< Irmiya 49 >
1 Game da Ammonawa. Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Isra’ila ba shi da’ya’ya maza ne? Ba shi da magāda ne? To, me ya sa Molek ya mallaki Gad? Me ya sa mutanensa suka zama a garuruwansa?
關於阿孟子民:上主這樣說:「難道以色列沒有子孫,沒有後嗣﹖為什麼米耳公佔據了加得,而他的人民竟住在加得的城中﹖
2 Amma kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan yi kirarin yaƙi a kan Rabba ta Ammonawa; zai zama tarin juji, za a sa wuta a ƙauyukan da suke kewayenta. Sa’an nan Isra’ila zai kori waɗanda suka kore shi,” in ji Ubangiji.
為此,看,時日將到──上主的斷語──我必使阿孟子民的辣巴聽到戰爭的吶喊;她要成為一堆廢墟,她的附屬城市要為火燒盡;以色列終歸要繼承自己的產業──上主說。
3 “Ki yi kuka, ya Heshbon, gama an hallaka Ai! Ku tā da murya ku yi kuka, ya mazaunan Rabba! Ku sa tufafin makoki; ku ruga nan da can a cikin katanga, gama Molek zai tafi bauta, tare da firistocinsa da kuma fadawansa.
赫市朋,哀號罷! 因為破壞者已來近了;辣巴的女郎! 你們該哭泣,穿上苦衣哀傷,割傷自己的身體,因為米耳公要與自己的司祭和公卿,同去充軍。
4 Me ya sa kuke taƙama da kwarurukanku, taƙama da kwarurukanku masu amfani? Ya ke diya marar aminci, kin dogara a wadatarki kika kuma ce, ‘Wa zai iya fāɗa mini?’
失節的女郎! 你為什麼要誇耀你的山谷是富裕的山谷,仗恃你的寶藏說:「有誰敢來與我對抗﹖
5 Zan kawo razana a kanki daga waɗanda suke kewaye da ke,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Za a kore kowannenku, babu wani da zai tattara masu gudun hijira.
看,我從各方給你召來恐怖──我主萬軍上主的斷語──你們必被驅逐,各自奔逃,再沒人來聚集逃散的人。
6 “Duk da haka, daga baya, zan maido da wadatar Ammonawa,” in ji Ubangiji.
雖然如此,日後我仍要轉變阿孟子民的命運──上主的斷語。」
7 Game da Edom. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Babu sauran hikima a Teman ne? Shawara ta ɓace daga masu basira ne? Hikimarsu ta ruɓe ne?
關於厄東,萬軍的上主這樣說:「難道在特曼已沒有智慧,聰敏的人已計窮才盡了嗎﹖
8 Ku juya ku gudu, ku ɓuya a cikin kogwanni masu zurfi, ku da kuke zama a Dedan, gama zan kawo masifa a kan Isuwa a lokacin da zan hukunta shi.
德丹的居民! 你們該轉身逃遁,藏居深處,因為我要給厄撒烏招來災禍,已到了懲罰他的時候。
9 In masu tsinkar’ya’yan inabi suka zo maka, ba za su rage’ya’yan inabi kaɗan ba? In ɓarayi suka zo da dare, ba za su sata abin da kawai suke bukata ba?
如果收葡萄的人來到你這裏,決不會留下殘餘;如果盜賊夜間來襲,必要盡力搶取;
10 Amma zan washe Isuwa sarai; zan bubbuɗe wuraren ɓuyarsa, don kada yă ɓoye kansa.’Ya’yansa, danginsa da maƙwabtansa za su hallaka, ba kuwa zai ƙara kasancewa ba.
我就要這樣暴露厄撒烏,揭發他的隱處,使他無法躲藏;他的後裔,必被消滅,不再存於自己的鄰邦中。
11 Ka bar marayunka; zan tsare ransu. Gwaurayenka kuma za su dogara a gare ni.”
請留下你的孤兒,我必使他們生存,你的寡婦也可託付給我。
12 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “In waɗanda ba su dace su sha kwaf ɗin ba suka sha shi, me ya sa za ka kuɓuta? Ba za ka kuɓuta ba, sai ka sha shi.
因為上主這樣說:看,那原來不該飲苦爵的,一定要飲,你要想完全免罰嗎﹖你決不致於免罰,你也該痛飲!
13 Na rantse da kaina,” in ji Ubangiji, “cewa Bozra za tă zama kufai da kuma abin tsoro, abin dariya da abin la’ana; kuma dukan garuruwanta za su kasance kufai har abada.”
因為,我曾指自己起誓──上主的斷語──波責辣必成為一片荒涼,受人憎恨、侮辱和詛咒;她所有的城市,必要永遠變為荒野。
14 Na ji saƙo daga Ubangiji cewa; an aiki jakada zuwa ga al’ummai ya ce, “Ku tattara kanku don ku fāɗa mata! Ku tashi don yaƙi!”
我從上主聽得了一個消息,在萬民間傳開了一個號令:「你們該聯盟向她進攻! 你們該起來交戰! 」
15 “Yanzu zan mai da kai ƙanƙani a cikin al’ummai abin reni a cikin mutane.
因為,看,我已使你成為萬民中最小的,成為人間最可輕賤的。
16 Tsoron da ka sa ake ji da kuma girman kan zuciyarka ya ruɗe ka, kai da kake zama a kogon dutse, kai da kake kan tudu. Ko da yake ka gina wa kanka sheƙa can bisa kamar na gaggafa, daga can zan sauko da kai ƙasa,” in ji Ubangiji.
你高居在石縫的隱處,盤據在峻嶺的山巔。你自以為驚異,你心卷的驕傲欺騙了你。即使你像老鷹一樣高結你的巢穴,我也要從那裏將你推下──上主的斷語。
17 “Edom za tă zama abin tsoro; dukan wanda ya wuce zai giggice ya yi tsaki saboda dukan mikinta.
厄東必變成荒野,凡由她那裏經過的人,見了她的種種慘狀,必要唏噓嘆。
18 Kamar yadda aka tumɓuke Sodom da Gomorra, tare da garuruwan da suke maƙwabtaka da su,” in ji Ubangiji, “haka ba wanda zai zauna a can; ba wani da zai zauna a cikinta.
她必要像毀滅的索多瑪、哈摩辣及附近的城市一樣──上主說──再沒有人居住,再沒有人在那裏寄宿。
19 “Kamar zaki mai haurawa daga kurmin Urdun zuwa wurin kiwo mai kyau, zan kori Edom daga ƙasarta nan da nan. Wane ne zaɓaɓɓen da zan naɗa don wannan? Wane ne yake kama da ni kuma wa zai kalubalance ni? Kuma wane makiyayi ne zai yi gāba da ni?”
看,好像一隻雄獅,從約但的叢林上來,走向常綠的牧場;同樣,我也要突然將他們趕走,派我選定的人民來統治。誠然,誰是我的對手﹖誰敢向我提出質問﹖誰是能對抗我的牧人﹖
20 Saboda haka, ku ji abin da Ubangiji ya shirya a kan Edom, abin da ya nufa wa waɗanda suke zama a Teman. Za a ja ƙanana na garken tumaki a tafi; zai hallaka wurin kiwonsu sarai saboda su.
為此,請你們聽上主對厄東設計的計謀,對特曼居民策劃的策略:連最弱小的羊也要被人牽去,他們的牧楊也必陷於戰慄中。
21 Amon fāɗuwarsu zai sa ƙasa ta girgiza; za a kuma ji muryar kukansu a Jan Teku.
他們倒塌的響聲,震撼大地;哀號之聲,直達紅海。
22 Duba! Gaggafa tana firiya tana kuma saukowa, tana buɗe fikafikanta a bisa Bozra. A wannan rana zukatan jarumawan Edom za su zama kamar macen da take naƙuda.
看,他好像老鷹飛升翱翔,在波責辣上展開自己的翅膀;在那一日,厄東的勇士必心志頹喪,有如臨產的婦女。
23 Game da Damaskus. “Hamat da Arfad sun giggice, gama sun ji mummunar labari. Suna damuwa, sun damu kamar tekun da baya hutu.
關於大馬士革:哈瑪特和阿爾帕得聽到了不好的消息,大起恐慌,像海洋一樣動盪,愁苦得不能安寧。
24 Damaskus ta karai ta juya don ta gudu tsoro kuma ya kama ta; wahala da zafi sun kama ta, zafi kamar na mace mai naƙuda.
大馬士革失去勇氣,轉身逃遁,極感戰慄,備受憂慮痛苦,好像一臨產的婦女。
25 Me ya sa ba a tafi aka bar sanannen birnin nan ba, birnin da nake jin daɗi?
哀哉,有的城邑,享樂的都市,已被摒棄!
26 Tabbatacce, samarinta za su fāɗi a tituna; dukan sojojinta za su yi shiru a wannan rana,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
她的少年將倒斃在廣場,她的戰士在那一日內要悉數滅亡──萬軍上主的斷語──
27 “Zan cinna wa katangar Damaskus wuta; za tă ci kagaran Ben-Hadad.”
我必在大馬士革城牆上放火,吞滅本哈達得的宮闕。
28 Game da Kedar da mulkokin Hazor, waɗanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya fāɗa wa. Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Tashi, ku fāɗa wa Kedar ku kuma hallaka mutanen Gabas.
關於刻達爾和巴比倫王拿步高克服了的哈祚爾諸國,上主這樣說:「起來! 進攻刻達爾,蹂躪東方子民!
29 Za a ƙwace tentunansu da garkunansu; za a tafi da mafakanta tare da dukan kayayyakinsu da raƙumansu. Mutane za su yi musu ihu, ‘Razana ko’ina!’
奪取他們的帳幕和牲畜,帷幔和所有的器具;牽走他們的駱駝,向他們吶喊:四面恐怖。
30 “Ku yi maza ku gudu! Ku zauna a kogo masu zurfi, ku da kuke zama a Hazor,” in ji Ubangiji. “Nebukadnezzar sarkin Babilon ya shirya muku maƙarƙashiya; ya ƙulla maƙarƙashiya a kanku.
哈祚爾的居民! 你們應逃遁遠去,藏匿深處──上主的斷語──因為巴比倫王拿步高已設計謀害你們,已策畫攻擊你們。
31 “Ku tashi ku kuma fāɗa wa al’umma da sauƙi wadda take zama da ƙarfin hali,” in ji Ubangiji, “al’ummar da ba ta da ƙofofi ko ƙyamare; mutanenta suna zama su kaɗai.
起來,進攻優游閒居,不設門閂,孑然獨居的民族──上主的斷語──
32 Za a washe raƙumansu, garkunansu mai girma za su zama ganima. Zan watsar da waɗanda suke a wurare masu nesa a ko’ina zan kuma kawo musu masifa a kowane gefe,” in ji Ubangiji.
因為搶奪他們的駱駝,劫掠他們成群的牲畜;凡剃去鬢髮的,我必叫他們隨風飄散,由四面八方給他們招來災禍──上主的斷語──
33 “Hazor za tă zama mazaunin diloli, kufai har abada. Ba wanda zai zauna a can; ba wanda zai zauna a cikinta.”
哈祚爾要變為豺狼的巢穴,永遠荒涼,留下一人,不會再有人居住。」
34 Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da Elam, a farkon mulkin Zedekiya sarkin Yahuda.
猶大王漆德克雅初年,關於厄藍有上主的話傳給耶肋米亞先知說:「
35 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ga shi, zan karye ƙarfin Elam, zaunannen ƙarfinsu.
萬軍的上主這樣說:看,我要折斷厄藍的弓弩,稱雄的勢力;
36 Zan kawo a kan Elam a kusurwoyi huɗu daga kusurwoyi huɗu na duniya; zan watsar da su zuwa kusurwoyi huɗu, kuma ba al’ummar da masu gudun hijirar Elam ba za su kai ba.
我要從天下四面八方,給厄藍召來四方的風,使他們隨風飄散,以致沒有一個民族,沒有厄藍的難民。
37 Zan ragargaza Elam a gaban maƙiyansu, a gaban waɗanda suke neman ransu; zan kawo masifa a kansu, da zafin fushina,” in ji Ubangiji. “Zan runtume su da takobi sai na kawo ƙarshensu.
我必使厄藍在自己性命的人前,驚惶失措;給他們招來災禍,我忿怒的火焰──上主的斷語──派出刀劍追迫他們,直至將他們完全消滅。
38 Zan sa kursiyina a Elam in kuma hallaka sarkinta da fadawanta,” in ji Ubangiji.
我必在厄藍設立我的寶座,殲滅其中的君王將帥──上主的斷語──
39 “Duk da haka zan maido da wadatar Elam a kwanaki masu zuwa,” in ji Ubangiji.
雖然如此,在末日我仍要轉變厄藍的命運──上主的斷語。」