< Irmiya 49 >
1 Game da Ammonawa. Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Isra’ila ba shi da’ya’ya maza ne? Ba shi da magāda ne? To, me ya sa Molek ya mallaki Gad? Me ya sa mutanensa suka zama a garuruwansa?
Of [the] people of Ammon thus he says Yahweh ¿ [do] children not [belong] to Israel or? [does] an heir not [belongs] to it why? has he dispossessed Milcom Gad and people his in cities its has it dwelt?
2 Amma kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan yi kirarin yaƙi a kan Rabba ta Ammonawa; zai zama tarin juji, za a sa wuta a ƙauyukan da suke kewayenta. Sa’an nan Isra’ila zai kori waɗanda suka kore shi,” in ji Ubangiji.
Therefore here! days [are] coming [the] utterance of Yahweh and I will sound aloud against Rabbah of [the] people of Ammon a shout of battle and it will become a mound of desolation and daughters its with fire they will be kindled and it will dispossess Israel [those who] dispossessed it he says Yahweh.
3 “Ki yi kuka, ya Heshbon, gama an hallaka Ai! Ku tā da murya ku yi kuka, ya mazaunan Rabba! Ku sa tufafin makoki; ku ruga nan da can a cikin katanga, gama Molek zai tafi bauta, tare da firistocinsa da kuma fadawansa.
Wail O Heshbon for it has been devastated Ai cry out O daughters of Rabbah gird yourselves sackcloth mourn and run to and fro among the walls for Milcom in exile he will go priests his and officials his together.
4 Me ya sa kuke taƙama da kwarurukanku, taƙama da kwarurukanku masu amfani? Ya ke diya marar aminci, kin dogara a wadatarki kika kuma ce, ‘Wa zai iya fāɗa mini?’
Why? do you boast in the valleys [is] flowing valley your O daughter apostate who trusts in treasures her who? will he come against me.
5 Zan kawo razana a kanki daga waɗanda suke kewaye da ke,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Za a kore kowannenku, babu wani da zai tattara masu gudun hijira.
Here I [am] about to bring on you terror [the] utterance of [the] Lord Yahweh of hosts from all around you and you will be driven away everyone before it and not [one who] gathers together [belongs] to the fugitive.
6 “Duk da haka, daga baya, zan maido da wadatar Ammonawa,” in ji Ubangiji.
And after thus I will turn back [the] captivity of [the] people of Ammon [the] utterance of Yahweh.
7 Game da Edom. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Babu sauran hikima a Teman ne? Shawara ta ɓace daga masu basira ne? Hikimarsu ta ruɓe ne?
Of Edom thus he says Yahweh of hosts ¿ [is] there not still wisdom in Teman has it been lost? counsel from understanding [people] has it been corrupted? wisdom their.
8 Ku juya ku gudu, ku ɓuya a cikin kogwanni masu zurfi, ku da kuke zama a Dedan, gama zan kawo masifa a kan Isuwa a lokacin da zan hukunta shi.
Flee be turned back make deep to dwell O inhabitants of Dedan for [the] disaster of Esau I will bring on it a time [when] I will visit it.
9 In masu tsinkar’ya’yan inabi suka zo maka, ba za su rage’ya’yan inabi kaɗan ba? In ɓarayi suka zo da dare, ba za su sata abin da kawai suke bukata ba?
If grape gatherers they came to you not will they leave? gleanings if thieves in the night they destroyed sufficiency their.
10 Amma zan washe Isuwa sarai; zan bubbuɗe wuraren ɓuyarsa, don kada yă ɓoye kansa.’Ya’yansa, danginsa da maƙwabtansa za su hallaka, ba kuwa zai ƙara kasancewa ba.
For I I will strip bare Esau I will uncover hiding places its and it will hide itself not it will be able it will be devastated offspring its and relatives its and neighbors its and there not [will be] it.
11 Ka bar marayunka; zan tsare ransu. Gwaurayenka kuma za su dogara a gare ni.”
Leave! fatherless your I I will preserve [them] alive and widows your on me let them rely.
12 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “In waɗanda ba su dace su sha kwaf ɗin ba suka sha shi, me ya sa za ka kuɓuta? Ba za ka kuɓuta ba, sai ka sha shi.
For thus - he says Yahweh there! [those] who not sentence their [was] to drink the cup completely they will drink [it] and you he completely will you be exempt from punishment? not you will be exempt from punishment for certainly you will drink [it].
13 Na rantse da kaina,” in ji Ubangiji, “cewa Bozra za tă zama kufai da kuma abin tsoro, abin dariya da abin la’ana; kuma dukan garuruwanta za su kasance kufai har abada.”
For by myself I swear [the] utterance of Yahweh that a waste a reproach a desolation and a curse it will become Bozrah and all cities its they will become ruins of perpetuity.
14 Na ji saƙo daga Ubangiji cewa; an aiki jakada zuwa ga al’ummai ya ce, “Ku tattara kanku don ku fāɗa mata! Ku tashi don yaƙi!”
A report I have heard from with Yahweh and an envoy among the nations [has been] sent gather together and come on it and rise up for battle.
15 “Yanzu zan mai da kai ƙanƙani a cikin al’ummai abin reni a cikin mutane.
For here! small I will make you among the nations despised among humankind.
16 Tsoron da ka sa ake ji da kuma girman kan zuciyarka ya ruɗe ka, kai da kake zama a kogon dutse, kai da kake kan tudu. Ko da yake ka gina wa kanka sheƙa can bisa kamar na gaggafa, daga can zan sauko da kai ƙasa,” in ji Ubangiji.
Horror your it has deceived you [the] arrogance of heart your O dweller in [the] clefts of the rock O occupant of [the] height[s] of a hill for you will make high like eagle nest your from there I will bring down you [the] utterance of Yahweh.
17 “Edom za tă zama abin tsoro; dukan wanda ya wuce zai giggice ya yi tsaki saboda dukan mikinta.
And it will become Edom a horror every [one who] passes by at it he will be appalled and he may hiss on all wounds its.
18 Kamar yadda aka tumɓuke Sodom da Gomorra, tare da garuruwan da suke maƙwabtaka da su,” in ji Ubangiji, “haka ba wanda zai zauna a can; ba wani da zai zauna a cikinta.
Like [the] overthrow of Sodom and Gomorrah and neighbors its he says Yahweh not he will dwell there anyone and not he will sojourn in it a child of humankind.
19 “Kamar zaki mai haurawa daga kurmin Urdun zuwa wurin kiwo mai kyau, zan kori Edom daga ƙasarta nan da nan. Wane ne zaɓaɓɓen da zan naɗa don wannan? Wane ne yake kama da ni kuma wa zai kalubalance ni? Kuma wane makiyayi ne zai yi gāba da ni?”
There! like a lion [which] it goes up from [the] thicket[s] of the Jordan to pastureland of an ever-flowing [stream] for I will act in a moment I will cause to run it from on it and whoever [is] chosen to it I will appoint for who? [is] like me and who? will he summon me and who? this [is] a shepherd who he will stand before me.
20 Saboda haka, ku ji abin da Ubangiji ya shirya a kan Edom, abin da ya nufa wa waɗanda suke zama a Teman. Za a ja ƙanana na garken tumaki a tafi; zai hallaka wurin kiwonsu sarai saboda su.
Therefore hear [the] plan of Yahweh which he has planned against Edom and purposes his which he has purposed against [the] inhabitants of Teman if not people will drag away them [the] young [ones] of the flock if not he will devastate on them pastureland their.
21 Amon fāɗuwarsu zai sa ƙasa ta girgiza; za a kuma ji muryar kukansu a Jan Teku.
From [the] sound of falling they it will shake the earth of [the] calling out at [the] sea of reed[s] it will be heard sound its.
22 Duba! Gaggafa tana firiya tana kuma saukowa, tana buɗe fikafikanta a bisa Bozra. A wannan rana zukatan jarumawan Edom za su zama kamar macen da take naƙuda.
There! like eagle someone will ascend and he may swoop down so he may spread out wings his over Bozrah and it will be [the] heart of [the] warriors of Edom on the day that like [the] heart of a woman in labor.
23 Game da Damaskus. “Hamat da Arfad sun giggice, gama sun ji mummunar labari. Suna damuwa, sun damu kamar tekun da baya hutu.
Of Damascus it will be ashamed Hamath and Arpad for new[s] bad they have heard they will melt away [is] in the sea anxiety to be quiet not it will be able.
24 Damaskus ta karai ta juya don ta gudu tsoro kuma ya kama ta; wahala da zafi sun kama ta, zafi kamar na mace mai naƙuda.
It will be disheartened Damascus it will turn back to flee and panic - it will take hold distress and pains it will seize it like [woman] giving birth.
25 Me ya sa ba a tafi aka bar sanannen birnin nan ba, birnin da nake jin daɗi?
How! not it has been forsaken a city of (praise *Q(K)*) [the] town of joy my.
26 Tabbatacce, samarinta za su fāɗi a tituna; dukan sojojinta za su yi shiru a wannan rana,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Therefore they will fall young men its in open places its and all [the] men of war they will be silenced in the day that [the] utterance of Yahweh of hosts.
27 “Zan cinna wa katangar Damaskus wuta; za tă ci kagaran Ben-Hadad.”
And I will kindle a fire at [the] wall of Damascus and it will consume [the] fortresses of Ben Hadad.
28 Game da Kedar da mulkokin Hazor, waɗanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya fāɗa wa. Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Tashi, ku fāɗa wa Kedar ku kuma hallaka mutanen Gabas.
Of Kedar - and of [the] kingdoms of Hazor which he attacked (Nebuchadnezzar *Q(K)*) [the] king of Babylon thus he says Yahweh arise go up against Kedar and devastate [the] people of [the] east.
29 Za a ƙwace tentunansu da garkunansu; za a tafi da mafakanta tare da dukan kayayyakinsu da raƙumansu. Mutane za su yi musu ihu, ‘Razana ko’ina!’
Tents their and flock[s] their people will take away tent curtains their and all equipment their and camels their they will carry off for themselves and people will call out to them terror [is] from round about.
30 “Ku yi maza ku gudu! Ku zauna a kogo masu zurfi, ku da kuke zama a Hazor,” in ji Ubangiji. “Nebukadnezzar sarkin Babilon ya shirya muku maƙarƙashiya; ya ƙulla maƙarƙashiya a kanku.
Flee take flight exceedingly make deep to dwell O inhabitants of Hazor [the] utterance of Yahweh that he has planned on you Nebuchadnezzar [the] king of Babylon a plan and he has purposed (on you *Q(K)*) a purpose.
31 “Ku tashi ku kuma fāɗa wa al’umma da sauƙi wadda take zama da ƙarfin hali,” in ji Ubangiji, “al’ummar da ba ta da ƙofofi ko ƙyamare; mutanenta suna zama su kaɗai.
Arise go up against a nation at ease [which] dwells to security [the] utterance of Yahweh not a pair of gates and not a bar [belong] to it alone they dwell.
32 Za a washe raƙumansu, garkunansu mai girma za su zama ganima. Zan watsar da waɗanda suke a wurare masu nesa a ko’ina zan kuma kawo musu masifa a kowane gefe,” in ji Ubangiji.
And they will become camels their spoil and [the] abundance of livestock their plunder and I will scatter them to every wind [those who] are cut off of [the] corner and from all sides its I will bring disaster their [the] utterance of Yahweh.
33 “Hazor za tă zama mazaunin diloli, kufai har abada. Ba wanda zai zauna a can; ba wanda zai zauna a cikinta.”
And it will become Hazor a habitation of jackals a desolation until perpetuity not he will dwell there anyone and not he will sojourn in it a child of humankind.
34 Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da Elam, a farkon mulkin Zedekiya sarkin Yahuda.
Which it came [the] word of Yahweh to Jeremiah the prophet concerning Elam at [the] beginning of [the] reign of Zedekiah [the] king of Judah saying.
35 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ga shi, zan karye ƙarfin Elam, zaunannen ƙarfinsu.
Thus he says Yahweh of hosts here I [am] about to break [the] bow of Elam [the] beginning of strength their.
36 Zan kawo a kan Elam a kusurwoyi huɗu daga kusurwoyi huɗu na duniya; zan watsar da su zuwa kusurwoyi huɗu, kuma ba al’ummar da masu gudun hijirar Elam ba za su kai ba.
And I will bring against Elam four winds from [the] four [the] ends of the heavens and I will scatter them to all the winds these and not it will be the nation where not it will go there [the] outcasts of (Elam. *Q(K)*)
37 Zan ragargaza Elam a gaban maƙiyansu, a gaban waɗanda suke neman ransu; zan kawo masifa a kansu, da zafin fushina,” in ji Ubangiji. “Zan runtume su da takobi sai na kawo ƙarshensu.
And I will shatter Elam (before *LAB(h)*) enemies their and before - [those who] seek life their and I will bring on them - calamity [the] burning of anger my [the] utterance of Yahweh and I will send after them the sword until have made an end of I them.
38 Zan sa kursiyina a Elam in kuma hallaka sarkinta da fadawanta,” in ji Ubangiji.
And I will set throne my in Elam and I will destroy from there king and officials [the] utterance of Yahweh.
39 “Duk da haka zan maido da wadatar Elam a kwanaki masu zuwa,” in ji Ubangiji.
And it will be - at [the] end of the days (I will turn back *Q(K)*) ([the] captivity of *Q(k)*) Elam [the] utterance of Yahweh.