< Irmiya 49 >
1 Game da Ammonawa. Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Isra’ila ba shi da’ya’ya maza ne? Ba shi da magāda ne? To, me ya sa Molek ya mallaki Gad? Me ya sa mutanensa suka zama a garuruwansa?
Concerning the children of Ammon. Thus saith Jehovah: Hath Israel no sons? Hath he not an heir? Why then doth Milcom inherit Gad, And his people dwell in his cities?
2 Amma kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan yi kirarin yaƙi a kan Rabba ta Ammonawa; zai zama tarin juji, za a sa wuta a ƙauyukan da suke kewayenta. Sa’an nan Isra’ila zai kori waɗanda suka kore shi,” in ji Ubangiji.
Therefore, behold, the days come, saith Jehovah, That I will cause a cry of war to be heard against Rabbah of the sons of Ammon, And she shall become a ruinous heap, And her daughters shall be burned with fire; And Israel shall take possession of their land, who took possession of his.
3 “Ki yi kuka, ya Heshbon, gama an hallaka Ai! Ku tā da murya ku yi kuka, ya mazaunan Rabba! Ku sa tufafin makoki; ku ruga nan da can a cikin katanga, gama Molek zai tafi bauta, tare da firistocinsa da kuma fadawansa.
Howl, O Heshbon, for Ai is laid waste! Cry, ye daughters of Rabbah, Gird yourselves with sackcloth, lament, And run ye to and fro within the fences! For Milcom goeth into captivity, His priests and his princes together.
4 Me ya sa kuke taƙama da kwarurukanku, taƙama da kwarurukanku masu amfani? Ya ke diya marar aminci, kin dogara a wadatarki kika kuma ce, ‘Wa zai iya fāɗa mini?’
Wherefore dost thou glory in the valleys? Thy valley shall flow [[with blood]], O perverse daughter, That gloriest in thy treasures, [[Saying, ]] “Who shall come against me?”
5 Zan kawo razana a kanki daga waɗanda suke kewaye da ke,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Za a kore kowannenku, babu wani da zai tattara masu gudun hijira.
Behold, I will bring a terror upon thee, saith Jehovah of hosts, From all those that are around thee, And ye shall be driven out, every one right forth, And there shall be none to gather up the fugitives.
6 “Duk da haka, daga baya, zan maido da wadatar Ammonawa,” in ji Ubangiji.
But after this will I bring back the captivity of the sons of Ammon, saith Jehovah.
7 Game da Edom. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Babu sauran hikima a Teman ne? Shawara ta ɓace daga masu basira ne? Hikimarsu ta ruɓe ne?
Concerning the Edomites. Thus saith Jehovah of hosts: Is wisdom no more in Teman? Is counsel passed away from the prudent? Is their wisdom vanished?
8 Ku juya ku gudu, ku ɓuya a cikin kogwanni masu zurfi, ku da kuke zama a Dedan, gama zan kawo masifa a kan Isuwa a lokacin da zan hukunta shi.
Flee ye, turn ye back, Dwell in deep places, O ye inhabitants of Dedan! For the destruction of Esau do I bring, The time of his punishment upon him.
9 In masu tsinkar’ya’yan inabi suka zo maka, ba za su rage’ya’yan inabi kaɗan ba? In ɓarayi suka zo da dare, ba za su sata abin da kawai suke bukata ba?
If grape-gatherers had come upon thee, Would they not have left some gleanings? If thieves by night, They would have destroyed only till they had enough.
10 Amma zan washe Isuwa sarai; zan bubbuɗe wuraren ɓuyarsa, don kada yă ɓoye kansa.’Ya’yansa, danginsa da maƙwabtansa za su hallaka, ba kuwa zai ƙara kasancewa ba.
But I will make Esau bare; I will uncover his hiding-places, So that he shall not be able to hide himself. His offspring shall be destroyed, and his brethren, and his neighbors, And he shall be no more.
11 Ka bar marayunka; zan tsare ransu. Gwaurayenka kuma za su dogara a gare ni.”
Leave thy fatherless children, I will preserve them alive, And thy widows, let them trust in me!
12 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “In waɗanda ba su dace su sha kwaf ɗin ba suka sha shi, me ya sa za ka kuɓuta? Ba za ka kuɓuta ba, sai ka sha shi.
For thus saith Jehovah: Behold, they who ought not to have drunk the cup have deeply drunken, And shalt thou go altogether unpunished? Thou shalt not go unpunished; Thou shalt surely drink.
13 Na rantse da kaina,” in ji Ubangiji, “cewa Bozra za tă zama kufai da kuma abin tsoro, abin dariya da abin la’ana; kuma dukan garuruwanta za su kasance kufai har abada.”
For by myself have I sworn, saith Jehovah, That Bozrah shall become an astonishment, A reproach, a desolation, and a curse; And all her cities shall be perpetual wastes.
14 Na ji saƙo daga Ubangiji cewa; an aiki jakada zuwa ga al’ummai ya ce, “Ku tattara kanku don ku fāɗa mata! Ku tashi don yaƙi!”
I have heard a proclamation from Jehovah, And an ambassador hath been sent among the nations, [[Saying, ]] “Assemble yourselves, and come against her, And arise to battle!”
15 “Yanzu zan mai da kai ƙanƙani a cikin al’ummai abin reni a cikin mutane.
For, behold, I will make thee small among the nations, Despised among men.
16 Tsoron da ka sa ake ji da kuma girman kan zuciyarka ya ruɗe ka, kai da kake zama a kogon dutse, kai da kake kan tudu. Ko da yake ka gina wa kanka sheƙa can bisa kamar na gaggafa, daga can zan sauko da kai ƙasa,” in ji Ubangiji.
Thy terribleness hath deceived thee, The pride of thy heart, Because thou dwellest in the recesses of the rock, And holdest the height of the hill. Though thou set thy nest on high, like the eagle, From thence will I bring thee down, saith Jehovah.
17 “Edom za tă zama abin tsoro; dukan wanda ya wuce zai giggice ya yi tsaki saboda dukan mikinta.
And Edom shall be an astonishment: Every one that passeth by her shall be astonished, And shall hiss on account of all her plagues.
18 Kamar yadda aka tumɓuke Sodom da Gomorra, tare da garuruwan da suke maƙwabtaka da su,” in ji Ubangiji, “haka ba wanda zai zauna a can; ba wani da zai zauna a cikinta.
As in the overthrow of Sodom and Gomorrah, And their neighboring cities, saith Jehovah, There shall not a man abide there, Nor a son of man dwell within her.
19 “Kamar zaki mai haurawa daga kurmin Urdun zuwa wurin kiwo mai kyau, zan kori Edom daga ƙasarta nan da nan. Wane ne zaɓaɓɓen da zan naɗa don wannan? Wane ne yake kama da ni kuma wa zai kalubalance ni? Kuma wane makiyayi ne zai yi gāba da ni?”
Behold, he [[the enemy]] cometh up like a lion from the pride of Jordan against the habitation of the rock; Suddenly will I drive him [[Edom]] thence, And him who is chosen by me will I set over her. For who is like me, Or who will summon me to trial? Or who is the shepherd that will stand up against me?
20 Saboda haka, ku ji abin da Ubangiji ya shirya a kan Edom, abin da ya nufa wa waɗanda suke zama a Teman. Za a ja ƙanana na garken tumaki a tafi; zai hallaka wurin kiwonsu sarai saboda su.
Therefore, hear ye the purpose of Jehovah, Which he hath formed against Edom, And the designs which he meditateth against the inhabitants of Teman! Surely he [[the enemy]] shall drag them forth like feeble sheep; Surely he shall come upon them, And make their pastures desolate.
21 Amon fāɗuwarsu zai sa ƙasa ta girgiza; za a kuma ji muryar kukansu a Jan Teku.
At the noise of their fall the earth trembleth, Even to the Red Sea is their cry heard.
22 Duba! Gaggafa tana firiya tana kuma saukowa, tana buɗe fikafikanta a bisa Bozra. A wannan rana zukatan jarumawan Edom za su zama kamar macen da take naƙuda.
Behold, like an eagle, he [[the enemy]] cometh up, And spreadeth his wings over Bozrah; And the hearts of the heroes of Edom, in that day, Shall be as the heart of a woman in her pangs.
23 Game da Damaskus. “Hamat da Arfad sun giggice, gama sun ji mummunar labari. Suna damuwa, sun damu kamar tekun da baya hutu.
Concerning Damascus. Hamath and Arpad are confounded; They faint, because they have heard evil tidings. There is anxiety at the sea; It cannot be at rest.
24 Damaskus ta karai ta juya don ta gudu tsoro kuma ya kama ta; wahala da zafi sun kama ta, zafi kamar na mace mai naƙuda.
Damascus is faint-hearted; She turneth herself to flee; Trembling hath seized on her; Anguish and pangs have taken hold of her, as of a woman in travail.
25 Me ya sa ba a tafi aka bar sanannen birnin nan ba, birnin da nake jin daɗi?
“Why is not the praised city left, The city of my joy?”
26 Tabbatacce, samarinta za su fāɗi a tituna; dukan sojojinta za su yi shiru a wannan rana,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Yea, her young men shall fall in her streets, And all her men of war shall be cut off in that day, Saith Jehovah of hosts.
27 “Zan cinna wa katangar Damaskus wuta; za tă ci kagaran Ben-Hadad.”
Yea, I will kindle a fire in the wall of Damascus, Which shall consume the palaces of Benhadad.
28 Game da Kedar da mulkokin Hazor, waɗanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya fāɗa wa. Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Tashi, ku fāɗa wa Kedar ku kuma hallaka mutanen Gabas.
Concerning Kedar, and concerning the kingdoms of Hazor, which Nebuchadnezzar, king of Babylon, smote. Thus saith Jehovah: Arise ye, go up against Kedar, And spoil the sons of the East!
29 Za a ƙwace tentunansu da garkunansu; za a tafi da mafakanta tare da dukan kayayyakinsu da raƙumansu. Mutane za su yi musu ihu, ‘Razana ko’ina!’
Their tents and their flocks shall they take away; They shall take to themselves their curtains, and all their furniture, and their camels, And men shall cry to them, “Terror is on every side.”
30 “Ku yi maza ku gudu! Ku zauna a kogo masu zurfi, ku da kuke zama a Hazor,” in ji Ubangiji. “Nebukadnezzar sarkin Babilon ya shirya muku maƙarƙashiya; ya ƙulla maƙarƙashiya a kanku.
Flee, get you far off, dwell in deep places, O ye inhabitants of Hazor, saith Jehovah. For Nebuchadnezzar, the king of Babylon, meditates a design against you, And has formed a purpose against you.
31 “Ku tashi ku kuma fāɗa wa al’umma da sauƙi wadda take zama da ƙarfin hali,” in ji Ubangiji, “al’ummar da ba ta da ƙofofi ko ƙyamare; mutanenta suna zama su kaɗai.
Arise ye, go up against a nation at ease, That dwelleth securely, saith Jehovah; Which hath neither gates nor bars; Which dwelleth alone.
32 Za a washe raƙumansu, garkunansu mai girma za su zama ganima. Zan watsar da waɗanda suke a wurare masu nesa a ko’ina zan kuma kawo musu masifa a kowane gefe,” in ji Ubangiji.
And their camels shall be a booty, And the multitude of their cattle a spoil; And I will scatter to all the winds them that shave the cheeks, And from every side will I bring their calamity, saith Jehovah.
33 “Hazor za tă zama mazaunin diloli, kufai har abada. Ba wanda zai zauna a can; ba wanda zai zauna a cikinta.”
And Hazor shall be a dwelling for jackals, A desolation forever. There shall not a man abide there, Nor any son of man dwell therein.
34 Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da Elam, a farkon mulkin Zedekiya sarkin Yahuda.
The word of Jehovah which came to Jeremiah the prophet against Elam, in the beginning of the reign of Zedekiah, king of Judah, saying: —
35 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ga shi, zan karye ƙarfin Elam, zaunannen ƙarfinsu.
Thus saith Jehovah of hosts: Behold, I break the bow of Elam, The chief part of their strength.
36 Zan kawo a kan Elam a kusurwoyi huɗu daga kusurwoyi huɗu na duniya; zan watsar da su zuwa kusurwoyi huɗu, kuma ba al’ummar da masu gudun hijirar Elam ba za su kai ba.
And I will bring against Elam The four winds from the four extremities of the heavens, And I will scatter them to all these winds, And there shall be no nation To which the outcasts of Elam shall not come.
37 Zan ragargaza Elam a gaban maƙiyansu, a gaban waɗanda suke neman ransu; zan kawo masifa a kansu, da zafin fushina,” in ji Ubangiji. “Zan runtume su da takobi sai na kawo ƙarshensu.
For I will cause Elam to be dismayed before their enemies, And before them that seek their life. And I will bring evil upon them, The fierceness of my anger, saith Jehovah. And I will send after them the sword, Until I have consumed them.
38 Zan sa kursiyina a Elam in kuma hallaka sarkinta da fadawanta,” in ji Ubangiji.
And I will set up my throne in Elam, And I will destroy from thence king and princes, saith Jehovah.
39 “Duk da haka zan maido da wadatar Elam a kwanaki masu zuwa,” in ji Ubangiji.
But it shall come to pass in future times, That I will bring back the captivity of Elam, saith Jehovah.