< Irmiya 48 >

1 Game da Mowab. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Kaito ga Nebo, gama za tă lalace. Kiriyatayim za su kunyata a kuma kame ta; katagar za tă sha kunya ta kuma wargaje.
Acerca de Moab. El Señor de los ejércitos, el Dios de Israel, ha dicho: Dolor en Nebo, porque ha sido destruida; Quiriataim ha sido avergonzado y ha sido tomado; el lugar fuerte ha sido avergonzado y destruido.
2 Ba za a ƙara yabi Mowab ba; a Heshbon mutane za su shirya mata maƙarƙashiya. ‘Zo, mu tafi mu kawo ƙarshe ga wannan al’umma.’ Ke kuma, ya Madmen za ki yi shiru; takobi zai fafare ki.
La alabanza de Moab ha llegado a su fin; En cuanto a Hesbón, el mal ha sido diseñado contra ella; Ven, pongámosle fin a ella como nación. Mas tu boca será cerrada, O Madmen; La espada te perseguirá.
3 Saurari kuka daga Horonayim, kukan risɓewa mai girma da hallaka.
Se oye el llanto de Horonaim, ruina y gran destrucción;
4 Za a karye Mowab; ƙanananta za su yi kuka.
Moab está quebrantado; Su grito ha salido a Zoar.
5 Sun haura hanyar zuwa Luhit, suna kuka mai zafi yayinda suke tafiya; a hanyar da ta gangara zuwa Horonayim suna kuka a kan hallakar da aka ji.
Porque por la ladera de Luhit subirán llorando todo el camino; porque en el camino a Horonaim, el grito de destrucción ha llegado a sus oídos.
6 Ku gudu! Ku gudu don tserar da ranku; ku zama kamar kurmi a hamada.
Ve en vuelo, escapa de tus vidas y Sean como la zarza en el desierto.
7 Da yake kun dogara ga ayyukanku da arzikinku, ku ma za a kwashe ku bayi, Kemosh zai tafi bauta, tare da firistocinsa da fadawansa.
Porque por haber puesto tu fe en tus obras y tus riquezas, tú, incluso tú, serás tomado; y Quemos saldrá como prisionero, sus sacerdotes y sus gobernantes juntos.
8 Mai hallakarwa zai aukar wa kowane gari, kuma ba wani garin da zai kuɓuta. Kwari zai lalace tudu kuma ya hallaka, domin Ubangiji ya faɗa.
Y el atacante vendrá contra todos los pueblos, ni uno estará a salvo; y el valle será arruinado, y la destrucción llegará a las tierras bajas, como el Señor lo ha dicho.
9 Ku sa gishiri a kan Mowab, gama za tă zama kango; garuruwanta za su zama kufai, ba mazauna a cikinsu.
Levante un pilar para Moab, porque ella llegará a su fin; y sus pueblos se convertirán en ruinas, sin que nadie viva en ellos.
10 “La’ananne ne shi wanda yake sake a yin aikin Ubangiji! La’ananne ne wanda ya janye takobinsa daga zub da jini!
Sea maldito el que hace la obra del Señor con engaño; Que sea maldito el que retiene su espada de sangre.
11 “Mowab ta kasance cikin kwanciyar rai tun ƙuruciyarta, kamar ruwan inabin da aka bari lis, ba a juya daga tulu zuwa wani tulu ba ba tă tafi bauta ba. Saboda haka tana da ɗanɗanonta, kuma ƙanshinta bai canja ba.
Desde sus primeros días, Moab ha estado viviendo en comodidad; como el vino almacenado durante mucho tiempo, no ha sido drenado de un recipiente a otro, nunca se ha ido como prisionero; por lo que su sabor aún está en él, su olor no ha cambiado.
12 Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan aika da mutanen da za su tuntsurar da tuluna, su kuma zubar da ita waje. Za su bar tulunan ba kome a ciki su kuma farfashe tulunanta.
Ciertamente, los días se acercan, dice el Señor, cuando le enviaré a los hombres que le harán volverse hasta que no haya más vino en sus vasijas, y sus odres vacíos de vino se romperán por completo.
13 Sa’an nan Mowab za tă ji kunyar Kemosh, yadda gidan Isra’ila ya ji kunya sa’ad da suka dogara ga Betel.
Y se avergonzará Moab a causa de Quemos, como se avergonzó a los hijos de Israel a causa de Betel su esperanza.
14 “Yaya za ku ce, ‘Mu jarumawa ne, mutane masu ƙarfi a yaƙi?’
¿Cómo pueden decir: Somos hombres de guerra y combatientes fuertes?
15 Mowab za tă hallaka a kuma kai wa garuruwanta hari; samarinta kyawawa za su gangara cikin mayanka,” in ji Sarki, wanda sunansa Ubangiji Maɗaukaki ne.
El que trae destrucción a Moab ha subido contra ella; y sus jóvenes escogidos han bajado al degolladero, dice el Rey, cuyo nombre es el Señor de los ejércitos.
16 “Fāɗuwar Mowab ta yi kusa; bala’inta zai auku nan da nan.
La calamidad de Moab está cerca, y su mal viene muy rápido.
17 Yi kuka saboda ita, dukanku mazaunan kewayenta, duk waɗanda suka san shahararta; ku ce, ‘Dubi yadda sandan sarauta mai iko ya karye, dubi yadda sanda mai daraja ya karye!’
Todos los que lo rodean, den señales de dolor por él, y todos los que conocen su nombre, digan: ¡Cómo se rompe la vara fuerte, incluso él glorioso bordon!
18 “Sauko daga darajarku ku zauna a busasshiyar ƙasa, Ya mazaunan Diyar Dibon, gama shi mai hallaka Mowab zai haura a kanku zai kuma lalace biranenku masu kagarai.
Desciende de tu gloria, pueblo de Dibón, y toma asiento en el lugar reseco; porque él destructor de Moab ha subido contra ti, enviando destrucción a tus fortalezas.
19 Ku tsaya a bakin hanya ku duba, ku da kuke zama a Arower. Ku tambayi mutumin da yake gudu da macen da take tserewa, tambaye su, ‘Me ya faru?’
Oh hija de Aroer, toma tu puesto por cierto, de guardia; pregúntale quién está huyendo y quién se ha escapado, pregunta, ¿qué se ha hecho?
20 An kunyata Mowab, gama ta wargaje. Ku yi kuka ku kuma tā da murya! Ku yi shela kusa da Arnon cewa an hallaka Mowab.
Moab ha sido avergonzada, está quebrantada; hace fuertes ruidos de dolor, pidiendo ayuda; den la noticia junto al Arnón, que Moab ha sido destruida.
21 Hukunci ya zo wa tudu, zuwa Holon, Yahza da Mefa’at,
Y el castigo ha llegado a las tierras bajas; en Holon, Jahaza, Mefaat,
22 zuwa Dibon, Nebo da Bet-Dibilatayim,
Dibón, Nebo, Bet-diblataim,
23 zuwa Kiriyatayim, Bet-Gamul da Bet-Meyon,
Quiriataim, y en Beth-gamul, y en Bet-meon,
24 zuwa Keriyot da Bozra zuwa dukan garuruwan Mowab, nesa da kusa.
Queriot, y en Bosra, y en todos los pueblos de la tierra de Moab, lejanos y cercanos.
25 An karye ƙahon Mowab; an karye hannunta,” in ji Ubangiji.
Se corta el poder de Moab y su poder destruido, dice el Señor.
26 “Ku bugar da ita domin ta tayar wa Ubangiji. Bari Mowab tă yi ta birgima a cikin amanta; bari tă zama abin dariya.
Emborrachenlo, porque su corazón se ha enorgullecido contra el Señor; y Moab se revolcara en su vómito, y todos se burlarán de él.
27 Isra’ila ma bai zama abin dariya a gare ki ba? Ba a kama shi cikin ɓarayi, har kaɗa kai na ba’a kike yi a duka sa’ad da kike magana game da shi?
¿No hiciste burla de Israel? fue tomado entre los ladrones? porque cuando estabas hablando de él, estabas hablando con desprecio.
28 Ku bar garuruwanku ku zauna a cikin duwatsu, ku da kuke zama a Mowab. Ku zama kamar kurciyar da take sheƙarta a bakin kogo.
Oh pueblo de Moab, sal de los pueblos y escápate en la roca; Sé como la paloma de Araba, que la convierte en lugar de vivir detrás de la boca de la caverna.
29 “Mun ji labarin girman kan Mowab mun ji alfarma girmankanta da kumburinta girmankanta da fariyarta da renin zuciyarta.
Hemos recibido la noticia del orgullo de Moab, de su soberbia; y su gran opinión de sí mismo, de su arrogancia, la altivez de su corazón.
30 Na san alfarmanta amma a banza ne,” in ji Ubangiji, “kuma taƙamarta ba ya cimma kome.
Tengo conocimiento de su ira, dice el Señor, que no es nada; Sus jactancias no han hecho nada.
31 Saboda haka zan yi kuka a kan Mowab gama dukan Mowab zan yi kuka, Zan yi gurnani don mutanen Kir Hareset.
Por esta causa daré gritos de dolor por Moab, clamando por todo Moab; Estaré triste por los hombres de Kir-heres.
32 Zan yi kuka saboda kai, yadda Yazer ya yi kuka Ya kuringar Sibma. Rassanki sun kai har teku; sun kai har tekun Yazer. Mai hallakarwa ya fāɗo a kan’ya’yan itatuwanku da kuma inabinku da suka nuna.
Mi llanto por ti, oh viña de Sibma, será más que el llanto de Jazer; tus ramas se han extendido sobre el mar, extendiéndose incluso hasta Jazer; la destrucción ha caído sobre tus frutos de verano y tus uvas cortadas.
33 Farin ciki da murna su ɓace daga lambunan itatuwa da kuma gonakin Mowab. Na dakatar da malalar ruwan inabi daga wurin matsi; ba wanda zai matse su da ihun farin ciki. Ko da yake akwai sowa sowar ba ta farin ciki ba ce.
Todo el gozo se ha ido; ya no se alegran por el campo fértil y por la tierra de Moab; He hecho que el vino llegue a su fin en los lagares donde los pisan; ya no pisaran las uvas con el sonido de voces alegres.
34 “Muryar kukansu na tashi daga Heshbon zuwa Eleyale da Yahaz, daga Zowar har zuwa Horonayim da Eglat Shelishiya, gama har ruwan Nimrim ma sun bushe.
El clamor de Hesbón llega incluso a Eleale; a Jahaz suena su voz; desde Zoar hasta Horonaim y Eglat-selisiya; porque las aguas de Nimrim se secarán.
35 A Mowab zan kawo ƙarshen waɗanda suke miƙa hadayu a masujadan kan tudu suna kuma ƙone turare ga allolinsu,” in ji Ubangiji.
Y pondré fin a Moab, dice el Señor al que hace ofrendas en el lugar alto y quema incienso a sus dioses.
36 “Saboda haka zuciyata na makoki don Mowab kamar busa; tana makoki kamar busa saboda mutanen Kir Hareset. Arzikin da suka samu ta ƙare.
Entonces mi corazón gemirá por Moab como el sonido de las flautas, y mi corazón está sonando como flautas por los hombres de Kir-heres: porque la riqueza que él tiene para sí mismo ha llegado a su fin.
37 An aske kowane kai aka kuma yanke kowane gemu aka kuma sa wa kowane kwankwaso rigar makoki.
Porque en todas partes se corta el vello de la cabeza y el vello de la cara; en cada mano hay heridas y se han vestido de silicio.
38 A kan dukan rufi a Mowab da kuma a dandalin jama’a babu wani abu sai kuka gama na karye Mowab kamar tulun da babu mai so,” in ji Ubangiji.
En todas las casas de Moab y en sus calles hay llanto por todas partes; porque Moab se ha roto como un vaso en el cual no hay placer, dice el Señor.
39 “Duba yadda aka ragargazar ta ita! Duba yadda suke kuka! Duba yadda Mowab ta juya bayanta da kunya! Mowab ta zama abin ba’a abin tsoro ga dukan waɗanda suke kewaye da ita.”
Hagan lamentación por Moab ¿Cómo ha sido quebrantado? ¿Cómo se ha vuelto la espalda de Moab avergonzado? así que Moab será una causa de burla y espanto para todos los que lo rodean.
40 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ga shi! Gaggafa tana firiya zuwa ƙasa, tana shimfiɗa fikafikanta a kan Mowab.
Porque el Señor ha dicho: Mira, vendrá como un águila en vuelo, extendiendo sus alas contra Moab.
41 Za a ci Keriyot a kuma kame kagarai. A wannan rana zukatan jarumawan Mowab za su zama kamar zuciyar macen da take naƙuda.
Ha sido tomado Queriot, y las fortalezas han sido ocupadas por los enemigos, y los corazones de los hombres de guerra de Moab en ese día serán como el corazón de una mujer en los dolores de parto.
42 Za a hallakar da Mowab a matsayin al’umma domin ta tayar wa Ubangiji.
Y Moab llegará a su fin como pueblo, porque él se ha estado levantando contra el Señor.
43 Razana da rami da tarko suna jiranku, Ya mutanen Mowab,” in ji Ubangiji.
El temor, la muerte y la red han caído sobre ti, pueblo de Moab, dice el Señor.
44 “Duk wanda ya gudu daga razana zai fāɗa cikin rami, duk wanda ya haura daga rami zai fāɗa cikin tarko; gama zan kawo wa Mowab shekarar hukuncinta,” in ji Ubangiji.
El que huya del miedo será vencido por la muerte; y el que se libere de la muerte, será capturado en la red: porque haré que venga esto a Moab, el año de su castigo, dice el Señor.
45 “A ƙarƙashin Heshbon masu gudun hijira suna tsaye ba mai taimako, gama wuta ta mutu daga Heshbon, harshen wuta daga tsakiyar Sihon; ta ƙone goshin Mowab, ƙoƙon kai na’yan tayarwa masu surutu.
Los que salieron huyendo del miedo están esperando a la sombra de Hesbón, porque se está quemando Hesbón y una llama de la casa de Sehón, se extiende y quema los montes Moab y la corona de cabeza de esos revoltosos.
46 Kaitonki, ya Mowab! Mutanen Kemosh sun hallaka; an kai’ya’yanki maza daurin talala’ya’yanki mata zaman bauta.
¡El dolor es tuyo, oh Moab! La gente de Quemos ha perecido, porque tus hijos y tus hijas han sido llevados prisioneros.
47 “Duk da haka zan maido da wadatar Mowab a kwanaki masu zuwa,” in ji Ubangiji. A nan hukuncin Mowab ya ƙare.
Pero aún así, dejaré que el destino de Moab cambie en los últimos días, dice el Señor.

< Irmiya 48 >