< Irmiya 49 >
1 Game da Ammonawa. Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Isra’ila ba shi da’ya’ya maza ne? Ba shi da magāda ne? To, me ya sa Molek ya mallaki Gad? Me ya sa mutanensa suka zama a garuruwansa?
К сыном Аммоним тако глаголет Господь: еда не суть сынове Израилевы, или наследника несть им? Почто убо прия наследие Мелхом Гада, и людие его во градех его живяху?
2 Amma kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan yi kirarin yaƙi a kan Rabba ta Ammonawa; zai zama tarin juji, za a sa wuta a ƙauyukan da suke kewayenta. Sa’an nan Isra’ila zai kori waɗanda suka kore shi,” in ji Ubangiji.
Сего ради, се, дние грядут, глаголет Господь, и оглашу на Равваф сынов Аммоних ратный звук, и будет в непроходная и в пагубу, и требища его огнем сожжена будут, и восприимет Израиль власть свою, глаголет Господь.
3 “Ki yi kuka, ya Heshbon, gama an hallaka Ai! Ku tā da murya ku yi kuka, ya mazaunan Rabba! Ku sa tufafin makoki; ku ruga nan da can a cikin katanga, gama Molek zai tafi bauta, tare da firistocinsa da kuma fadawansa.
Возопий, Есевоне, яко погибе Гай: возопийте, дщери Раввафски, препояшитеся вретищами, рыдайте и бегайте по забралом, яко Мелхом во плен отведется, священницы и князи его вкупе.
4 Me ya sa kuke taƙama da kwarurukanku, taƙama da kwarurukanku masu amfani? Ya ke diya marar aminci, kin dogara a wadatarki kika kuma ce, ‘Wa zai iya fāɗa mini?’
Что хвалишися во удолиих? Стече удолие твое, дщи безстудная, уповающая на богатства своя, глаголющи: кто приидет на мя?
5 Zan kawo razana a kanki daga waɗanda suke kewaye da ke,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Za a kore kowannenku, babu wani da zai tattara masu gudun hijira.
Се, Аз наведу на тя страх, глаголет Господь Вседержитель, от всех сущих окрест тебе: и разсеетеся вси от лица его, и не будет собирающаго бежащих.
6 “Duk da haka, daga baya, zan maido da wadatar Ammonawa,” in ji Ubangiji.
И посем возвращу пленники сынов Аммоних, глаголет Господь.
7 Game da Edom. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Babu sauran hikima a Teman ne? Shawara ta ɓace daga masu basira ne? Hikimarsu ta ruɓe ne?
Ко Идумеи сия глаголет Господь Вседержитель: еда есть ктому мудрость во Фемане? Погибе совет от разумных, непотребна бысть мудрость их,
8 Ku juya ku gudu, ku ɓuya a cikin kogwanni masu zurfi, ku da kuke zama a Dedan, gama zan kawo masifa a kan Isuwa a lokacin da zan hukunta shi.
попрано бысть место их: снидите в пропасть к седению, живущии во Дедане: яко жестокая сотвори: (погибель Исавлю) наведох нань во время, в неже посетих его.
9 In masu tsinkar’ya’yan inabi suka zo maka, ba za su rage’ya’yan inabi kaɗan ba? In ɓarayi suka zo da dare, ba za su sata abin da kawai suke bukata ba?
Яко оымателие вина приидоша на тя, не оставят тебе останков: аки татие в нощи возложат руки своя.
10 Amma zan washe Isuwa sarai; zan bubbuɗe wuraren ɓuyarsa, don kada yă ɓoye kansa.’Ya’yansa, danginsa da maƙwabtansa za su hallaka, ba kuwa zai ƙara kasancewa ba.
Яко (Аз) обнажих Исава, открых тайная его, не возможет утаитися, погибе рукою брата своего и соседа своего,
11 Ka bar marayunka; zan tsare ransu. Gwaurayenka kuma za su dogara a gare ni.”
и несть остатися сироте твоей, да живет: Аз же сотворю жити, и вдовицы на Мя уповаша.
12 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “In waɗanda ba su dace su sha kwaf ɗin ba suka sha shi, me ya sa za ka kuɓuta? Ba za ka kuɓuta ba, sai ka sha shi.
Тако бо глаголет Господь: се, имже не бе закона пити чашу, пиюще испиют: и ты ли аки неповинный останешися? Не будеши неповинен, но пия испиеши.
13 Na rantse da kaina,” in ji Ubangiji, “cewa Bozra za tă zama kufai da kuma abin tsoro, abin dariya da abin la’ana; kuma dukan garuruwanta za su kasance kufai har abada.”
Собою бо кляхся, глаголет Господь, яко в пустыню и в поругание и в посмех и в проклятие будеши посреде его, и вси гради его будут в пустыню вечную.
14 Na ji saƙo daga Ubangiji cewa; an aiki jakada zuwa ga al’ummai ya ce, “Ku tattara kanku don ku fāɗa mata! Ku tashi don yaƙi!”
Слух слышах от Господа, и послов во языки посла: соберитеся и идите противу ему и востаните на ополчение.
15 “Yanzu zan mai da kai ƙanƙani a cikin al’ummai abin reni a cikin mutane.
Се, мала дах тя во языцех и поругаема в людех.
16 Tsoron da ka sa ake ji da kuma girman kan zuciyarka ya ruɗe ka, kai da kake zama a kogon dutse, kai da kake kan tudu. Ko da yake ka gina wa kanka sheƙa can bisa kamar na gaggafa, daga can zan sauko da kai ƙasa,” in ji Ubangiji.
Играние твое прельсти тя, безстудие сердца твоего обиташе в разселинах каменных, похити крепость холма высокаго: егда вознесеши яко орел гнездо свое, оттоле свергу тя, глаголет Господь.
17 “Edom za tă zama abin tsoro; dukan wanda ya wuce zai giggice ya yi tsaki saboda dukan mikinta.
И будет Идумеа в запустение, всяк ходяй чрез ню подивится и позвиждет над всякою язвою ея.
18 Kamar yadda aka tumɓuke Sodom da Gomorra, tare da garuruwan da suke maƙwabtaka da su,” in ji Ubangiji, “haka ba wanda zai zauna a can; ba wani da zai zauna a cikinta.
Якоже превращена есть Содома и Гоморра и соседи ея, глаголет Господь, не поживет тамо муж, ниже пребудет тамо сын человечь.
19 “Kamar zaki mai haurawa daga kurmin Urdun zuwa wurin kiwo mai kyau, zan kori Edom daga ƙasarta nan da nan. Wane ne zaɓaɓɓen da zan naɗa don wannan? Wane ne yake kama da ni kuma wa zai kalubalance ni? Kuma wane makiyayi ne zai yi gāba da ni?”
Се, якоже лев изыдет от среды Иордана на место сильнаго, яко скоро сотворю им бежати от него, и кто будет избран, егоже поставлю над ним? Кто бо подобен Мне? И кто противостанет Ми? И кто есть сей пастырь, иже сопротивится лицу Моему?
20 Saboda haka, ku ji abin da Ubangiji ya shirya a kan Edom, abin da ya nufa wa waɗanda suke zama a Teman. Za a ja ƙanana na garken tumaki a tafi; zai hallaka wurin kiwonsu sarai saboda su.
Сего ради слышите совет Господень, егоже совеща на Едома, и умышление Его, еже умысли на живущих во Фемане, не свергут ли их малая от стад, и не разметано ли будет на них жилище их?
21 Amon fāɗuwarsu zai sa ƙasa ta girgiza; za a kuma ji muryar kukansu a Jan Teku.
От гласа бо падения их потрясеся земля, и вопль на мори Чермнем слышася гласа их.
22 Duba! Gaggafa tana firiya tana kuma saukowa, tana buɗe fikafikanta a bisa Bozra. A wannan rana zukatan jarumawan Edom za su zama kamar macen da take naƙuda.
Се, яко орел взыдет и возлетит и прострет криле свои над твердыньми его: и будет сердце сильных Идумейских в той день, яко сердце жены родящия.
23 Game da Damaskus. “Hamat da Arfad sun giggice, gama sun ji mummunar labari. Suna damuwa, sun damu kamar tekun da baya hutu.
К Дамаску: посрамися Емаф и Арфаф, яко слух зол слышаша, ужасошася, возмутишася на мори, (за попечение) упокоитися не могут.
24 Damaskus ta karai ta juya don ta gudu tsoro kuma ya kama ta; wahala da zafi sun kama ta, zafi kamar na mace mai naƙuda.
Расторжеся Дамаск, обратися на бежание, трепет объят и, скорбь и болезнь одержаша его яко раждающую.
25 Me ya sa ba a tafi aka bar sanannen birnin nan ba, birnin da nake jin daɗi?
Како не оставиша града славнаго, крепости любезныя?
26 Tabbatacce, samarinta za su fāɗi a tituna; dukan sojojinta za su yi shiru a wannan rana,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Сего ради падут юноши на стогнах твоих, и вси мужие воинстии падут в той день, глаголет Господь Вседержитель.
27 “Zan cinna wa katangar Damaskus wuta; za tă ci kagaran Ben-Hadad.”
И возжгу огнь на стене Дамаска, и пожжет стены сына Адерова.
28 Game da Kedar da mulkokin Hazor, waɗanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya fāɗa wa. Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Tashi, ku fāɗa wa Kedar ku kuma hallaka mutanen Gabas.
К Кидару, царице двора, егоже порази Навуходоносор царь Вавилонский, тако глаголет Господь: востаните и взыдите на Кидар и погубите сыны восточныя.
29 Za a ƙwace tentunansu da garkunansu; za a tafi da mafakanta tare da dukan kayayyakinsu da raƙumansu. Mutane za su yi musu ihu, ‘Razana ko’ina!’
Селения их и стада их возмут: одежды их и вся сосуды их и велблюды их возмут себе, и призовут на ня страх окрест.
30 “Ku yi maza ku gudu! Ku zauna a kogo masu zurfi, ku da kuke zama a Hazor,” in ji Ubangiji. “Nebukadnezzar sarkin Babilon ya shirya muku maƙarƙashiya; ya ƙulla maƙarƙashiya a kanku.
Бежите и отидите вскоре, в пропастех сядите, живущии во дворе, глаголет Господь: яко совеща на вы Навуходоносор царь Вавилонский совет и помысли на вас умышление.
31 “Ku tashi ku kuma fāɗa wa al’umma da sauƙi wadda take zama da ƙarfin hali,” in ji Ubangiji, “al’ummar da ba ta da ƙofofi ko ƙyamare; mutanenta suna zama su kaɗai.
Востаните и внидите к людем упокоеным, живущым в прохладе, глаголет Господь: иже ни дверий, ниже заворов имут, едини обитают.
32 Za a washe raƙumansu, garkunansu mai girma za su zama ganima. Zan watsar da waɗanda suke a wurare masu nesa a ko’ina zan kuma kawo musu masifa a kowane gefe,” in ji Ubangiji.
И будут велблюды их в расхищение и множество скота их в разграбление, и развею я всяким ветром остриженых окрест, и от всех окрестных их приведу на ня погибель, глаголет Господь.
33 “Hazor za tă zama mazaunin diloli, kufai har abada. Ba wanda zai zauna a can; ba wanda zai zauna a cikinta.”
И будет двор в жилище змием и пуст даже до века, не поживет тамо муж, ниже будет живяй в нем сын человечь.
34 Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da Elam, a farkon mulkin Zedekiya sarkin Yahuda.
Слово Господне, еже бысть ко Иеремии пророку на Елам, в начале царства Седекии царя Иудина, глаголя:
35 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ga shi, zan karye ƙarfin Elam, zaunannen ƙarfinsu.
тако глаголет Господь Вседержитель: се, Аз сокрушу лук Еламль, начало силы их,
36 Zan kawo a kan Elam a kusurwoyi huɗu daga kusurwoyi huɗu na duniya; zan watsar da su zuwa kusurwoyi huɗu, kuma ba al’ummar da masu gudun hijirar Elam ba za su kai ba.
и наведу на Елам четыри ветры от четырех стран небесных и развею я во вся ветры тыя, и не будет языка, в оньже бы не пришли бежащии Еламитяне.
37 Zan ragargaza Elam a gaban maƙiyansu, a gaban waɗanda suke neman ransu; zan kawo masifa a kansu, da zafin fushina,” in ji Ubangiji. “Zan runtume su da takobi sai na kawo ƙarshensu.
И устрашу их пред враги их и пред лицем ищущих души их, и наведу на ня злая, по гневу ярости Моея, глаголет Господь: и послю вслед их мечь Мой, дондеже сотру их:
38 Zan sa kursiyina a Elam in kuma hallaka sarkinta da fadawanta,” in ji Ubangiji.
и поставлю престол Мой во Еламе, и иждену оттуду царя и князи, глаголет Господь:
39 “Duk da haka zan maido da wadatar Elam a kwanaki masu zuwa,” in ji Ubangiji.
и будет в последния дни, возвращу плен Еламль, глаголет Господь.