< Irmiya 49 >
1 Game da Ammonawa. Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Isra’ila ba shi da’ya’ya maza ne? Ba shi da magāda ne? To, me ya sa Molek ya mallaki Gad? Me ya sa mutanensa suka zama a garuruwansa?
Quant aux enfants de Hammon, ainsi a dit l'Eternel: Israël n'a-t-il point d'enfants, ou n'a-t-il point d'héritier? pourquoi donc Malcam a-t-il hérité [du pays] de Gad, et pourquoi son peuple demeure-t-il dans les villes [de Gad]?
2 Amma kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan yi kirarin yaƙi a kan Rabba ta Ammonawa; zai zama tarin juji, za a sa wuta a ƙauyukan da suke kewayenta. Sa’an nan Isra’ila zai kori waɗanda suka kore shi,” in ji Ubangiji.
C'est pourquoi voici, les jours viennent, dit l'Eternel, que je ferai ouïr l'alarme dans Rabba des enfants de Hammon, et elle sera réduite en un monceau de ruines, et les villes de son ressort seront brûlées au feu, et Israël possédera ceux qui l'auront possédé, a dit l'Eternel.
3 “Ki yi kuka, ya Heshbon, gama an hallaka Ai! Ku tā da murya ku yi kuka, ya mazaunan Rabba! Ku sa tufafin makoki; ku ruga nan da can a cikin katanga, gama Molek zai tafi bauta, tare da firistocinsa da kuma fadawansa.
Hurle, ô Hesbon! car Haï a été ravagée. Villes du ressort de Rabba, criez; ceignez le sac sur vous, lamentez, courez le long des haies; car Malcam ira en captivité avec ses Sacrificateurs et ses principaux.
4 Me ya sa kuke taƙama da kwarurukanku, taƙama da kwarurukanku masu amfani? Ya ke diya marar aminci, kin dogara a wadatarki kika kuma ce, ‘Wa zai iya fāɗa mini?’
Pourquoi te glorifies-tu de tes vallées? ta vallée est écoulée, fille revêche. Elle se confiait en ses trésors, et [disait]: qui viendra contre moi?
5 Zan kawo razana a kanki daga waɗanda suke kewaye da ke,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Za a kore kowannenku, babu wani da zai tattara masu gudun hijira.
Voici, je m'en vais faire venir de tous tes environs la frayeur sur toi, dit le Seigneur l'Eternel des armées, et vous serez chassés chacun çà et là, et il n'y aura personne qui rassemble les dispersés.
6 “Duk da haka, daga baya, zan maido da wadatar Ammonawa,” in ji Ubangiji.
Mais après cela je ferai retourner les captifs des enfants de Hammon, dit l'Etemel.
7 Game da Edom. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Babu sauran hikima a Teman ne? Shawara ta ɓace daga masu basira ne? Hikimarsu ta ruɓe ne?
Quant à Edom, ainsi a dit l'Eternel des armées: n'est-il pas vrai qu'[il] n'[y a] plus de sagesse dans Téman? le conseil a manqué à ses habitants, leur sagesse s'est évanouie.
8 Ku juya ku gudu, ku ɓuya a cikin kogwanni masu zurfi, ku da kuke zama a Dedan, gama zan kawo masifa a kan Isuwa a lokacin da zan hukunta shi.
Fuyez, tournez [le dos], vous habitants de Dédan, qui avez fait des creux pour y habiter; car j'ai fait venir sur Esaü sa calamité, le temps auquel je l'ai visité.
9 In masu tsinkar’ya’yan inabi suka zo maka, ba za su rage’ya’yan inabi kaɗan ba? In ɓarayi suka zo da dare, ba za su sata abin da kawai suke bukata ba?
Est-il entré chez toi des vendangeurs? ils ne t'auraient point laissé de grappillage. Sont-ce des larrons de nuit? ils auraient fait du dégât autant qu'il leur aurait suffi.
10 Amma zan washe Isuwa sarai; zan bubbuɗe wuraren ɓuyarsa, don kada yă ɓoye kansa.’Ya’yansa, danginsa da maƙwabtansa za su hallaka, ba kuwa zai ƙara kasancewa ba.
Mais j'ai fouillé Esaü, j'ai découvert ses lieux secrets, tellement qu'il ne se pourra cacher; sa postérité est ravagée, ses frères aussi, et ses voisins; et ce n'est plus rien.
11 Ka bar marayunka; zan tsare ransu. Gwaurayenka kuma za su dogara a gare ni.”
Laisse tes orphelins, et je leur donnerai de quoi vivre, et que tes veuves s'assurent sur moi.
12 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “In waɗanda ba su dace su sha kwaf ɗin ba suka sha shi, me ya sa za ka kuɓuta? Ba za ka kuɓuta ba, sai ka sha shi.
Car ainsi a dit l'Eternel: voici, ceux qui ne devaient point boire de la coupe, en boiront certainement; et toi en serais-tu exempt en quelque manière? tu n'en seras point exempt; mais tu en boiras certainement.
13 Na rantse da kaina,” in ji Ubangiji, “cewa Bozra za tă zama kufai da kuma abin tsoro, abin dariya da abin la’ana; kuma dukan garuruwanta za su kasance kufai har abada.”
Car j'ai juré par moi-même, dit l'Eternel, que Botsra sera réduite en désolation, en opprobre, en désert, et en malédiction, et que toutes ses villes seront réduites en déserts perpétuels.
14 Na ji saƙo daga Ubangiji cewa; an aiki jakada zuwa ga al’ummai ya ce, “Ku tattara kanku don ku fāɗa mata! Ku tashi don yaƙi!”
J'ai ouï une publication de par l'Eternel, et il y a un ambassadeur envoyé parmi les nations, [pour leur dire]: assemblez-vous, et venez contre elle, et levez-vous pour combattre.
15 “Yanzu zan mai da kai ƙanƙani a cikin al’ummai abin reni a cikin mutane.
Car voici, je t'avais fait petit entre les nations, et contemptible entre les hommes.
16 Tsoron da ka sa ake ji da kuma girman kan zuciyarka ya ruɗe ka, kai da kake zama a kogon dutse, kai da kake kan tudu. Ko da yake ka gina wa kanka sheƙa can bisa kamar na gaggafa, daga can zan sauko da kai ƙasa,” in ji Ubangiji.
Mais ta présomption, [et] la fierté de ton cœur t'ont séduit, toi qui habites dans les creux des rochers, et qui occupes la hauteur des coteaux. Quand tu aurais élevé ton nid comme l'aigle, je t'en ferai descendre, dit l'Eternel.
17 “Edom za tă zama abin tsoro; dukan wanda ya wuce zai giggice ya yi tsaki saboda dukan mikinta.
Et l'Idumée sera réduite en désolation, tellement que quiconque passera près d'elle en sera étonné, et lui insultera à cause de toutes ses plaies.
18 Kamar yadda aka tumɓuke Sodom da Gomorra, tare da garuruwan da suke maƙwabtaka da su,” in ji Ubangiji, “haka ba wanda zai zauna a can; ba wani da zai zauna a cikinta.
Il n'y demeurera personne, a dit l'Eternel, et aucun fils d'homme n'y séjournera, comme dans la subversion de Sodome et de Gomorrhe, et de leurs lieux circonvoisins.
19 “Kamar zaki mai haurawa daga kurmin Urdun zuwa wurin kiwo mai kyau, zan kori Edom daga ƙasarta nan da nan. Wane ne zaɓaɓɓen da zan naɗa don wannan? Wane ne yake kama da ni kuma wa zai kalubalance ni? Kuma wane makiyayi ne zai yi gāba da ni?”
Voici, il montera comme un lion à cause de l'enflure du Jourdain, vers la demeure du pays rude, et après l'avoir fait reposer je le ferai courir hors de l'Idumée. Et qui [est] d'élite, que je lui donne commission contre elle? car qui est semblable à moi? et qui me déterminera le temps? et qui sera le Pasteur qui tiendra ferme contre moi?
20 Saboda haka, ku ji abin da Ubangiji ya shirya a kan Edom, abin da ya nufa wa waɗanda suke zama a Teman. Za a ja ƙanana na garken tumaki a tafi; zai hallaka wurin kiwonsu sarai saboda su.
C'est pourquoi écoutez la résolution que l'Eternel a prise contre Edom, et les desseins qu'il a formés contre les habitants de Téman; si les plus petits du troupeau ne les traînent par terre, et si l'on ne réduit en désolation leurs cabanes sur eux.
21 Amon fāɗuwarsu zai sa ƙasa ta girgiza; za a kuma ji muryar kukansu a Jan Teku.
La terre a été ébranlée du bruit de leur ruine; il y a eu un cri, le son en a été ouï en la mer Rouge.
22 Duba! Gaggafa tana firiya tana kuma saukowa, tana buɗe fikafikanta a bisa Bozra. A wannan rana zukatan jarumawan Edom za su zama kamar macen da take naƙuda.
Voici, il montera comme un aigle, et il volera, et étendra ses ailes sur Botsra; et le cœur des forts d'Edom en ce jour-là sera comme le cœur d'une femme qui est en travail.
23 Game da Damaskus. “Hamat da Arfad sun giggice, gama sun ji mummunar labari. Suna damuwa, sun damu kamar tekun da baya hutu.
Quant à Damas; Hamath et Arpad ont été rendues honteuses, parce qu'elles ont appris des nouvelles très mauvaises, ils sont fondus, il y a une tourmente en la mer, elle ne se peut apaiser.
24 Damaskus ta karai ta juya don ta gudu tsoro kuma ya kama ta; wahala da zafi sun kama ta, zafi kamar na mace mai naƙuda.
Damas est toute lâche, elle est mise en fuite, la peur l'a surprise, l'angoisse et les douleurs l'ont saisie comme d'une femme qui enfante.
25 Me ya sa ba a tafi aka bar sanannen birnin nan ba, birnin da nake jin daɗi?
Comment n'a été réservée la ville renommée, ma ville de plaisance?
26 Tabbatacce, samarinta za su fāɗi a tituna; dukan sojojinta za su yi shiru a wannan rana,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Car ses gens d'élite tomberont dans ses rues, et on fera perdre la parole à tous ses hommes de guerre en ce jour-là, dit l'Eternel des armées.
27 “Zan cinna wa katangar Damaskus wuta; za tă ci kagaran Ben-Hadad.”
Et je mettrai le feu à la muraille de Damas, qui dévorera les palais de Ben-hadad.
28 Game da Kedar da mulkokin Hazor, waɗanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya fāɗa wa. Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Tashi, ku fāɗa wa Kedar ku kuma hallaka mutanen Gabas.
Quant à Kédar, et aux Royaumes de Hatsor, lesquels Nébucanetsar Roi de Babylone frappera, ainsi a dit l'Eternel: levez-vous, montez vers Kédar, et détruisez les enfants d'Orient.
29 Za a ƙwace tentunansu da garkunansu; za a tafi da mafakanta tare da dukan kayayyakinsu da raƙumansu. Mutane za su yi musu ihu, ‘Razana ko’ina!’
Ils enlèveront leurs tentes et leurs troupeaux, et prendront pour eux leurs tentes, et tout leur équipage, et leurs chameaux, et on criera: frayeur tout autour.
30 “Ku yi maza ku gudu! Ku zauna a kogo masu zurfi, ku da kuke zama a Hazor,” in ji Ubangiji. “Nebukadnezzar sarkin Babilon ya shirya muku maƙarƙashiya; ya ƙulla maƙarƙashiya a kanku.
Fuyez, écartez-vous tant que vous pourrez, vous habitants de Hatsor, qui avez fait des creux pour y habiter, dit l'Eternel; car Nébucadnetsar Roi de Babylone a formé un dessein contre vous, il a pris une résolution contre vous.
31 “Ku tashi ku kuma fāɗa wa al’umma da sauƙi wadda take zama da ƙarfin hali,” in ji Ubangiji, “al’ummar da ba ta da ƙofofi ko ƙyamare; mutanenta suna zama su kaɗai.
Levez-vous, montez vers la nation qui est en repos, qui habite en assurance, dit l'Eternel; qui n'ont ni portes, ni barres, et qui habitent seuls.
32 Za a washe raƙumansu, garkunansu mai girma za su zama ganima. Zan watsar da waɗanda suke a wurare masu nesa a ko’ina zan kuma kawo musu masifa a kowane gefe,” in ji Ubangiji.
Et leurs chameaux seront au pillage, et la multitude de leur bétail sera en proie; et je les disperserai à tout vent, vers ceux qui se coupent l'extrémité des cheveux, et je ferai venir de tous les côtés leur calamité, dit l'Eternel.
33 “Hazor za tă zama mazaunin diloli, kufai har abada. Ba wanda zai zauna a can; ba wanda zai zauna a cikinta.”
Et Hatsor deviendra un repaire de dragons, et un désert à toujours; il n'y demeurera personne, et aucun fils d'homme n'y séjournera.
34 Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da Elam, a farkon mulkin Zedekiya sarkin Yahuda.
La parole de l'Eternel qui fut [adressée] à Jérémie le Prophète, contre Hélam, au commencement du règne de Sédécias Roi de Juda, en disant:
35 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ga shi, zan karye ƙarfin Elam, zaunannen ƙarfinsu.
Ainsi a dit l'Eternel des armées: voici, je m'en vais rompre l'arc d'Hélam, qui est leur principale force.
36 Zan kawo a kan Elam a kusurwoyi huɗu daga kusurwoyi huɗu na duniya; zan watsar da su zuwa kusurwoyi huɗu, kuma ba al’ummar da masu gudun hijirar Elam ba za su kai ba.
Et je ferai venir contre Hélam les quatre vents, des quatre bouts des cieux; et je les disperserai par tous ces vents-là; et il n'y aura point de nation chez laquelle ne viennent ceux qui seront chassés d'Hélam.
37 Zan ragargaza Elam a gaban maƙiyansu, a gaban waɗanda suke neman ransu; zan kawo masifa a kansu, da zafin fushina,” in ji Ubangiji. “Zan runtume su da takobi sai na kawo ƙarshensu.
Et je ferai que ceux d'Hélam seront épouvantés devant leurs ennemis, et devant ceux qui cherchent leur vie; et je ferai venir du mal sur eux, l'ardeur de ma colère, dit l'Eternel; et j'enverrai l'épée après eux, jusqu’à ce que je les aie consumés.
38 Zan sa kursiyina a Elam in kuma hallaka sarkinta da fadawanta,” in ji Ubangiji.
Et je mettrai mon trône en Hélam, et j'en détruirai les Rois et les principaux, dit l'Eternel.
39 “Duk da haka zan maido da wadatar Elam a kwanaki masu zuwa,” in ji Ubangiji.
Mais il arrivera qu'aux derniers jours je ferai retourner d'Hélam les captifs, dit l'Eternel.