Lord God Almighty: Because of what you've said, I will make my words like a fire in your mouth and you people like the wood it burns up.
15 Ya gidan Isra’ila,” in ji Ubangiji, “Ina kawo al’umma daga nesa a kanku al’umma ce ta tun dā mai ƙarfin hali, mutane ne da ba ku san harshensu ba, waɗanda ba za ku fahimci abin da suke faɗa ba.
Look! I am bringing a nation from far away to attack you, people of Israel, declares the Lord. It's a powerful nation that has existed for a long time; it's a nation whose language you don't know, and when they speak you can't understand them.
16 Kwarinsu kamar buɗaɗɗen kabari ne; dukansu jarumawa ne.
Their arrows bring death; they are all strong warriors.
17 Za su cinye amfanin gonakinku da abincinku, za su cinye’ya’yanku maza da mata; za su cinye garkunan tumakinku da na awakinku, za su cinye’ya’yan inabinku da na ɓaurenku. Da takobi za su hallaka biranenku masu katanga.
They will consume your harvest and your food; they will destroy your sons and your daughters; they will eat your flocks and your herds; they will feed on your vines and your fig trees. They will attack and will destroy the fortified towns that you have so much confidence in.
18 “Amma ko a cikin waɗancan kwanaki,” in ji Ubangiji, “ba zan hallaka ku gaba ɗaya ba.
But even at that time I won't completely destroy you, declares the Lord.
19 Sa’ad da kuma mutanen suka yi tambaya, ‘Me ya sa Ubangiji Allahnmu ya yi dukan wannan gare mu?’ Sai ka amsa musu, ‘Yadda kuka yashe ni kuka kuma bauta wa baƙin alloli a ƙasarku, haka yanzu za ku bauta wa baƙi a ƙasar da ba taku ba.’
When people ask you Jeremiah, “Why did the Lord our God do all these things to us?” you are to tell them, “In the same way you have abandoned me and served foreign gods here in your country, so you will serve foreigners in a country that isn't your own.”
20 “Ka sanar da wannan ga gidan Yaƙub ka yi shelarsa a Yahuda.
Announce this to the people of Jacob and Judah:
21 Ku ji wannan, ku wawaye marasa azanci, waɗanda suke da idanu amma ba sa gani, waɗanda suke da kunnuwa amma ba sa ji.
Listen to this, you foolish, stupid people, who have eyes but don't see, who have ears but don't hear.
22 Bai kamata ku ji tsorona ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata ku yi rawar jiki a gabana ba? Na sa yashi ya zama iyakar teku, madawwamiyar iyakar da ba zai tsallake ba. Raƙuman ruwa za su iya yin hauka, amma ba za su iya haye ta ba; za su iya yin ruri, amma ba za su iya ƙetare ta ba.
Aren't you afraid of what I can do? declares the Lord. Don't you think you should tremble in my presence? I am the one who set up the shore as the sea's boundary, an everlasting limit that it can't cross. The waves crash against it, but they can't defeat it. They roar, but they can't cross the barrier.
23 Amma mutanen nan suna da tauraren zukata, kuma’yan tawaye ne; sun kauce suka kuma rabu da ni.
But you people have a stubborn and rebellious attitude. You have left me and gone your own way.
24 Ba sa faɗa wa kansu, ‘Bari mu ji tsoron Ubangiji Allahnmu, wanda yake ba mu ruwan sama a kan kari na kaka da na bazara, wanda kullum yake tabbatar mana da girbi.’
You didn't think to say, “We should appreciate the Lord our God, who sends the autumn and spring rains at the right time, who makes sure we can have a harvest every year.”
25 Laifofinku sun raba ku da waɗannan abubuwa; zunubanku sun hana ku samun alheri.
Your wrong actions have taken these benefits from you; your sins have deprived you of my blessings.
26 “A cikin mutanena an sami mugaye waɗanda suke kwanton ɓauna kamar masu sa tarko wa tsuntsaye kamar waɗanda suke kafa tarko don su kama mutane.
For there are wicked men among my people. They're like bird-trappers, secretly watching and waiting to catch people in their snare.
27 Kamar keji cike da tsuntsaye, gidajensu sun cika da ruɗu; sun yi arziki suka kuma zama masu iko
Their homes are full of their ill-gotten gains, like cages full of birds. That's why they've become powerful and rich.
28 suka kuma yi ƙiba, suka yi bul-bul. Mugayen ayyukansu ba su da iyaka; ba sa wa marayu shari’ar adalci, ba sa kāre’yancin matalauta.
They've grown fat and smooth, and have become experts in evil. They deny justice to orphans, and they don't defend the rights of those in need.
29 Bai kamata in hukunta su saboda wannan ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata in yi ramuwa a kan irin al’umma kamar wannan ba?
Shouldn't I punish them for all this? declares the Lord. Shouldn't I retaliate for what this nation has done?
30 “Abin banmamaki da bantsoro ya faru a ƙasar.
Something horrible, something terrible has happened here in this country.
31 Annabawa suna annabcin ƙarya, firistoci suna mulki da ikon kansu, mutanena kuma suna son haka. Amma me za ku yi a ƙarshe?
The prophets give false prophecies; the priests rule as they please. My people love it like this, but what will you do when it all falls apart?